Sashe 169
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Hannunshi tsam cikin nata tafin hannunsu a hade,kunya duka ta kamata,baijin kunyar jama'ar da suke tare?,eanda ta lura wasu sai satar kallonsu suke,a hankali suja fara kewayawa bangaren makarantar yaran inda suke karatu,makaranta ce mai zaman kanta,nursery primary zuwa secondry duka cikin gidan suke,bangaren wajem wasannin yara daga cikinsu,gurin koyon sana'ar manya,da dan madaidaicin asiniti don duba lafiyarsu,duk inda suka zo wucewa suka ci karo da wasu idan manya ne sukan qaraso fuskarsu dauke da madaukakiyar fara'a,abinda zai baka mamaki yadda suke bashi hannu kai tsaye suyi musabaha cikin yanayi na sabo da jan mutum a jiki,idan mata ne sukan duqa cikin girmamawa su gaidashi su wuce suna murna,yara qananu maza da mata da gudu suke qarasowa wajensa,yakan daga su ya sumbacesu,ko ya shafa kansu idan sunyi girman da zaya dagasu,idan yaga wani cikin yanayin da bai masa zai tambayi ba'asi ko dalilin barinsa haka?,bare ma da wuya kaga wani cikinsu cikin mummunan kama,kowa neat yake cikin tsafta da tufafi mai kyau,tun tana satar kallonshi ta gefan idanu har ta koma ta gaban idanuwa,karon farko da taji ya burgeta a rayuwa,wanne irin mutum ne shi mai tausayi haka,sauqin kai jin qai da son yara?,yadda yake mu'amalantarsu abun yayi masifar burgeta,ko banza tana da maraya,tasan ciwon rashin uba,bare wadaj nan da ba'a rasa yaran da ake kira shegu a cikinsu,wanda basu da kowaba duniya,an yardasu tun suna da qananun shekafunsu,basuji ba basu gani ba,ba'a barsu da tabin da aka haifar musu ba na rashin fitowa ta hanyar data dace ba,sai da aka sake cika rayuwarsu da tabo da quncin rashin sakin waye uwa uba kuna dangi a garesu,ba shakka yayi wani abu mai girma arayuwarsa wanda koda shi daya yayi a duniya ya cimma nasara,ma'aiki S A W yana cewa 'nida mai kula da maraya kamar haka muke a aljanna(sai ya kwantanta da yatsansa dan manuni dana tsakiya)' me yafi wannan alkhairi na zama maqoci a aljanna wajen fiyayyen halitta?,ba sai kayi da yawa ba,ko guda daya ka kula da shi kana da wannan garabasar bare kuma kayi serving rayuwar daruruwa,koda baka jin rahama da tausayi cikin zuciyarka kana jinta kamar a qesashe ka dimanci shafa kan maraya kamar yadda ma'aiki ya umarci wani sahabi,Allah ka bamu iko ka bawa masu ikon da qargin cikinmu ikon taimakawa marayan.
Sannu a hankali suka ci gaba da takowa,dubanta yayi kana ua dauke kai yana jawota zuwa jikinsa sosai,kunya kamar qasa ta tsage ta shige,kasa daurewa tayi
"Ammm,akwai mutane fa da suke tare da mu"
"Shshshs,na fiki sani ai ko?,ko wani abu na daban na aikata bayan haka,it seems kin soma gajiya da tafiyar" ya qarasa fada yana tarota sosai,shiru tayi don ta fuskanci ci gaba da bayanin bashi da wani amfani,har zuwa sanda suka qarasa dakin kwanan yaran,don baya shiga sashen 'yammatan,yana baiwa masu kula da su mata ne su dama tambayi matsalarsu,a nan auka ci karo da wata yarinya wadda ta nufoshi da gudu,durqusawa yayi ya dauketa yana sakin murmushi,yana tausayin yaran,yana jinsu a jikinsa,ba shakka rayuwarsu akwai ban tausayi,ka tashi bakasan hatta wadanda sukayi silar kawoka duniya ba,me yafi wannan ciwo?,yana dauke da ita suka ci gaba da takawa wanda ya sanya sakin sumayya daga jikinsa,sam taqi yarda ya sauketa,yarinyar akwai surutu da wayo,tambaya take masa kan me yasa ya dade bai dawo ba?,ko da ya amsa mata sai kuma ta waiwayo ga sumayya tana tambayar wacece wannan,waiwayowa yayi ya kalli sumayya
"Sai ki bata amsa" ya fada yana tsareta da ido,murmushi ta saki wanda ya bayyana fararen haqoranta tana duban yarinyar,maqe kafada tayi
"A'ah uncle kai zaka fada min" gira ya dage murmushi na subuce masa yana duban yarinyar wadda shi ya sanya mata suna randa aka tsintota ya sanya mata amatullah
"Matata ce abokiyar rayuwata,qawata kuma qanwata" ya qarashe fada idanunsa na kan sumayyan,wani abu ne ya tsirga mata daga kai har tafin qafa,janye idanunta tayi tana maimaita kalamanshi
"Mata ta masoyiya?,yaushe na zama masoyiyarsa?" Waiwayawa yayi ya miqawa daya daga cikin masu kula da yaran amatullah sanda suka isa bakin office dinsa yana fadin su jirashi yanzu zai fito madam ta gaji zata huta.
Shike gaba tana bayanshi,suna qarasa shiga ya waiwayo da hanzari cikin shammata ya hadeta da qofan office din da faffadan qirjinsa,yayin da ya sanya hannunsa ta bayanta yana murzawa qofar muqulli,qugunta ya kama ya riqe da hannu daya,yayin da ya dafe qofar da daya hannun,hucin numfashinsa na sauka saman fuskarta,ya cika mata idanu ya mata wani mugun kwarjini
"Uhumm.....baki yarda bane da nace kedin matata ce kuma masoyiyata?" Ya tambayeta kanshu tsaye,jin tayi shiru yasa ya dora
"If kina doubting kiyi magana" ya sake fada yana dage mata girarshi,qarar wayarshi ya ceceta daga kallon da yake mata,ya dan ka baya yana amsa kiran wanda daga driva ne yake tuna mishi kada su makara har jirgi ya tashi
"Ok" kawai ya fada ya ja da baya,saman teburin ya nufa ya dudduba wasu takardu sannan ya nufi qofa wanda tana tsaye nan tana qoqarin didaita numfashinta,hannunta ya sanya cikin nata kaman yadda suka shigo suka fice bayan ya bar key din jikin qofar yasan akwai mai kullewa,a nan ya samu ma'aikatan,ya yabawa kowa yadda zasuji qwarin gwiwar ci gaba da kula da ayyukansu,sannan ya umarci dalhatu wanda shine shugaba baki daya daya turo mishi bayanan dukkan wata matsala damuwa ko buqatar da suke da shi ta emil dinsa,idan da hali a dauki masa vidiom duk wani mai matsala ko wata buqata koda a rubuce idan zasu iya a masa sending,zai samu lokaci ya duba a nutse in sha Allah,ya bude 'yar jakar dake hannunshi ya musu rabon kudi bawai don ya gaza albashinsu bane,wannan sabonshi ne haka yake duk sanda yazo,wanda wannan na daya daga cikin abinda yasa suke son yazo din da kansa,ya sake jadadda musu muhimmanci amana sannan suka fara tako masa don yi masa rakiya.
Gab da zai shiga motar tashi ya hangosu su uku,matasan yammata ne wanda zasu doshi shekara sha shida shida riqe da wata a tsakiyarsu tana dingisawa,sai da suka matso sosai ya kula da jini dake diga a qafarta,cikin tashin hankali ya kirasu suka yo wajensa,benci ya sanya aka dauko suka dorata akai,duk sun rude suna tambayar meta taka suka ce kwalba ce,hankalinshi tashe ya tsugunna da kanshi sanda suke yunqurin aje masa kujera ya dakatar da su,cikin rudewa yake yunqurin kama qafar ya duba inda ta shiga din caraf yaji an riqe qafan,sumayya ce,kusa da shi ta tsugunna ba tare data dubeshi ba,yayin da shi kuma ya biya da kallo yana janye nashi hannun,hakanan kawai taji wani abu ya soketa sanda ya tsugunna gabanta yana qoqarin kama qafar,batasan ta kai wajen ba,daga qafar tayi ta hasko mishi wajen tana duban 'yar budurwar
"Kina budurwa me ya kaiki yawo ba takalmi har ki taka kwalba haka?" Ta tambayeta
"Takalmin nake duba inda na ajjiyeshi ban kula ba she kwalbar na gaba na sai na taka" kai ya daga ya basu umarnin shiga clinic ya gaya musu abinda zasu dauko masa,cikin sakanni suka dawo,ya dauki wani daj qarfe da zai zaqulo kwalbar ya tunkari qafar,da sauri ta sanya hannu zata karba,sai ya sakar mata yana dubanta cikin mamaki,shi ya dinga nuna mata yadda zatayi har ta gama tayi mata dressing,tana cire safar hannun nata bayan ta gama qasa qasa yake dubanta,yana mamakin yadda tayi aikin perfectly,tayi kicin kicin da fuska,baisan me yasa ta hanashi yin aikin ba.
Suna zaune cikin mota murmushi ya subuce masa sanda wani tunani ya fado masa,kai ya kada yana cije lebansa na qasa,ya miqa hannunshi ya damqo nata hannun dake ajjiye saman cinyarta,waiwayowa tayi tana dubanshi,ido daya ya kashe mata,murya can qasa wanda sai ka mugun kasa kunne zaka iya jiyo me yake cewa
"Kada ki yarda ki soma kishina tun yanzu" fuska a hade ya fada,cikin mamaki take dubanshi,sai ta samu kanta da tabe baki
"Na meye zanyi kishinka?"
"Saboda na lura kin fada tarkon sona,ko kina jayayya"mamaki ya sake kamata,yaushe hakan ta faru da zai fadi haka,cikin dakiya tace
" qwarai kuwa"da qarfi ya janyota ta sake matsowa kusa da shi,idanuwansu cikin na juna yana dubanta kamar zai cinyeta danya,daga idanuwanta zuwa jajayen labbanta da suka sha jambaki,ji yake kamar ya cinyesu
"Me yasa kika hanani ta qafarta?"
"Wa kenan?" Ta ambata cikin dakiya,duk da yadda takeson janye idanunta saboda yadda kallon ke aika saqo har cikin qwaqwalwarta,murmushin gefan baki ya saki,he love her style har cikin zuciyarshi hakan ke burgeshi
"Kin qware wajen pretending,uumm?" Ya sake fada yana jifanta da wani salon kallo,so take ta janye idanunta amma ta kasa,har sai da ya samu nasarar jefa kasala da mutuwar jiki tattare da ita
"Idan haka ne,kada ki sake hanani aikina ko ma akan waye" ya fadi yana sakinta
"Dama ba hanaka nayi ba,taimakonka kawai nayi" ta amsa tana gyara zamanta
"Really?,dis is d begining of love,taimako and tausayi,alright?"ya fadi yana daga kafadunsa cikin i dont care manner,shiru tayi maganarsa na mata kaikawo,bata son ya sake kasheta da wannan mayun idanun nashi hakan ya sanya batayi musu shi ba.
Sannu a hankali suka ci gaba da takowa,dubanta yayi kana ua dauke kai yana jawota zuwa jikinsa sosai,kunya kamar qasa ta tsage ta shige,kasa daurewa tayi
"Ammm,akwai mutane fa da suke tare da mu"
"Shshshs,na fiki sani ai ko?,ko wani abu na daban na aikata bayan haka,it seems kin soma gajiya da tafiyar" ya qarasa fada yana tarota sosai,shiru tayi don ta fuskanci ci gaba da bayanin bashi da wani amfani,har zuwa sanda suka qarasa dakin kwanan yaran,don baya shiga sashen 'yammatan,yana baiwa masu kula da su mata ne su dama tambayi matsalarsu,a nan auka ci karo da wata yarinya wadda ta nufoshi da gudu,durqusawa yayi ya dauketa yana sakin murmushi,yana tausayin yaran,yana jinsu a jikinsa,ba shakka rayuwarsu akwai ban tausayi,ka tashi bakasan hatta wadanda sukayi silar kawoka duniya ba,me yafi wannan ciwo?,yana dauke da ita suka ci gaba da takawa wanda ya sanya sakin sumayya daga jikinsa,sam taqi yarda ya sauketa,yarinyar akwai surutu da wayo,tambaya take masa kan me yasa ya dade bai dawo ba?,ko da ya amsa mata sai kuma ta waiwayo ga sumayya tana tambayar wacece wannan,waiwayowa yayi ya kalli sumayya
"Sai ki bata amsa" ya fada yana tsareta da ido,murmushi ta saki wanda ya bayyana fararen haqoranta tana duban yarinyar,maqe kafada tayi
"A'ah uncle kai zaka fada min" gira ya dage murmushi na subuce masa yana duban yarinyar wadda shi ya sanya mata suna randa aka tsintota ya sanya mata amatullah
"Matata ce abokiyar rayuwata,qawata kuma qanwata" ya qarashe fada idanunsa na kan sumayyan,wani abu ne ya tsirga mata daga kai har tafin qafa,janye idanunta tayi tana maimaita kalamanshi
"Mata ta masoyiya?,yaushe na zama masoyiyarsa?" Waiwayawa yayi ya miqawa daya daga cikin masu kula da yaran amatullah sanda suka isa bakin office dinsa yana fadin su jirashi yanzu zai fito madam ta gaji zata huta.
Shike gaba tana bayanshi,suna qarasa shiga ya waiwayo da hanzari cikin shammata ya hadeta da qofan office din da faffadan qirjinsa,yayin da ya sanya hannunsa ta bayanta yana murzawa qofar muqulli,qugunta ya kama ya riqe da hannu daya,yayin da ya dafe qofar da daya hannun,hucin numfashinsa na sauka saman fuskarta,ya cika mata idanu ya mata wani mugun kwarjini
"Uhumm.....baki yarda bane da nace kedin matata ce kuma masoyiyata?" Ya tambayeta kanshu tsaye,jin tayi shiru yasa ya dora
"If kina doubting kiyi magana" ya sake fada yana dage mata girarshi,qarar wayarshi ya ceceta daga kallon da yake mata,ya dan ka baya yana amsa kiran wanda daga driva ne yake tuna mishi kada su makara har jirgi ya tashi
"Ok" kawai ya fada ya ja da baya,saman teburin ya nufa ya dudduba wasu takardu sannan ya nufi qofa wanda tana tsaye nan tana qoqarin didaita numfashinta,hannunta ya sanya cikin nata kaman yadda suka shigo suka fice bayan ya bar key din jikin qofar yasan akwai mai kullewa,a nan ya samu ma'aikatan,ya yabawa kowa yadda zasuji qwarin gwiwar ci gaba da kula da ayyukansu,sannan ya umarci dalhatu wanda shine shugaba baki daya daya turo mishi bayanan dukkan wata matsala damuwa ko buqatar da suke da shi ta emil dinsa,idan da hali a dauki masa vidiom duk wani mai matsala ko wata buqata koda a rubuce idan zasu iya a masa sending,zai samu lokaci ya duba a nutse in sha Allah,ya bude 'yar jakar dake hannunshi ya musu rabon kudi bawai don ya gaza albashinsu bane,wannan sabonshi ne haka yake duk sanda yazo,wanda wannan na daya daga cikin abinda yasa suke son yazo din da kansa,ya sake jadadda musu muhimmanci amana sannan suka fara tako masa don yi masa rakiya.
Gab da zai shiga motar tashi ya hangosu su uku,matasan yammata ne wanda zasu doshi shekara sha shida shida riqe da wata a tsakiyarsu tana dingisawa,sai da suka matso sosai ya kula da jini dake diga a qafarta,cikin tashin hankali ya kirasu suka yo wajensa,benci ya sanya aka dauko suka dorata akai,duk sun rude suna tambayar meta taka suka ce kwalba ce,hankalinshi tashe ya tsugunna da kanshi sanda suke yunqurin aje masa kujera ya dakatar da su,cikin rudewa yake yunqurin kama qafar ya duba inda ta shiga din caraf yaji an riqe qafan,sumayya ce,kusa da shi ta tsugunna ba tare data dubeshi ba,yayin da shi kuma ya biya da kallo yana janye nashi hannun,hakanan kawai taji wani abu ya soketa sanda ya tsugunna gabanta yana qoqarin kama qafar,batasan ta kai wajen ba,daga qafar tayi ta hasko mishi wajen tana duban 'yar budurwar
"Kina budurwa me ya kaiki yawo ba takalmi har ki taka kwalba haka?" Ta tambayeta
"Takalmin nake duba inda na ajjiyeshi ban kula ba she kwalbar na gaba na sai na taka" kai ya daga ya basu umarnin shiga clinic ya gaya musu abinda zasu dauko masa,cikin sakanni suka dawo,ya dauki wani daj qarfe da zai zaqulo kwalbar ya tunkari qafar,da sauri ta sanya hannu zata karba,sai ya sakar mata yana dubanta cikin mamaki,shi ya dinga nuna mata yadda zatayi har ta gama tayi mata dressing,tana cire safar hannun nata bayan ta gama qasa qasa yake dubanta,yana mamakin yadda tayi aikin perfectly,tayi kicin kicin da fuska,baisan me yasa ta hanashi yin aikin ba.
Suna zaune cikin mota murmushi ya subuce masa sanda wani tunani ya fado masa,kai ya kada yana cije lebansa na qasa,ya miqa hannunshi ya damqo nata hannun dake ajjiye saman cinyarta,waiwayowa tayi tana dubanshi,ido daya ya kashe mata,murya can qasa wanda sai ka mugun kasa kunne zaka iya jiyo me yake cewa
"Kada ki yarda ki soma kishina tun yanzu" fuska a hade ya fada,cikin mamaki take dubanshi,sai ta samu kanta da tabe baki
"Na meye zanyi kishinka?"
"Saboda na lura kin fada tarkon sona,ko kina jayayya"mamaki ya sake kamata,yaushe hakan ta faru da zai fadi haka,cikin dakiya tace
" qwarai kuwa"da qarfi ya janyota ta sake matsowa kusa da shi,idanuwansu cikin na juna yana dubanta kamar zai cinyeta danya,daga idanuwanta zuwa jajayen labbanta da suka sha jambaki,ji yake kamar ya cinyesu
"Me yasa kika hanani ta qafarta?"
"Wa kenan?" Ta ambata cikin dakiya,duk da yadda takeson janye idanunta saboda yadda kallon ke aika saqo har cikin qwaqwalwarta,murmushin gefan baki ya saki,he love her style har cikin zuciyarshi hakan ke burgeshi
"Kin qware wajen pretending,uumm?" Ya sake fada yana jifanta da wani salon kallo,so take ta janye idanunta amma ta kasa,har sai da ya samu nasarar jefa kasala da mutuwar jiki tattare da ita
"Idan haka ne,kada ki sake hanani aikina ko ma akan waye" ya fadi yana sakinta
"Dama ba hanaka nayi ba,taimakonka kawai nayi" ta amsa tana gyara zamanta
"Really?,dis is d begining of love,taimako and tausayi,alright?"ya fadi yana daga kafadunsa cikin i dont care manner,shiru tayi maganarsa na mata kaikawo,bata son ya sake kasheta da wannan mayun idanun nashi hakan ya sanya batayi musu shi ba.