Sashe 60
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali ta dinga takawa har gaban gadon da mukhtar din ke kwance,ko ina na'ura ce ke aiki a jikinsa,baki daya fuskarsa ta sauya kamar ba mukhtar ba,kallo daya zaka masa kasan lallai ya bugu sosai a kansa don tuni har ya kumbura kan nasa,kujera ta ajjiye bakin gadon tana qoqarin danne zuciyarta tare da tuna nasihar da malam yayi kata kafin su tafi
"Kuka baya maganin komai,addu'a ita ke magani" abinda ya gaya mata na qarshe kenan,kanta ta girgiza tana sake baiwa kanta qwarin gwiwa,sai ta kama tafin hannunsa ta sanya cikin nata,a hankali murya can qasa mai cike da rauni ta soma karanto ayoyin qur'ani wadanda su suka dinga debe mata kewa tsawon daren,saidai abinda ke daga mata hankali dai dai da second daya babu wani abu da taga ya motsa daga jikinsa,wanda likitocin sunce ta kula ko yaya taga ya motsa ta sanar musu,duk da lokaci bayan lokaci suna shigowa suna sake dubashi.
Sai da suka saitu sosai kan hanya sannan mama tace
"Ina abdallah" tofa,sai lokacin hankalin kowa ya dawo jikinsa,duk cikinsu babu mai amsar tambayar,don hatta jama'ar da suka ceci mukhtar dim babu wanda yace yaga yaro,take wani sabon tashin hankalin ya samesu,mama kam kasa daurewa tayi saboda tsananin tausayin sumayya sai kawai ta sanya kuka,kai tsaye malam ya nemi alfarmar mai abun hawar ya canja akalarsa zuwa policestation wanda tafi kusa da inda al'amarin ya faru don si shigar da report cike da matsanancin tashin hankali.
Kiran sallar asubar fari sanyi ya fara busowa,sam bata lura ba tana gyara zamanta,tana daga kai suka hada idanu,ya bude idanuwansa tar yana kallonta,wani farinciki ya dinga zagaya ta,ga mamakinta taji sai taji ya kita sunanta,cikin matsanancin farinciki ta amsa
"Qarfe nawa?"
"An kusa sallar asuba"
"Daura min alwala sumayya banyi sallar magariba da isha ba" girgiza kai tayi
"Ya mukhtar jikinka duka kayan aiki ne,ka bari likita yazo sai ayi maka" tubure mata yayi hakan ya sanya ta lallaba ta shashshafa masa ruwan iya inda zai yiwu,yana daga kwancen ya dinga halarto da sallar yana yi har ya kammala baki daya tana zaune tana kallonsa,yana sallamar qarshe kansa saitinta ne sai ya zuba mata idanu,murmushi tayi tace
"Sannu ya mukhtar" kai ya kada mata sannan yace
"Ina abdallah" abdallah,ta dinga nanatawa,idan kunnuwanta basuyi mata qarya ba ance tare suke da abdallah,to ina yake ina yayi?
"Ina fata lafiya yake babu abinda ya sameshi" tabbas lafiya yake idan da ba lafiya ba da sun gaya mata
"Lafiya yake ya mukhtar" ta fada cikin salon son kwantar da hankalinsa
"Alhamdulillah" taji ya fada sai ya maida kansa,cikin farinciki da tada sallah itama.
Shaquwa taji ya soma yi wadda kan ta idar da sallar ta qara yawa,tana sallamewa tayi kansa tana masa sannu,da hanzari ta dauko ruwan roba ta bude ta fara bashi a hankali,sosai ya sha ruwan kuwa sannan ta cire roban daga bakinsa ta qulle tana masa sannu,minti biyar tsakani shaquwar ta dawo,ta sake matsawa gunsa tana riqe da hannunsa tana masa sannu cikin tashin hankali ganin yadda qirjinsa ke dagawa wannan karon
"Bari na qara maka ruwan" ta fadi tana shirin juyawa inda gorar ruwan take,sai taji ya damqe hannunta,juyowa tayi tare da tsayawa cak kamar an kafeta,idanuwansa taga sun fara juyewa,jikinta ya hau rawa ta qanqame hannunsa tana fadi a fili
"La'ilaha ilallah,muhammadur rasulullah" abinda ta dinga maimaitawa kenan a fili babu qaqqautawa,a hankali taji ya kama yana maimaitawa,kusan minti biyu yana fada shima cikin fusgar numfashi sai taga idanunsa na lumshewa,riqon da ya yiwa hannunta tsaurinsa ya sassauta
(Abinda ake so ga kowanne majinyaci kenan,mutuwa na da sa gigita da daga hankali,amma gata ake so ka yiwa mamaci wanda shine qarshen qaunar da zaka nuna masa,a yayin daka fuskanci wasu alamu na fitar ruhi daga gangar jikin majinyaci,bakinka ya dinga ambaton la'ilaha ilallahu muhammadur rasulullah ko za'a dace mamaci ya kama,ba cewa ake fadi abinda na fada ba,ko kuma cene la'ilaha ilallah,a'a ka dinga fadi yadda kunnuwansa zasu iya ji,idan Allah ya qaddara bawansa ne na gari sai ya kama ya kuma cika da ita,Allah kasa mu cika da wannan kalma mu da daukacin musulmi baki daya,amin).
Hannunta ta zare qirjinta na fat fat fat,hawaye ne ke bin kuncinta,wasi wasi ya cika zuciyarta,fata take ba abinda take zato bane,wannan tunani ya sanyata fita da gudu tayi ofishin likitan.
*mrs muhammad ce*
*Fatan alkhairi ga*
*oum imaan*
*mmn husna*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣9⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*assalamu alaikum*
*da fari ina neman afuwa ga wadanda na sanya kuka,Allah yayi mana kyakkyawan qarshe,haka rayuwa take zaqi da madaci*
_abu na biyu da nake so makaranta su gane shine,haqiqa Allah baya barin wani don wani yaji dadi,ko kuwa don kuna tsaka da farinciki sai Allah ya kasa dauke bawansa alhali ajalinsa yazo?,na tabbata ni ke ko kai an taba dauke mana masoyanmu,uwa,uba, 'ya'ya,qawaye maqwafta ko dangi,wala allah muna tsaka da jin dadin rayuwarmu bamu zatan musu mutuwa ba,ba kuma tare da sunyi sallama da mu ba,amma Allah ya daukesu saboda lokacinsu yayi kamar yadda Allah madaukaki ke fada a alqur'ani_
_(iza ja'a ajluhum la yasta'akiruna sa'atan wala yastaqdimun/idan lokacinsu yazo ba'a jinkirta musu sa'a daya kuma ba'a gaggauto da ita ma'ana su tafi alhalin suna da sauran minti daya cikin duniya)_
_(kullu nafsin za'iqatul maut)_
_(kullu man alaiha faan)_
_duk abinda ke kanta(qasa)qararre ne_
_mutuwa dole ce idan tazo sai an tafi,babu wanda zai dawwama cikin duniya ko shekara miliyan nawa zaiyi sai ya tafi,cikin dadi ko wuyar da kake ciki babu ruwan ubangiji,na tabbata babu wanda ba'a taba yiwa mutuwa ba,babu wanda bai taba rashin wani nasa ba,fatanmu Allah yasa mu cika da kyau da imani_
*sannan ina cewa masu karatu sun manta sunan littafin kenan KUNDIN QADDARATA?,kowa ya san rayuwa tafe take da qaddara,cikar imanin mumini kenan a jarrabceshi,jarrabawa na zamowa kankarar zunubi ga mumini,Allah ya bamu ikon cinye jarabobinmu*
*wa bash shiris saabirin,Allazina iza asabathum musibatun qalu innalillahi wa inna ilaihi raji'un*
*_KA YIWA MASU HAQURI BUSHARA,SUNE WADANDA IDAN MASIFA TA SAMESU SUKE CEWA MU DAGA ALLAH MUKE KUMA MU GARESHI NE ZAMU KOMA(innalillahi wa inna ilaihi raji'un)_*
________________________________
A rude ta fada ofishin likitan tana kiransa,likita ne mai kirki,ya gane ko wacece saboda haka ya miqe kawai ya biyota,zata fada dakin ya dakatar da ita yace ta jira a waje
"Sumayya,jikin muntarin ne?" Kawu wanda idar da sallarsu kenan daga masallaci suka yo cikin asibitin suka tambayeta
"Kai kawai ta iya daga musu hawaye na bin kuncinta,don bata jin zata iya cewa komai,jiri ta fara ji yana neman kayar da ita saboda tashin hankali da mintinan da suka kwashe a tsaye,sabida haka sai ta daddafa ta zauna kan kujerar sake barandar dakin.
Likitoci biyu ne suka zo suka sake shigewa dakin suna nan zaune,awa guda ta kusa shudewa dai dai lokacin da mama halima da zainab suka iso,yayin da malam ya fara biyawa ta police station ko an samu labarin abdallah,jikin mama ta jingina kawai ta kwantar da kanta a kafadarta ba um ba um-um,sannu maman ke mata tana tambayar jikin mukhtar din,kawu ne ya amsa mata da cewa da sauqi don baki dayansu hankalinsu bai jikinsu.
Budewar qofar dakin ne ya ja hankalinsu,likita na farko ya wuce baice musu komai ba,na biyu ma haka,na ukun ne ya tako gabansu a hankali sannan ya dubesu
" dukkan mai rai mamaci ne wannan alqawarin Allah ne babu mai zama cikin duniya sai ya tafi,ina mai baku haquri,Allah ya yiwa mara lafiyanku cikawa,sai kuyi masa addu'a",kuka ne da salati ya gauraye wajen,wani dogon numfashi sumayya ta ja,cikin daga murya wadda bata san ta yita ba ta furta
"INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN,ALLAHUMMA AJIRNI FI MUSIBATI WA AKHLIFNI KHAIRAN MINHA" tun daga haka bafa dada ba bata rage ba,don ba sosai take ganewa ba,bin kowa kawai take da idanuwa.
Isowar yaya yahanasu shi ya sake ruda gurin,zubewa tayi a qasa tana kuka kamar ranta zai fita,daga bisani ta sume a nan,sai da aka bata taimakon gaggawa sannan ta dawo hayyacinta,zuwa lokacin an kammala settling na tafiya da gawar mukhtar,motar asibiti suka basu a kaishi ciki(ambulance)itakam sumayya ido kawai take bin kowa da shi,sai ajiyar zuciya da take ta faman saki har suka isa gidansu na aure,gidan da suka tanada domin sabunta rayuwar aurensu,gidan da suka ciwa burin sake gina kyakkyawar alaqa da danganta har gaban ABADAN,ashe wannan mafarki nasu bazai cika ba,ashe wannan buri nasu yankakke ne,ashe sunyi zaman qarshe da mukhtar kenan a daren jiya?,abinda ya dinga bijiro mata kenan,kallon mutane take suna kuka,sai ta dinga jin dama itace su,dama itama zatayi kuka,domin kuka ya fiye mata sau dubu akan bala'i da sukar da take ji a qirjinta.
Cikin uwar dakanta aka wuce da ita aka zaunar da ita,har lokacin babu um ba um um sai ido kawai,a falo aka kwantar da mukhtar,aka bawa makusantansa dama suka wanke shi aka maaa suttura sannan aka buqaci 'yan uwansa suje suyi masa sallama,take gidan ya sake rudewa da koke koke,hakanne yasa anty salma tace a bar kowa ya gama shiga sannan sumayya ta shiha daga baya,da qyar aka fidda su yaya yahanash,kuka take tana ya yafe mata,itakam ta yafe masa dan bai taba saba mata ba,tsakaninsu biyayya ce irinta d'a da uwarsa tunda ta fara riqonsa har ta aurar da shi.
"Kuka baya maganin komai,addu'a ita ke magani" abinda ya gaya mata na qarshe kenan,kanta ta girgiza tana sake baiwa kanta qwarin gwiwa,sai ta kama tafin hannunsa ta sanya cikin nata,a hankali murya can qasa mai cike da rauni ta soma karanto ayoyin qur'ani wadanda su suka dinga debe mata kewa tsawon daren,saidai abinda ke daga mata hankali dai dai da second daya babu wani abu da taga ya motsa daga jikinsa,wanda likitocin sunce ta kula ko yaya taga ya motsa ta sanar musu,duk da lokaci bayan lokaci suna shigowa suna sake dubashi.
Sai da suka saitu sosai kan hanya sannan mama tace
"Ina abdallah" tofa,sai lokacin hankalin kowa ya dawo jikinsa,duk cikinsu babu mai amsar tambayar,don hatta jama'ar da suka ceci mukhtar dim babu wanda yace yaga yaro,take wani sabon tashin hankalin ya samesu,mama kam kasa daurewa tayi saboda tsananin tausayin sumayya sai kawai ta sanya kuka,kai tsaye malam ya nemi alfarmar mai abun hawar ya canja akalarsa zuwa policestation wanda tafi kusa da inda al'amarin ya faru don si shigar da report cike da matsanancin tashin hankali.
Kiran sallar asubar fari sanyi ya fara busowa,sam bata lura ba tana gyara zamanta,tana daga kai suka hada idanu,ya bude idanuwansa tar yana kallonta,wani farinciki ya dinga zagaya ta,ga mamakinta taji sai taji ya kita sunanta,cikin matsanancin farinciki ta amsa
"Qarfe nawa?"
"An kusa sallar asuba"
"Daura min alwala sumayya banyi sallar magariba da isha ba" girgiza kai tayi
"Ya mukhtar jikinka duka kayan aiki ne,ka bari likita yazo sai ayi maka" tubure mata yayi hakan ya sanya ta lallaba ta shashshafa masa ruwan iya inda zai yiwu,yana daga kwancen ya dinga halarto da sallar yana yi har ya kammala baki daya tana zaune tana kallonsa,yana sallamar qarshe kansa saitinta ne sai ya zuba mata idanu,murmushi tayi tace
"Sannu ya mukhtar" kai ya kada mata sannan yace
"Ina abdallah" abdallah,ta dinga nanatawa,idan kunnuwanta basuyi mata qarya ba ance tare suke da abdallah,to ina yake ina yayi?
"Ina fata lafiya yake babu abinda ya sameshi" tabbas lafiya yake idan da ba lafiya ba da sun gaya mata
"Lafiya yake ya mukhtar" ta fada cikin salon son kwantar da hankalinsa
"Alhamdulillah" taji ya fada sai ya maida kansa,cikin farinciki da tada sallah itama.
Shaquwa taji ya soma yi wadda kan ta idar da sallar ta qara yawa,tana sallamewa tayi kansa tana masa sannu,da hanzari ta dauko ruwan roba ta bude ta fara bashi a hankali,sosai ya sha ruwan kuwa sannan ta cire roban daga bakinsa ta qulle tana masa sannu,minti biyar tsakani shaquwar ta dawo,ta sake matsawa gunsa tana riqe da hannunsa tana masa sannu cikin tashin hankali ganin yadda qirjinsa ke dagawa wannan karon
"Bari na qara maka ruwan" ta fadi tana shirin juyawa inda gorar ruwan take,sai taji ya damqe hannunta,juyowa tayi tare da tsayawa cak kamar an kafeta,idanuwansa taga sun fara juyewa,jikinta ya hau rawa ta qanqame hannunsa tana fadi a fili
"La'ilaha ilallah,muhammadur rasulullah" abinda ta dinga maimaitawa kenan a fili babu qaqqautawa,a hankali taji ya kama yana maimaitawa,kusan minti biyu yana fada shima cikin fusgar numfashi sai taga idanunsa na lumshewa,riqon da ya yiwa hannunta tsaurinsa ya sassauta
(Abinda ake so ga kowanne majinyaci kenan,mutuwa na da sa gigita da daga hankali,amma gata ake so ka yiwa mamaci wanda shine qarshen qaunar da zaka nuna masa,a yayin daka fuskanci wasu alamu na fitar ruhi daga gangar jikin majinyaci,bakinka ya dinga ambaton la'ilaha ilallahu muhammadur rasulullah ko za'a dace mamaci ya kama,ba cewa ake fadi abinda na fada ba,ko kuma cene la'ilaha ilallah,a'a ka dinga fadi yadda kunnuwansa zasu iya ji,idan Allah ya qaddara bawansa ne na gari sai ya kama ya kuma cika da ita,Allah kasa mu cika da wannan kalma mu da daukacin musulmi baki daya,amin).
Hannunta ta zare qirjinta na fat fat fat,hawaye ne ke bin kuncinta,wasi wasi ya cika zuciyarta,fata take ba abinda take zato bane,wannan tunani ya sanyata fita da gudu tayi ofishin likitan.
*mrs muhammad ce*
*Fatan alkhairi ga*
*oum imaan*
*mmn husna*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣9⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*assalamu alaikum*
*da fari ina neman afuwa ga wadanda na sanya kuka,Allah yayi mana kyakkyawan qarshe,haka rayuwa take zaqi da madaci*
_abu na biyu da nake so makaranta su gane shine,haqiqa Allah baya barin wani don wani yaji dadi,ko kuwa don kuna tsaka da farinciki sai Allah ya kasa dauke bawansa alhali ajalinsa yazo?,na tabbata ni ke ko kai an taba dauke mana masoyanmu,uwa,uba, 'ya'ya,qawaye maqwafta ko dangi,wala allah muna tsaka da jin dadin rayuwarmu bamu zatan musu mutuwa ba,ba kuma tare da sunyi sallama da mu ba,amma Allah ya daukesu saboda lokacinsu yayi kamar yadda Allah madaukaki ke fada a alqur'ani_
_(iza ja'a ajluhum la yasta'akiruna sa'atan wala yastaqdimun/idan lokacinsu yazo ba'a jinkirta musu sa'a daya kuma ba'a gaggauto da ita ma'ana su tafi alhalin suna da sauran minti daya cikin duniya)_
_(kullu nafsin za'iqatul maut)_
_(kullu man alaiha faan)_
_duk abinda ke kanta(qasa)qararre ne_
_mutuwa dole ce idan tazo sai an tafi,babu wanda zai dawwama cikin duniya ko shekara miliyan nawa zaiyi sai ya tafi,cikin dadi ko wuyar da kake ciki babu ruwan ubangiji,na tabbata babu wanda ba'a taba yiwa mutuwa ba,babu wanda bai taba rashin wani nasa ba,fatanmu Allah yasa mu cika da kyau da imani_
*sannan ina cewa masu karatu sun manta sunan littafin kenan KUNDIN QADDARATA?,kowa ya san rayuwa tafe take da qaddara,cikar imanin mumini kenan a jarrabceshi,jarrabawa na zamowa kankarar zunubi ga mumini,Allah ya bamu ikon cinye jarabobinmu*
*wa bash shiris saabirin,Allazina iza asabathum musibatun qalu innalillahi wa inna ilaihi raji'un*
*_KA YIWA MASU HAQURI BUSHARA,SUNE WADANDA IDAN MASIFA TA SAMESU SUKE CEWA MU DAGA ALLAH MUKE KUMA MU GARESHI NE ZAMU KOMA(innalillahi wa inna ilaihi raji'un)_*
________________________________
A rude ta fada ofishin likitan tana kiransa,likita ne mai kirki,ya gane ko wacece saboda haka ya miqe kawai ya biyota,zata fada dakin ya dakatar da ita yace ta jira a waje
"Sumayya,jikin muntarin ne?" Kawu wanda idar da sallarsu kenan daga masallaci suka yo cikin asibitin suka tambayeta
"Kai kawai ta iya daga musu hawaye na bin kuncinta,don bata jin zata iya cewa komai,jiri ta fara ji yana neman kayar da ita saboda tashin hankali da mintinan da suka kwashe a tsaye,sabida haka sai ta daddafa ta zauna kan kujerar sake barandar dakin.
Likitoci biyu ne suka zo suka sake shigewa dakin suna nan zaune,awa guda ta kusa shudewa dai dai lokacin da mama halima da zainab suka iso,yayin da malam ya fara biyawa ta police station ko an samu labarin abdallah,jikin mama ta jingina kawai ta kwantar da kanta a kafadarta ba um ba um-um,sannu maman ke mata tana tambayar jikin mukhtar din,kawu ne ya amsa mata da cewa da sauqi don baki dayansu hankalinsu bai jikinsu.
Budewar qofar dakin ne ya ja hankalinsu,likita na farko ya wuce baice musu komai ba,na biyu ma haka,na ukun ne ya tako gabansu a hankali sannan ya dubesu
" dukkan mai rai mamaci ne wannan alqawarin Allah ne babu mai zama cikin duniya sai ya tafi,ina mai baku haquri,Allah ya yiwa mara lafiyanku cikawa,sai kuyi masa addu'a",kuka ne da salati ya gauraye wajen,wani dogon numfashi sumayya ta ja,cikin daga murya wadda bata san ta yita ba ta furta
"INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN,ALLAHUMMA AJIRNI FI MUSIBATI WA AKHLIFNI KHAIRAN MINHA" tun daga haka bafa dada ba bata rage ba,don ba sosai take ganewa ba,bin kowa kawai take da idanuwa.
Isowar yaya yahanasu shi ya sake ruda gurin,zubewa tayi a qasa tana kuka kamar ranta zai fita,daga bisani ta sume a nan,sai da aka bata taimakon gaggawa sannan ta dawo hayyacinta,zuwa lokacin an kammala settling na tafiya da gawar mukhtar,motar asibiti suka basu a kaishi ciki(ambulance)itakam sumayya ido kawai take bin kowa da shi,sai ajiyar zuciya da take ta faman saki har suka isa gidansu na aure,gidan da suka tanada domin sabunta rayuwar aurensu,gidan da suka ciwa burin sake gina kyakkyawar alaqa da danganta har gaban ABADAN,ashe wannan mafarki nasu bazai cika ba,ashe wannan buri nasu yankakke ne,ashe sunyi zaman qarshe da mukhtar kenan a daren jiya?,abinda ya dinga bijiro mata kenan,kallon mutane take suna kuka,sai ta dinga jin dama itace su,dama itama zatayi kuka,domin kuka ya fiye mata sau dubu akan bala'i da sukar da take ji a qirjinta.
Cikin uwar dakanta aka wuce da ita aka zaunar da ita,har lokacin babu um ba um um sai ido kawai,a falo aka kwantar da mukhtar,aka bawa makusantansa dama suka wanke shi aka maaa suttura sannan aka buqaci 'yan uwansa suje suyi masa sallama,take gidan ya sake rudewa da koke koke,hakanne yasa anty salma tace a bar kowa ya gama shiga sannan sumayya ta shiha daga baya,da qyar aka fidda su yaya yahanash,kuka take tana ya yafe mata,itakam ta yafe masa dan bai taba saba mata ba,tsakaninsu biyayya ce irinta d'a da uwarsa tunda ta fara riqonsa har ta aurar da shi.