Sashe 27
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tamkar an dorawa zuciyarta dutse haka taji saboda tsabar kishi,yau nukhtar dinta zai sake zama na wata a karo na biyu,me yasa yaya yahanasu taqi barinsu su huta,me yasa ba zata gane irin yadda take son mukhtar dinta ba,laifi ne dan baka haihu ba?,shine lawai dalilin da yasa suke ta rabata da farincikinta a lokuta mabanbanta,ina ma ace ana siyar da haihuwa yau da ta sayeta koda zata rasa zanin daurawa,koda zata rasa lomar abincin da zata sanyawa bakinta,don dai kawai su barta da mukhtar suyi rayuwar farinciki.
So take ta bude baki da gaya masa magana ko zata ji sauqin tuquqin da zuciyarta ke maga amma sai ta kasa,girman mukhtar cikin idonta yafi gaban haka,miqewa tayi gudu gudu sauri sauri idonta na saukar da qwalla kan kuncinta,miqewa yayi biyita da sauri cike da muradin cimmata,saidai tuni ta afka toilet dinta ta rufe qofa tare da sakin kuka.
Bakin toilet din ya tsaya yana naci da magiyar ta fito,sai da suka kusa kwashe minti ashirin a haka,ba zata iya kallonsa ya tafi dakin wata ba hakan ya sanyata cikin muryar kuka tace
"Bana son ganinka yaya mukhtar ka tafi don Allah ka qyaleni"
"Yau nine sumayya baki son gani?.....yau......." Bai kamamala maganar ba wayarsa dake aljihun gaban rigarsa ya hau ruri,hannunshi ya zira,ganin mai kiran ya sanyashi dagawa
"Dear m,ina ka tsaya ne wai bayan na ji shigowarka",bazai iya tantance mai yaji ba,so yake ya rufeta da masifa amma sai ya kasa,maimakon haka sai ya bige da cewa
" ina gun yayarki zance ko qanwarki ina lallashi"gabanta ha fadi haushi ta turniqeta,kada fa ace duk abinda ake bata labari kan sumayyar gaskiya ne,amma babu komai saura qiris tayi maganin abun
"Lallashin me kuma dear bayan ba wannan ne karo na farko ba da aka fara mata kishiya,ka taho ko nazo da kaina na tafi da kai"
"Ok gani nan" ya fadi da sauri tare da katse kiran,maida idanunsa yayi ga qofar toilet din,ya tabbatar taji duk abinda suka ce,kamar sumayyan ce ke gabansa ya marairaice
"Shikenan sumayya zan tafi,ga ledarki can cikin daki Allah ya bamu alkhairi" ya fada yana juyawa.
Zamewa tayi tayi zaman dirshan saman tiles din bandakin sabon kuka na kubce mata wanda ta sanya tafin hannunta ta toshe bakinta don kada su jiyota,duk da cewa ita tace ya tafin bata yi tsammanin tafiyar tasa da gaggawa ba haka.
Ta jima tana kuka a ciki kafin ta lallashi kanta bayan tayi tilawar wasiyyoyin mahaifiyarta tun daga auren da aka qara mata na fari zuwa wannan da ya kasance na biyu.
Bata bar bayin ba sai da cikakkiyar alwala,ta koma daki ta sauya kayan bacci,doguwar riga ce har qasa mai taushi da kauri,hijabi ta dora saman riga ta shimfida abun sallaha ta tayar da sallah hawaye na layi kan kumatunta.
Yana shiga ta miqe ta taroshi cikin karairaya da yauqi,ta amshi ledar hannunsa ta ajjye kana ta rungumeshi,yaqe haqora kawai yake,ko daya bata burgeshi ba,alamu sun nuna babu kunya ko qwaya daya cikin idanunta,ko daya baiji dadin kasancewarta cikin jikinsa ba amma sai ya kasa cewa da ita komai,sai ya dinga dauko daren farkon sumayya da na fa'iza da nata yana hadawa,tuni lissafin ya wargaje don tako ina sun sha banban.
Biye yake da ita kawai sai ido da yake binta da shi,ita ta hada musu ruwa sukayi wanka sannan ta samo plate ta juye kazar a ciki,kusan ita ta dinga ciyar da shi ta kuma ci da kanta har suka kammala ta janyeshi gado don tuni ta dokanta,kusan ita ta gabatar da komai a maimakonshi,mamaki da haushi ke tuqeshi,gefe guda wani irin takaici wanda idan ya yunqura zaiyi magana sai yaji ya kasa cewa komai,data dubeshi kuma sai yaji komai ya wuce ya bar tasiri cikin ransa.
Kwana tayi zaune bayan ta gaji da yin sallolin,abinda bata taba zata zata iya ba,yaushe mukhtar ya sake zame mata wani na daban haka,ita kanta tana mamakin yadda ta koyi kishinsa har haka,sai da ta gabatar da sallar asuba taji idanunta sun soma nauyi da zugi,duk yadda taso ta yakice baccin amma bata samu nasara ba,haka yazo ya saceta cikin gaggawa ya kuma mata nauyi wanda hakan ya sanya ta gaza sanin meke wakana cikin gidan har misalin qarfe goma da rabi ma safe wanda ta farka a firgice.
Bandakin cikin dakinta ta shiga da yake bayan na corridor akwaai cikin daki,wanka tayi bayan ta wanke bakinta ta dawo cikin dakin,jikinta babu qwari ta shirya cikin atamfa doguwar riga wadda ta mata kyau,duk da bata jin qwarin jikinta amma tayi lite make up wadda ta dace da yanayinta,babu dauda ko qura a rea dinta sai dan kakkabe kakkabe kawai da tayi sannan ta fito don samawa kanta abinda zata ci koda ruwan zafi ne,don jinta take iska na yawo da ita tsabar babu komai a cikinta,ledar jiya mukhtar din ya bata ta dauka ta fice da ita.
Bata kula da su ba sai data shigo cikin falon sosai,mukhyat sanye da yadi mai taushi fari tas wanda ka yiwa aiki da zare ash,sai wandda idanunta suka sake sauka kanta wanda bata tantama itace zainab din.
Macace wadda kallo daya ta yi mata ta fuskanci ta girmesu ita da fa'iza baki daya,A qalla tayi shekaru ashirin ta takwas wanda hakan ke nuna ta girmi sumayyan da shekara goma tunda sai yanzu taje cikin shekararta ta goma sha tara,baqa ce zainab din amma ba baqi can ba,tana da cika wadda za'a iya kiranta qiba kai tsaye duk da wata mai yawa bace,bata daga cikin sahun kyawawa ko kadan amma zaiyi wuya kai tsaye ka kirata da mummuna saboda yanayin iya gogayya da iya salo,saidai tako ina sumayyan ta mata fintikau,abu daya zata iya nuna mata qwala qwalan idanu da suke zagayayyu suka fi na sumayya girma,sakamakon natan lumsassu ne ba kowanne lokaci kake iya gane girmansu ba,sanye take da material mai santsi wanda aka yiwa dinkin riga da skert,breakfast sukeyi wanda ya qunshi tea da soyayyen qwai da bread,sai kaji wanda ba tantama na jiya ne aka sake gasa su.
Shi ya soma ganinta lokacin da zainab ke qoqarin bashi naman a baki,sai ya goce wanda hakan ya janyo hankalin zainab din ta ankara da fitowar sumayyan,murmushi ya sakar mata yayin da itama tayi qoqarin maida masa martani
"Kin tashi kenan,na leqaki na taras kina bacci"
"Eh,ban jima ai da tashi ba" ta fada tana takowa gabansu
"Kinyi kyau sumy ta" ya fada yana sake dubanta wanda kalmar ba qaramin dukan qirjin zainab tayi ba,lokaci daya ranta yayi baqi,sumayyan ta yaga mata tako ina,kyau da quruciya,akwai alamun nutsuwa tattare da ita sosai,hakan ta kwana da sanin lamba daya ce ita cikin zuciyar mukhtar din,don ko darensu na jiya ya bata amsa,duk yadda taso rikitashi ban manta sumayyan ba ita yake kira.
"Na gode ango mijin amarya,da fatan kun tashi lafiya" ta fada wajen kaiwa matuqa gurin boye kishi da damuwarta,sai ta dubi zainab
"Amarya ina kwana ya kwanan baqunta"
"Lafiya ya kike"ta fada tana yatsina tare da qoqarin baiwa mukhtar tea
"Qalau" itama sumayyan ta fada cikin yanayin data amsa mata tare da motsa kafada kana ta nufi kitchen don kaucewa ci gaba da kallon abinda ke faruwa.
Alamu sun nuna iyaka na cikinsu ne abincin,batasan waye yayi ba,amaryar ko mijin amaryar,koma waye dama bata da buqata,sai ta dora tea kan gas da a yanzu shi mukhtar ya siya mata take amfani da shi,ta bude kazar ta sake mata sabon hadi na spices,ta duba dan madaidaicin ovean dinta ta soma kici kicin hadawa tare da duba hanyoyin da ake hadawar.
Cikin haka mukhtar din ya shigi kitchen din dauke da kwanukan da suka ci abincin zainab din na biye da shi,bata bi takan sumayyan ba ta nufi side dinta ta dire kayan,mukhtar ya dubu sumayyan
"Me za'a girka mana ne naga ana hada ovean"
"Ai baka da buqatar abinci na malam" ta fada cikin gatse,murmushi yayi yana kallonta,lallai sumayyan ta fara zama babbar mace,tunda har tafara banbance tsakanin aya da tsakuwa.
Kafin ya furta komai muryar zainab ta ratsa kunnuwansu tana qwala masa kira cikin wani irin salo,tamkar an soketa a qirji amma saita basar,ya juya yana cewa da ita
"Ina zuwa"
"Banda buqatar dawowarka ma" ta fada kishi na cinta tana qoqarin danneshi.
Har ta kammala babu shi babu alamarsa,ta juye ta koma daki da abincinta zuciyarta na raunana,saboda wannan ne karo na farko data taba ganin sauyi daga gareshi har irin haka.
**** ***** ****
Cikin kwanakin wani amarci ta dinga gani cikin gidan wanda bata tsammata ba,baki daya kamar daukar mukhtar din akayi aka sauya mata shi,hutu ya dauka na fita kasuwa har na kwanaki bakwai,ko yaushe suna daki idan kaga fitowarsa salla ce zaya yi,saita wuni sur bata sanyashi cikin idanunta ba,abun na taba ranta saidai bata yarda ta fiya zurfafa lamarin cikin ranta,runda anty dije ta gaya mata dole zata iya ganin wasu sauye sauye duk son da yake mata,amarya kota buzuz ce sai an mata rawar qafa,to bare baya ga wannan babu wani sauyi da ta gani cikin ma'amalarsu shi da ita.
*KUNDIN QADDARA TA*
Kwanaki uku take zaton zaya yiwa zainab din tunda bazawara ce,sai gashi ya shiga cikin kwana na hudu biyar shida har zuwa bakwai.
Ranar kwana na bakwai din a ranar zaya soma fita kasuwa,tana kwance dakinta bayan sha daya na safe taji sallamarsa,sai ta miqe ta zauna tana amsa masa,fuskarta babu yabo babu fallasa,gefanta ya samu ya zauna yana fadin
"Ranki ya dade kinyi wuyar gani" ido ta daga ta dubeshi,lallai ne wai ita za'a yiwa halin maza,magana yake gaya mata a fakaice koko yaya,duk da hakan sai ta dake ta kuma basar ta kaufa zancan ta hanyar fadin
"Ina kwana"
"Lafiya sumy ta,kinga na qarawa zainab kwana ko,kinga baquwace tace kuma tan tsorom zama ita daya" wani haushi ya taso ya turniqeta,budurwa ce zainab din ko yau ta fara zaman gidan aure,ko ko tsabagen rainin wayo ne,wadan nan kalaman takeson gayawa mukhtar din amma girmansa da take gani yasa ta gaza furtasu ta hadiye kayanta sai ta bige da cewa
"Ko,Allah sarki" daga yanayin da tayi maganar kawai ya tabbatar masa cewa ta inda zancansa ya shiga ta nan ya fice.
So take ta bude baki da gaya masa magana ko zata ji sauqin tuquqin da zuciyarta ke maga amma sai ta kasa,girman mukhtar cikin idonta yafi gaban haka,miqewa tayi gudu gudu sauri sauri idonta na saukar da qwalla kan kuncinta,miqewa yayi biyita da sauri cike da muradin cimmata,saidai tuni ta afka toilet dinta ta rufe qofa tare da sakin kuka.
Bakin toilet din ya tsaya yana naci da magiyar ta fito,sai da suka kusa kwashe minti ashirin a haka,ba zata iya kallonsa ya tafi dakin wata ba hakan ya sanyata cikin muryar kuka tace
"Bana son ganinka yaya mukhtar ka tafi don Allah ka qyaleni"
"Yau nine sumayya baki son gani?.....yau......." Bai kamamala maganar ba wayarsa dake aljihun gaban rigarsa ya hau ruri,hannunshi ya zira,ganin mai kiran ya sanyashi dagawa
"Dear m,ina ka tsaya ne wai bayan na ji shigowarka",bazai iya tantance mai yaji ba,so yake ya rufeta da masifa amma sai ya kasa,maimakon haka sai ya bige da cewa
" ina gun yayarki zance ko qanwarki ina lallashi"gabanta ha fadi haushi ta turniqeta,kada fa ace duk abinda ake bata labari kan sumayyar gaskiya ne,amma babu komai saura qiris tayi maganin abun
"Lallashin me kuma dear bayan ba wannan ne karo na farko ba da aka fara mata kishiya,ka taho ko nazo da kaina na tafi da kai"
"Ok gani nan" ya fadi da sauri tare da katse kiran,maida idanunsa yayi ga qofar toilet din,ya tabbatar taji duk abinda suka ce,kamar sumayyan ce ke gabansa ya marairaice
"Shikenan sumayya zan tafi,ga ledarki can cikin daki Allah ya bamu alkhairi" ya fada yana juyawa.
Zamewa tayi tayi zaman dirshan saman tiles din bandakin sabon kuka na kubce mata wanda ta sanya tafin hannunta ta toshe bakinta don kada su jiyota,duk da cewa ita tace ya tafin bata yi tsammanin tafiyar tasa da gaggawa ba haka.
Ta jima tana kuka a ciki kafin ta lallashi kanta bayan tayi tilawar wasiyyoyin mahaifiyarta tun daga auren da aka qara mata na fari zuwa wannan da ya kasance na biyu.
Bata bar bayin ba sai da cikakkiyar alwala,ta koma daki ta sauya kayan bacci,doguwar riga ce har qasa mai taushi da kauri,hijabi ta dora saman riga ta shimfida abun sallaha ta tayar da sallah hawaye na layi kan kumatunta.
Yana shiga ta miqe ta taroshi cikin karairaya da yauqi,ta amshi ledar hannunsa ta ajjye kana ta rungumeshi,yaqe haqora kawai yake,ko daya bata burgeshi ba,alamu sun nuna babu kunya ko qwaya daya cikin idanunta,ko daya baiji dadin kasancewarta cikin jikinsa ba amma sai ya kasa cewa da ita komai,sai ya dinga dauko daren farkon sumayya da na fa'iza da nata yana hadawa,tuni lissafin ya wargaje don tako ina sun sha banban.
Biye yake da ita kawai sai ido da yake binta da shi,ita ta hada musu ruwa sukayi wanka sannan ta samo plate ta juye kazar a ciki,kusan ita ta dinga ciyar da shi ta kuma ci da kanta har suka kammala ta janyeshi gado don tuni ta dokanta,kusan ita ta gabatar da komai a maimakonshi,mamaki da haushi ke tuqeshi,gefe guda wani irin takaici wanda idan ya yunqura zaiyi magana sai yaji ya kasa cewa komai,data dubeshi kuma sai yaji komai ya wuce ya bar tasiri cikin ransa.
Kwana tayi zaune bayan ta gaji da yin sallolin,abinda bata taba zata zata iya ba,yaushe mukhtar ya sake zame mata wani na daban haka,ita kanta tana mamakin yadda ta koyi kishinsa har haka,sai da ta gabatar da sallar asuba taji idanunta sun soma nauyi da zugi,duk yadda taso ta yakice baccin amma bata samu nasara ba,haka yazo ya saceta cikin gaggawa ya kuma mata nauyi wanda hakan ya sanya ta gaza sanin meke wakana cikin gidan har misalin qarfe goma da rabi ma safe wanda ta farka a firgice.
Bandakin cikin dakinta ta shiga da yake bayan na corridor akwaai cikin daki,wanka tayi bayan ta wanke bakinta ta dawo cikin dakin,jikinta babu qwari ta shirya cikin atamfa doguwar riga wadda ta mata kyau,duk da bata jin qwarin jikinta amma tayi lite make up wadda ta dace da yanayinta,babu dauda ko qura a rea dinta sai dan kakkabe kakkabe kawai da tayi sannan ta fito don samawa kanta abinda zata ci koda ruwan zafi ne,don jinta take iska na yawo da ita tsabar babu komai a cikinta,ledar jiya mukhtar din ya bata ta dauka ta fice da ita.
Bata kula da su ba sai data shigo cikin falon sosai,mukhyat sanye da yadi mai taushi fari tas wanda ka yiwa aiki da zare ash,sai wandda idanunta suka sake sauka kanta wanda bata tantama itace zainab din.
Macace wadda kallo daya ta yi mata ta fuskanci ta girmesu ita da fa'iza baki daya,A qalla tayi shekaru ashirin ta takwas wanda hakan ke nuna ta girmi sumayyan da shekara goma tunda sai yanzu taje cikin shekararta ta goma sha tara,baqa ce zainab din amma ba baqi can ba,tana da cika wadda za'a iya kiranta qiba kai tsaye duk da wata mai yawa bace,bata daga cikin sahun kyawawa ko kadan amma zaiyi wuya kai tsaye ka kirata da mummuna saboda yanayin iya gogayya da iya salo,saidai tako ina sumayyan ta mata fintikau,abu daya zata iya nuna mata qwala qwalan idanu da suke zagayayyu suka fi na sumayya girma,sakamakon natan lumsassu ne ba kowanne lokaci kake iya gane girmansu ba,sanye take da material mai santsi wanda aka yiwa dinkin riga da skert,breakfast sukeyi wanda ya qunshi tea da soyayyen qwai da bread,sai kaji wanda ba tantama na jiya ne aka sake gasa su.
Shi ya soma ganinta lokacin da zainab ke qoqarin bashi naman a baki,sai ya goce wanda hakan ya janyo hankalin zainab din ta ankara da fitowar sumayyan,murmushi ya sakar mata yayin da itama tayi qoqarin maida masa martani
"Kin tashi kenan,na leqaki na taras kina bacci"
"Eh,ban jima ai da tashi ba" ta fada tana takowa gabansu
"Kinyi kyau sumy ta" ya fada yana sake dubanta wanda kalmar ba qaramin dukan qirjin zainab tayi ba,lokaci daya ranta yayi baqi,sumayyan ta yaga mata tako ina,kyau da quruciya,akwai alamun nutsuwa tattare da ita sosai,hakan ta kwana da sanin lamba daya ce ita cikin zuciyar mukhtar din,don ko darensu na jiya ya bata amsa,duk yadda taso rikitashi ban manta sumayyan ba ita yake kira.
"Na gode ango mijin amarya,da fatan kun tashi lafiya" ta fada wajen kaiwa matuqa gurin boye kishi da damuwarta,sai ta dubi zainab
"Amarya ina kwana ya kwanan baqunta"
"Lafiya ya kike"ta fada tana yatsina tare da qoqarin baiwa mukhtar tea
"Qalau" itama sumayyan ta fada cikin yanayin data amsa mata tare da motsa kafada kana ta nufi kitchen don kaucewa ci gaba da kallon abinda ke faruwa.
Alamu sun nuna iyaka na cikinsu ne abincin,batasan waye yayi ba,amaryar ko mijin amaryar,koma waye dama bata da buqata,sai ta dora tea kan gas da a yanzu shi mukhtar ya siya mata take amfani da shi,ta bude kazar ta sake mata sabon hadi na spices,ta duba dan madaidaicin ovean dinta ta soma kici kicin hadawa tare da duba hanyoyin da ake hadawar.
Cikin haka mukhtar din ya shigi kitchen din dauke da kwanukan da suka ci abincin zainab din na biye da shi,bata bi takan sumayyan ba ta nufi side dinta ta dire kayan,mukhtar ya dubu sumayyan
"Me za'a girka mana ne naga ana hada ovean"
"Ai baka da buqatar abinci na malam" ta fada cikin gatse,murmushi yayi yana kallonta,lallai sumayyan ta fara zama babbar mace,tunda har tafara banbance tsakanin aya da tsakuwa.
Kafin ya furta komai muryar zainab ta ratsa kunnuwansu tana qwala masa kira cikin wani irin salo,tamkar an soketa a qirji amma saita basar,ya juya yana cewa da ita
"Ina zuwa"
"Banda buqatar dawowarka ma" ta fada kishi na cinta tana qoqarin danneshi.
Har ta kammala babu shi babu alamarsa,ta juye ta koma daki da abincinta zuciyarta na raunana,saboda wannan ne karo na farko data taba ganin sauyi daga gareshi har irin haka.
**** ***** ****
Cikin kwanakin wani amarci ta dinga gani cikin gidan wanda bata tsammata ba,baki daya kamar daukar mukhtar din akayi aka sauya mata shi,hutu ya dauka na fita kasuwa har na kwanaki bakwai,ko yaushe suna daki idan kaga fitowarsa salla ce zaya yi,saita wuni sur bata sanyashi cikin idanunta ba,abun na taba ranta saidai bata yarda ta fiya zurfafa lamarin cikin ranta,runda anty dije ta gaya mata dole zata iya ganin wasu sauye sauye duk son da yake mata,amarya kota buzuz ce sai an mata rawar qafa,to bare baya ga wannan babu wani sauyi da ta gani cikin ma'amalarsu shi da ita.
*KUNDIN QADDARA TA*
Kwanaki uku take zaton zaya yiwa zainab din tunda bazawara ce,sai gashi ya shiga cikin kwana na hudu biyar shida har zuwa bakwai.
Ranar kwana na bakwai din a ranar zaya soma fita kasuwa,tana kwance dakinta bayan sha daya na safe taji sallamarsa,sai ta miqe ta zauna tana amsa masa,fuskarta babu yabo babu fallasa,gefanta ya samu ya zauna yana fadin
"Ranki ya dade kinyi wuyar gani" ido ta daga ta dubeshi,lallai ne wai ita za'a yiwa halin maza,magana yake gaya mata a fakaice koko yaya,duk da hakan sai ta dake ta kuma basar ta kaufa zancan ta hanyar fadin
"Ina kwana"
"Lafiya sumy ta,kinga na qarawa zainab kwana ko,kinga baquwace tace kuma tan tsorom zama ita daya" wani haushi ya taso ya turniqeta,budurwa ce zainab din ko yau ta fara zaman gidan aure,ko ko tsabagen rainin wayo ne,wadan nan kalaman takeson gayawa mukhtar din amma girmansa da take gani yasa ta gaza furtasu ta hadiye kayanta sai ta bige da cewa
"Ko,Allah sarki" daga yanayin da tayi maganar kawai ya tabbatar masa cewa ta inda zancansa ya shiga ta nan ya fice.