Sashe 18
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin kwanakin da suka biyo baya damina ta shigo,wanda hakan shi yayi sanadiyyar zubewar ginin maqotan yaya yahanasu ya fadowa gidansu har ya janyo rushewar wani bangare na gidan,hakan ya sanya mukhtar yace su baro gidansh su dawo gidansa don a samu sararin gyaran gidan nasu,ko bayan rasuwar mai gidan anty yahanasu kusan shine jigo dake d'awainiya wa su yaya yahanasun.
Qarfe biyu na azahar suka iso gidan tare da yaranta biyu jamila da sayyada,sumayya na tsakar gida a lokacin tana wankin kayanta,da fara'arta ta taso tana musu sannu da zuwa tare da qoqarin karbar jakar hannun yaya yahansun bayan yara sun gama shigewa da sauran kayayyakin nasu d'akin fa'iza,kaucewa tayi gami da jifanta sa wani kallo tana fadin
"Kada ki kuskura ki taba min jaka,matsa da Allah ki bawa mutane guri" ta fada tana wuceta sauran yaran suka mara mata baya,a salube ta koma kan wankinta taci gaba da yi har ta kammala tana jiyo shewarsu cikin dakin fa'izan kai kace yaya yahanasun sa'arta ce,ya tabbatar cewa da ita ke shewa haka da yaya yahanasun sai ace bata da mutunci bata da kunya,amma ga fa'iza na faman shewa da qyaqyatawa gabanta,matar da ko sau daya sumayyan bata iya hada idanu da ita,biyayya take mata tamkar uwar mijinta haka ta dauketa sakamakon ganin irin girman matsayin da take da shi gun mukhtar.
Tana kammala shanya kayan ta shige wanka saboda tana so taje kitso sakamakon ita ke da girki gobe,har ta fito ta gama shiryawa ko alamun dora abinci babu gun fa'iza,itama bata damu ba sai ta hada shayi kawai ta sha tayi ficewarta ta barsu.
Qarfe biyar ta dawo gidan saboda layi da ta taras a gidan kitson,tun daga qofar gida ta soma jin muryar fa'iza cikin balbalin bala'i,ta kutsa kai cikin gidan cikin mamakin ita da wa,dai dai lokacin da fa'izar ke fadin
"Yo da kika damen da zancan ciki laifin uban waye mayun 'ya'ya?,qanin naki yayi min cikin mana ya gani idan ban dauka ba,wata uwar yake yimin idan kwana na ne banda kwanciya da zaki uzzura min,to wallahi babu ma mai kwanarmin cikin daki balle ya sanya min ido,dama daki ba daki ba ya zuciyar talaka,sai ku nemi gun kwana" ta fada tana komawa cikin dakin tare da banko labulenta.
Idanu sumayya tabi tsakar gidan nasu da shi,ko ina kaya ne na yaya yahanasun a barbaje a qasa,gaban sumayyan ya fadi,jikinta yayi sanyi,ta qarasa tsakar gidan,hannu ta sanya tana tattare kayan nasu waje daya,tsawa yaya yahanasun ta daka mata
"Kada ki sake taba mana kaya shegiya munafuka 'yar gidan malamai,to wallahi bari na gaya miki idan ma shiga tsakaninmu kikayi da fa'iza kinyi kadan,hakan da takeyi bazai tunzura zuciyata tunda nasan ba cikin hayyacinta take ba,ke sayyada maza ku hade mana kayan gefe guda mu jira shi muntarin ya dawo" sororo tayi tana dubanta
"Daina kallo na mayya,li'ilafi quraishi,ni baki isa ki cinyeni ba" sai ta kauda kai ta wuce kai tsaye dakinta ta bude ta shige.
Bata sake fitowa yayi zamanta cikin dakin,sai ta qirqiro wasu 'yan qananun ayyaukan ma cikin dakin nata don kawar da duk wani tunani da zai dameta,tana aikin tana ambatar hasbunallahu wa ni'imal wakil,allahumk finihim bima shi'ita,hakan ba qaramin taimaka mata yayi ba,sai ya tafiyar da lokacinta cikin sauqi har aka kira sallar magariba,ta miqe ta fito domin daura alwala,suna zaune gefe daya na tsakar gidan da qullin kayansu,sosai har cikin zuciyarta taji babu dadi,bai kamata mukhyar yazo ya taras da su haka ba,ko babu komai 'yan uwansa ne jininsa ne,kuma tayi imami cewa idan wani nata ne shima mukhtar din ba zaya wofantar da su haka ba,ta danne zuciyarta ta qarasa gurinsu,cikim sanyin murya tace
"Don Allah yaya ki shigi dakina,ko da ba zaki zauna din ba ki shigo idan yaso idan ya mukhtar din ya dawo sai asan yadda za'ayi din" wani kallon banza ta bita da shi
"Ke wallahi ki fita a idona,wai ke wacce iriyar mayatacciya ce ne,nace bazan shiga ba dole ne,to bari kiji,idan ma wani laqani aka baki na sai na shiga sannan zaki samu galaba a kaina to wallahi ki gayawa malaminki kunyi qarya kun kwana da yunwa" jikinta sai yayi sanyi ta kasa tafiya,zuciyarta na gaya mata basu zama masu kyautawa mukhtar ba indai yazo ya tadda jininsa a wulaqance,duk da tarin izgilu cin fuska da cin mutunci da ita yaya yahanasun ke jifanta da shi,ba ita take dubawa karamcin mukhtar take dubawa.
A haka mukhtar din ya shigo ya riskesu,tayi masa sannu da zuwa ta karbar kayan hannunsa duk da ba ranar girkinta bane,ya amsa yana duban yaya yahanasu."a'ah,yaya yanzu kuka zone na ganku a nan a zaune ku da kayanku"kai ta girgiza
"Inaaa,ai tun azahar muna gidan nan" cikin mamaki ya dubeta tare da zaro ido sai ya dubi sumayya yana jifanta da tuhuma,qas tayi da kanta don bata da ta cewa,ganin haka yasa ya dubi yaya yahanasun
"Amma kuke zaune a nan?,kada kice min nan kuka wuni?" Waiwayawa tayi ta dubi sumayya
"Sai ki bamu guri ko ko ban isa ba?" Bata ce uffan ba ta koma dakinta duk da alwala ta fito da niyyar daurawa.
Sai da taga shigarta dakin sannan ta maido dubanta ga fa'iza
"Mutuniyar tamu,wallhi lafiya lau ta karbemu,daga yi mata tambaya kan naji shiru har yanzu mun samu qaruwa ko a'ah ta shiga masifa ta inda take shiga ba ta nan take fita ba,qarshe tayo mana waje da kayanmu" sosai ransa ya baci,ya soma huci cikin fushi yace
"Fa'izar?,to da tayi muku haka gidanta ne ko nawa?,bazan lamunci wannan iskanci ba" ya fada yana juyawa zuwa ga dakinta wanda fa'izar na ciki tana jin kowa tayi lakur abinta.
Da sauri yaya yahanasun ta dakatar da shi
"Kaga muntari bana son hauka fa,laifi muka yi mata mu mika bata mata rai,nasan kuma zata huce,don haka bance kaje ka sake bata mata rai ba,kadai lallabata har ta yarda mu zauna taren" jagale yayi tare da juyiwa yana duban yayar tasa,take kuma ya tuna sunfi kusa fa ita da fa'izan,ya ma kamata a yau din ya qyaleta taga halin fa'izan taga wace ita ra'ayil ain wato ganin ido,saboda haka sai ya saki murmushi cikin salon canza shawarar da yayi farat daya,gyada kai yayi
"Shikenan,muje to a lallabatan" da sauri suka miqe yaya yahanasun tana cewa
"To,to ai kaga hakan yafi" tabi bayansa.
Tana miqe daga kan gadonta tana taunar chewing gum dai dai,zama sukayi kan kujerarta dake fuskantar gadon,yayin da mukhtar ya qarasa gefan gadon ya tsaya,duk da cewa ransa a matuqar bace yake,ji yake kamar ya janyo fa'izan ya yi mata dan banzan duka ya watsar amma sai ya dake
"Fa'iza,me yasa ba zaki bar yaya ta zauna dakinki ba,ai ina ganin bai kamata ba" hura hanci take tana tunanin ko yanzu mukhtar ya soma tsoronta,inko haka ne kowa tasa ta qare,tabbas sai kowa ma yaci ubansa cikin gidan
"Mukhtar banga dama bane,bari kaji" ta fada tana miqewa zaune kan gadon
"Na farko bansan sa ido gaskiya kuma na fuskanci su sun fara koyar wannan halayyar,na biyu na fuskanci ni aka rainawa wayo,ga mai daki ciki da falo can ba'a dosheta ba saini mai daki daya kamar zuciyar talaka" ba qaramin dukansa maganar tayi a zuciya ba amma ya hadiye don so yake ya jata aje gun ta dora da
"Saboda haka su nemi gurin kwana don ni bazan zauna da wadan nan qattan a daki na ba" wani qullutun abu ne ya tokare masa wuya qanda ya hanashi sake magana,sai yaya yahanasu da tace
"Haba ke kuwa fa'iza,kwana nawa ne duka duka mun koma gidanmu,ai ban zaci ko wani na turo gidan nan ki masa sauki a dakinki ba zaki kasa,kada fa ki manta nice silar zuwanki gidan nan" zabura tayi tana dakatar da ita
"Kinga kada ki sake kice zaki mun gori,don ke kika kawoni gidan ai bake kike aure na ba,buqatar maje haji sallah kuma da taku buqatar ai ba haka siddan kika kawoni ba,sabida haka kuje ni don Allah kada ku cikan kunne,tunda kun nace sai kun zauna a dakin kuje zanyi tunani,ko kwana daya ne kuyi kafin ku koma inda kuka fito".
Ba qaramin daurewa kan yaya yahanasun yayi ba da kalaman fa'iza,duk yadda fadima ke gaya mata sai yau ta sake tabbatarwa da lamba daya ce ita wajen rashin mutunci tsiya da tsiyataku
" fa'iza ni kike gayawa haka"kanga tsaye babu kunya tace
"Na fada din,ke kike aurena ne nace wai kawai da zaki takuran,wannan fa kamar kina lissafin sau nawa nake kwanciya da mijina ne"tuni maganar ta sake dora yaya yahanasun kan dokin zuciya
" ke qaramar mara kunya,ko bani nake aurenki ba kinsan ina da power din da zan sa ungulu ta koma gidanta na tsamiya ko?"
"Bismillah,sai mu gani " ta fada tana murguda baki gami da turo daurinta gaban goshinta ta dage kanta idanunta na kallon ceiling din daki.
tabbas tana jin yau idan bata nunawa fa'iza isar da take da ita a wajen mukhtar ba bata huce takaici ba,idanunta taf da bacin rai ta dubeshi
"Mukhtar,ina so a yau yau din nan ka sawwaqewa fa'iza,yanzun nan" ta qarashe cikin daga murya.
Duk da cewa ranshi ya kai qololuwa wajen baci kan abinda fa'izq ta yiwa yaya yahanasun amma sai ya danne komai tamkar bai b'aci ba,ai dama duk wanda ya sai rariya yasan zata zub da ruwa,to ya kamata yaya yahanasun taga yadda tata rariyar ke zubar da nata ruwan,ruwan kuma da baiyi qasa a gwiwar malalowa ya jiqata sharkaf ba,kai ya kada sannan yace
"Kan me zan saki fa'iza yaya,ni babu abinda ta yimin,hasalima fa'iza ai zabinki ce,kinga bai kamaci na wofantar da ita ba,zan riqeta hannu bibbiyu kamar yadda kika umarceni" tsawa ta daka masa
"Mukhtar,kai makaho ne?,ko kuwa kai kurma ne,baka ganin abinda ta yimin ne,ni na umarceka nace ka saketa kamar yadda na umarceka ka aureta a baya" kai ya sake kadawa tare da yin tattaki don barin dakin yana cewa
"Ki gafarceni yaya,amma yanzu na fara zama da fa'iza,don ni bata aikata min komai ba" sai ya fice abinsa ya barsu ana kallon kallo.
Qarfe biyu na azahar suka iso gidan tare da yaranta biyu jamila da sayyada,sumayya na tsakar gida a lokacin tana wankin kayanta,da fara'arta ta taso tana musu sannu da zuwa tare da qoqarin karbar jakar hannun yaya yahansun bayan yara sun gama shigewa da sauran kayayyakin nasu d'akin fa'iza,kaucewa tayi gami da jifanta sa wani kallo tana fadin
"Kada ki kuskura ki taba min jaka,matsa da Allah ki bawa mutane guri" ta fada tana wuceta sauran yaran suka mara mata baya,a salube ta koma kan wankinta taci gaba da yi har ta kammala tana jiyo shewarsu cikin dakin fa'izan kai kace yaya yahanasun sa'arta ce,ya tabbatar cewa da ita ke shewa haka da yaya yahanasun sai ace bata da mutunci bata da kunya,amma ga fa'iza na faman shewa da qyaqyatawa gabanta,matar da ko sau daya sumayyan bata iya hada idanu da ita,biyayya take mata tamkar uwar mijinta haka ta dauketa sakamakon ganin irin girman matsayin da take da shi gun mukhtar.
Tana kammala shanya kayan ta shige wanka saboda tana so taje kitso sakamakon ita ke da girki gobe,har ta fito ta gama shiryawa ko alamun dora abinci babu gun fa'iza,itama bata damu ba sai ta hada shayi kawai ta sha tayi ficewarta ta barsu.
Qarfe biyar ta dawo gidan saboda layi da ta taras a gidan kitson,tun daga qofar gida ta soma jin muryar fa'iza cikin balbalin bala'i,ta kutsa kai cikin gidan cikin mamakin ita da wa,dai dai lokacin da fa'izar ke fadin
"Yo da kika damen da zancan ciki laifin uban waye mayun 'ya'ya?,qanin naki yayi min cikin mana ya gani idan ban dauka ba,wata uwar yake yimin idan kwana na ne banda kwanciya da zaki uzzura min,to wallahi babu ma mai kwanarmin cikin daki balle ya sanya min ido,dama daki ba daki ba ya zuciyar talaka,sai ku nemi gun kwana" ta fada tana komawa cikin dakin tare da banko labulenta.
Idanu sumayya tabi tsakar gidan nasu da shi,ko ina kaya ne na yaya yahanasun a barbaje a qasa,gaban sumayyan ya fadi,jikinta yayi sanyi,ta qarasa tsakar gidan,hannu ta sanya tana tattare kayan nasu waje daya,tsawa yaya yahanasun ta daka mata
"Kada ki sake taba mana kaya shegiya munafuka 'yar gidan malamai,to wallahi bari na gaya miki idan ma shiga tsakaninmu kikayi da fa'iza kinyi kadan,hakan da takeyi bazai tunzura zuciyata tunda nasan ba cikin hayyacinta take ba,ke sayyada maza ku hade mana kayan gefe guda mu jira shi muntarin ya dawo" sororo tayi tana dubanta
"Daina kallo na mayya,li'ilafi quraishi,ni baki isa ki cinyeni ba" sai ta kauda kai ta wuce kai tsaye dakinta ta bude ta shige.
Bata sake fitowa yayi zamanta cikin dakin,sai ta qirqiro wasu 'yan qananun ayyaukan ma cikin dakin nata don kawar da duk wani tunani da zai dameta,tana aikin tana ambatar hasbunallahu wa ni'imal wakil,allahumk finihim bima shi'ita,hakan ba qaramin taimaka mata yayi ba,sai ya tafiyar da lokacinta cikin sauqi har aka kira sallar magariba,ta miqe ta fito domin daura alwala,suna zaune gefe daya na tsakar gidan da qullin kayansu,sosai har cikin zuciyarta taji babu dadi,bai kamata mukhyar yazo ya taras da su haka ba,ko babu komai 'yan uwansa ne jininsa ne,kuma tayi imami cewa idan wani nata ne shima mukhtar din ba zaya wofantar da su haka ba,ta danne zuciyarta ta qarasa gurinsu,cikim sanyin murya tace
"Don Allah yaya ki shigi dakina,ko da ba zaki zauna din ba ki shigo idan yaso idan ya mukhtar din ya dawo sai asan yadda za'ayi din" wani kallon banza ta bita da shi
"Ke wallahi ki fita a idona,wai ke wacce iriyar mayatacciya ce ne,nace bazan shiga ba dole ne,to bari kiji,idan ma wani laqani aka baki na sai na shiga sannan zaki samu galaba a kaina to wallahi ki gayawa malaminki kunyi qarya kun kwana da yunwa" jikinta sai yayi sanyi ta kasa tafiya,zuciyarta na gaya mata basu zama masu kyautawa mukhtar ba indai yazo ya tadda jininsa a wulaqance,duk da tarin izgilu cin fuska da cin mutunci da ita yaya yahanasun ke jifanta da shi,ba ita take dubawa karamcin mukhtar take dubawa.
A haka mukhtar din ya shigo ya riskesu,tayi masa sannu da zuwa ta karbar kayan hannunsa duk da ba ranar girkinta bane,ya amsa yana duban yaya yahanasu."a'ah,yaya yanzu kuka zone na ganku a nan a zaune ku da kayanku"kai ta girgiza
"Inaaa,ai tun azahar muna gidan nan" cikin mamaki ya dubeta tare da zaro ido sai ya dubi sumayya yana jifanta da tuhuma,qas tayi da kanta don bata da ta cewa,ganin haka yasa ya dubi yaya yahanasun
"Amma kuke zaune a nan?,kada kice min nan kuka wuni?" Waiwayawa tayi ta dubi sumayya
"Sai ki bamu guri ko ko ban isa ba?" Bata ce uffan ba ta koma dakinta duk da alwala ta fito da niyyar daurawa.
Sai da taga shigarta dakin sannan ta maido dubanta ga fa'iza
"Mutuniyar tamu,wallhi lafiya lau ta karbemu,daga yi mata tambaya kan naji shiru har yanzu mun samu qaruwa ko a'ah ta shiga masifa ta inda take shiga ba ta nan take fita ba,qarshe tayo mana waje da kayanmu" sosai ransa ya baci,ya soma huci cikin fushi yace
"Fa'izar?,to da tayi muku haka gidanta ne ko nawa?,bazan lamunci wannan iskanci ba" ya fada yana juyawa zuwa ga dakinta wanda fa'izar na ciki tana jin kowa tayi lakur abinta.
Da sauri yaya yahanasun ta dakatar da shi
"Kaga muntari bana son hauka fa,laifi muka yi mata mu mika bata mata rai,nasan kuma zata huce,don haka bance kaje ka sake bata mata rai ba,kadai lallabata har ta yarda mu zauna taren" jagale yayi tare da juyiwa yana duban yayar tasa,take kuma ya tuna sunfi kusa fa ita da fa'izan,ya ma kamata a yau din ya qyaleta taga halin fa'izan taga wace ita ra'ayil ain wato ganin ido,saboda haka sai ya saki murmushi cikin salon canza shawarar da yayi farat daya,gyada kai yayi
"Shikenan,muje to a lallabatan" da sauri suka miqe yaya yahanasun tana cewa
"To,to ai kaga hakan yafi" tabi bayansa.
Tana miqe daga kan gadonta tana taunar chewing gum dai dai,zama sukayi kan kujerarta dake fuskantar gadon,yayin da mukhtar ya qarasa gefan gadon ya tsaya,duk da cewa ransa a matuqar bace yake,ji yake kamar ya janyo fa'izan ya yi mata dan banzan duka ya watsar amma sai ya dake
"Fa'iza,me yasa ba zaki bar yaya ta zauna dakinki ba,ai ina ganin bai kamata ba" hura hanci take tana tunanin ko yanzu mukhtar ya soma tsoronta,inko haka ne kowa tasa ta qare,tabbas sai kowa ma yaci ubansa cikin gidan
"Mukhtar banga dama bane,bari kaji" ta fada tana miqewa zaune kan gadon
"Na farko bansan sa ido gaskiya kuma na fuskanci su sun fara koyar wannan halayyar,na biyu na fuskanci ni aka rainawa wayo,ga mai daki ciki da falo can ba'a dosheta ba saini mai daki daya kamar zuciyar talaka" ba qaramin dukansa maganar tayi a zuciya ba amma ya hadiye don so yake ya jata aje gun ta dora da
"Saboda haka su nemi gurin kwana don ni bazan zauna da wadan nan qattan a daki na ba" wani qullutun abu ne ya tokare masa wuya qanda ya hanashi sake magana,sai yaya yahanasu da tace
"Haba ke kuwa fa'iza,kwana nawa ne duka duka mun koma gidanmu,ai ban zaci ko wani na turo gidan nan ki masa sauki a dakinki ba zaki kasa,kada fa ki manta nice silar zuwanki gidan nan" zabura tayi tana dakatar da ita
"Kinga kada ki sake kice zaki mun gori,don ke kika kawoni gidan ai bake kike aure na ba,buqatar maje haji sallah kuma da taku buqatar ai ba haka siddan kika kawoni ba,sabida haka kuje ni don Allah kada ku cikan kunne,tunda kun nace sai kun zauna a dakin kuje zanyi tunani,ko kwana daya ne kuyi kafin ku koma inda kuka fito".
Ba qaramin daurewa kan yaya yahanasun yayi ba da kalaman fa'iza,duk yadda fadima ke gaya mata sai yau ta sake tabbatarwa da lamba daya ce ita wajen rashin mutunci tsiya da tsiyataku
" fa'iza ni kike gayawa haka"kanga tsaye babu kunya tace
"Na fada din,ke kike aurena ne nace wai kawai da zaki takuran,wannan fa kamar kina lissafin sau nawa nake kwanciya da mijina ne"tuni maganar ta sake dora yaya yahanasun kan dokin zuciya
" ke qaramar mara kunya,ko bani nake aurenki ba kinsan ina da power din da zan sa ungulu ta koma gidanta na tsamiya ko?"
"Bismillah,sai mu gani " ta fada tana murguda baki gami da turo daurinta gaban goshinta ta dage kanta idanunta na kallon ceiling din daki.
tabbas tana jin yau idan bata nunawa fa'iza isar da take da ita a wajen mukhtar ba bata huce takaici ba,idanunta taf da bacin rai ta dubeshi
"Mukhtar,ina so a yau yau din nan ka sawwaqewa fa'iza,yanzun nan" ta qarashe cikin daga murya.
Duk da cewa ranshi ya kai qololuwa wajen baci kan abinda fa'izq ta yiwa yaya yahanasun amma sai ya danne komai tamkar bai b'aci ba,ai dama duk wanda ya sai rariya yasan zata zub da ruwa,to ya kamata yaya yahanasun taga yadda tata rariyar ke zubar da nata ruwan,ruwan kuma da baiyi qasa a gwiwar malalowa ya jiqata sharkaf ba,kai ya kada sannan yace
"Kan me zan saki fa'iza yaya,ni babu abinda ta yimin,hasalima fa'iza ai zabinki ce,kinga bai kamaci na wofantar da ita ba,zan riqeta hannu bibbiyu kamar yadda kika umarceni" tsawa ta daka masa
"Mukhtar,kai makaho ne?,ko kuwa kai kurma ne,baka ganin abinda ta yimin ne,ni na umarceka nace ka saketa kamar yadda na umarceka ka aureta a baya" kai ya sake kadawa tare da yin tattaki don barin dakin yana cewa
"Ki gafarceni yaya,amma yanzu na fara zama da fa'iza,don ni bata aikata min komai ba" sai ya fice abinsa ya barsu ana kallon kallo.