Sashe 121
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shuru amira tayi wanda hakan ke gwada baki daya bata ji dadi ba,jikinta a sanyaye taci gaba da cin abincin,sai da daqiqa kusan biyar ta shude sannan ta iya cewa
"Malam yafi gaban komai amira,sai kin dawo Allah ya kiyaye,amma don Allah ki dawo da wuri,sannan kimin alqawari zaki shiga ayi komai da ke,zaki dauki kanki kamar diyar baabaa,wallahu tun wancan satin baabaa ke tsokanata,wai idan baki dawo ba baisan ya zanyi ba,qila saidai ya daga bikin ko?" Murmushi tayi,alqawarin yayi mata girma da yawa,amma tilas ta dauka,anayi da kai yafi ba'a yi da kai,masoyinka kuma yafi maqiyinka
"Kada ki damu,nayi alqawari in sha Allah"
"Amma kafin ki wuce zaki shigo ki gaida su ummee,daga nan kiga ankon da aka fitar ko,ku hudu amma kalar naku daban,ke da qawaye na su uku"
"Me zai hana,in sha Allah" ta fada kawai din a wuce gun,amma mai zai kaita gidan a irin wannan lokacin da wannan mutumin ke qasar,daga haka ta ware suka ci gaba da hirarsu.
******** ******** ********
Tun dare ta kasa bacci,gani take kamar gari bazai waye ba,bata ji kwanciyar hankali ba sai data ganta a mota sun dauki hanya,babu wanda ta gayawa tana zuwa don so take tayi masu ba zata.
Qarfe daya da minti ashirin na azahar a qofar gida tayi musu kasancewar sun fito ne da wuri,ita ta fara shiga kafin driver din su anty dijen ya soma shiga mata da akwatunta da qatuwar jakar dake dauke da kayan tsaraba.
Halima ce a kitchen,mama na bakin fanfo tana daura alwalar sallar azahar,yayin da zainab ke mopping falon mama wanda ta dage labulensa,hakimin abdallah na kwance abinsa saman kujera yana kallon cartoon,zainab na mopping din tana mitar ya hanasu kallon kowacce tasha sai ta 'yan aljanu,mama na fadin ai yafi,sunfi son suyita kallon waqe waqe da raye rayen banzan nan da wofi.
Tana sallamar halima ta saki kwashe miyar da takeyi ta fito,zainab ta saki mopper,yayin da mama tayi tsaye tana dubanta tare da amsa mata sallamar fuskarta dauke da madaukakin murmushi,kusan a tare suja ruqunqumeta suna ambatar sunanta,dadi ya cika kowannansu,sam abdallah bai fahimci me ake ba sai da suka shigo falon,dirowa yayi daga kan kujerar yayi kan sumayya yana kiran
"Mamiiiiiiii naaaaaaa" baki daya ya cukuikuyeta kamar zai shige jikinta,itama tsam ta rungumeshi tana dariya farinciki fal zuciyarta kamar an wanketa da ruwan qanqara.
Baki daya sun baibayeta,idanuwanta na kam abdallah,photocopy na mukhtar take kalla,cikin shekara guda tal ya sake wani girma da wayo na ban mamaki,ya fara zama dan saurayi,shekara kusan biyar ba wasa bace,girman dan mutum babu wuya,duba daya ya wadatar da kai ka gane yaron na samun gata da kulawa,don suturar jikinsa ma kadai amsa ce,zainab da halima kowa da abinda zai fadi
"Yaya sumayya kin ganki kuwa?,kamar irin hajiyoyin nan"
"Yaya sumayya kin zama budurwa wallahi,irin 'yammatan abujan nan,gaskiya tafiyan nan ta karbeki,kaman an canjoki baki daya" dariya take ta rasa abin cewa,tunda ta sauko daga mota ta lura da kallon da jama'ar unguwar tasu ke mata wasu ma kamar basu ganeta ba,haka su halina suka cikata da surutu har sai da mama ta korasu halima taje ta zubo abinci ta kaima driver a waje din da yayi salla zai koma,sannan ta zubowa sumayyan ma, zainab kuma ta kai mata kayan daki,sai bayan fitarsu sannan suka ji kunnuwansu,abdallah na maqale jikinta yana ta bare choculets yana gama musu aiki.
Haka suka wuni ba wanda ya fita a gidan,sai maqota dake shigowa jifa jifa yi mata sannu da zuwa,wanda wasunsu labarin yadda sumayyar ta koma suka ji suka zo ganewa idanuwansu.
Koda ya abbakar yazo shima baki ya saki
"Lallai nasan gobe mutuniyar anan zata wuni"
"Ni ya kamata naje yaya,ina babymu nasan ta fara wayi bata san mamarta ba(da yake matarsa ta haihu)"
"Ke dai kawai sai kin ganta,na tabbata ba zata iya haquri har kizo ba", malam ne kawai bai shigo da wuri ba amma ta gaza bacci sai da taga shigowarshi,kusan raba dare sukayi suna hira da shi,zuciyarsa na masa dadi duk sanda ya kalli diyar tashi,babu shakka rayuwa ta soma yi mata kyau,saidai a yanzun yana ganin ya kamata ta fidda abokin rayuwa ta sake aure,ko bai mata maganar yanzu ba zai fara yi mata jirwaye mai kama da wanka,zai tashi haiqan wajen yi mata addu'ar katari da miji na gari ita da 'yan uwanga baki daya,sai wajen sha biyu da rabi na dare suka rabu taje ta kwanta.
******** ******** *******
Washe gari a dakin malam din ta karya,ko wanka bata yi ba kayan bacci ne jikinta rida da dogon wando masu kauri,ta dora dogon hijabinta mai hannu,bayan sun kammala suka ci gaba da taba hirarsu,gayaran murya malam din yayi
"tunda gaki Allah ya dawo dake auren 'yar uwarki ina jin ba zai wuce wata biyu ba,dama su suka matsa da magiyar a bari ki dawo,basa son ayu bikin wai bakyanan,shima kuma abubakar ya goyi bayansu" murmushi tayi ta dan sadda kai a zuciyarta tana lissafin bayan bikin amira da sati hudu kenan?
"Alhamdulillahi,Allah ya tabbatar mana da alkhairi"
"Amin ya Allahu,gwara ayi,hankalina sai yafi kwanciya,burina naga kowacce dakin mijinta,shine cikakken mutuncin 'ya mace,duk inda kika kai ga isa da dukiya nasaba da ilimi matuqar baki da aure baki kammala zama cikakkiya ba,don shine rabin,sai muyita addu'a,shi dama ibada ne,idan ka dace ka godewa Allah,idan ya jarabceka kayi haquri ka kuma nemi lada a wajensa"
"Haka ne malam,Allah ya tabbatar da dukkan alkhairi" kai ta sunkuyar,jikinta yayi sanyi,ba shakka ta fuskanci zaurencan malam,gugar zana yake mata,ita kam ina zata tsomala rayuwarta a yanzu idan malam ya taso mata da batun aure,da sauri ta nemi tsari kada Allah ya karkato da hankalinsa.
Cikin siyasa da qwarewa ta cikim hirar da suke yake jan hankalinta dangane da halayen rayuwa,babu shakka dukkan maganarsa izina ce kuma abar dauka,sosai taji dadin hirar da shi saboda yadda yayi mata tuni sosai game da wasu lamura masu matuqar muhimmanci ga rayuwar diya mace,ranar malam bashi ya fita ba sai sha biyu na rana,tun mama na leqosu taga ko ya gama shirin fitar har ta gaji ta barsu.
Sanda ta fito zuwa falon mama ashe anty amina matar yaya abubakar har tazo,dariya ta saki tana dubanta
"Tab,wlh anty kwata kwata banji shigowarki"
"Ina zakiji 'yar gaban goshin malam" zainab tayi caraf ta karbe
"Wallahi anty kema kya fada,baki daya faadar malam tata ce" karyar da wuya amina tayi
"Dole malam yaji da sumayya don gaskiya ba daya kuke ba,kun manta yadda rayuwa tayi da ita ne,QADDARA ta wajiga ta?"
"gaya musu dau matar yaya" ta fada tana amsar babyn fuskarta qunshe da fara'a tana cewa
"Ga babbar jika,ga babbar jika a mata" yarinyar kuwa dariya ta dinga bangalawa kamar ta gane wace sumayyan a wajenta,yarinyar kyakkyawa sosai ta biyo jinin gidansu sumayya.
Amina ke ta bin sumayya da kallo har sai data tanka
"Wai sumayya me anty dije ke baki haka,kinga yadda kika koma kuwa?" Dariya ta saki
"Haka kowa ke fada anty"
"Wallahi kin sauya baki daya masha Allah,boyayyen kyawun nan duk ya fito,yau dai na yarda kinfi abban yusra kyau" dariya ta tuntsire da ita,sabida sau da dama suna musu kan hakan amma taqi yarda,sai gashi yau ta sallama.
******* ****** ******
Washe gari qarfe sha biyu na rana ta shirya tsaf cikin african abaya,abaya ce me mix da atamfa wadda tasha kwalliyar duwatsu,tayi kyau qwarai,jaka da takalminta duka marching colour,gidan hajiya tayi niyyar zuwa yau,hajiyan abdur rahman,so take ta wanke kanta,don tasan sam bata kyauta ba,shiru kawai wancan karon abdur rahman yayi mata.
Ita da halima zasu je,saboda zainab ita yau ke da girki,suka yiwa mama sallama suka fice bayan tace su gaida mata hajiyan da bahijja,don shima abdur rahman din kwana biyu kenan bai leqo ba,abinda idan yana gari bai taba tsallake kwanaki biyun bai leqo ba,ba wani tazara ce mai yawa tsakaninsu ba,hakan ya sanya cikin mintuna arba'in mai adaidaita sahu ya saukesu bakim get din gidan suka sallameshi suka nufi gidan.
Tun kafin su shiga abdallah ya soma fadin
"Zamu gun daddy A ko?,gun hajiya da bahijja" kallon mamaki sumayya ke masa kafin ta maida dubanta ga halima
"Kai,wai yaron nan har gidansu abdur rahman ya sani?" Murmushi halima tayi
"Me zai hana,yaron dake wuni a gidan" shuru kawai tayi tana kada kai har suka shiga gidan.
Daga can bakim setting room ta hangi takalma,wanda hakan ke alamta masu gidan na da baqi maza,babu kowa falon sai bahijja dake kwance kan doguwar kujera,sallamarsu ita ta sanyata miqewa zaune,fuskarta taf da fara'a takewa sumayya sannu da zuwa gami da miqewa tsaye saboda murna da mamakin ganin sumayyan,ana haka hajiyan ta fito daga dakin da yake mallakin bahijja hannunta dauke da magunguna,lale marhabin ta shiga yiwa su sumayya suna gaisawa da halima,yayin data ja abdallah jikinta tana fadin
"Matso mai gida na,kwana biyu ban ganka ba,daddynka ya shiga rububi bude asibiti ya hanashi sukuni,hala ma kun ganshi?,don yana sitting room tare da baqi" murmushi sumayyan tayi a aladabce
"Bamu ganshi ba,amma kamar akwai mutane a wajen"
"Masha Allah,mutanen uk,tafiya ba sallama" ta fada cikin zolaya,sai kunya ta kamata ta sadda kai
"Wallahi hajiya,shirin tafiyar duk shi ya cinye lokacin amma naso zuwa"
"Babu komai,ai komai sai Allah ya nufa,kun dawo lafiya yasu dijen,kina wajenta ko?" Kai ta kada tana fadin
"Eh,lafiya qalau suna gaisheku"
"To madalla muna amsawa,bahijja miqe ki sama musu wani abu a kitchen kafin a gama abinci"
"Halan bata da lafiya ne hajiya?" Sumayya ta tambaya tana duban bahijja
"Bata jin dadi,kuma saboda wani iya shege bata da lafiya amma taqi shan magani,ta ina lafiya zata samu"
"Gaskiya kam" sumayya ta fada,ita da halima suka shiga,haka suka fito da snacks ruwa da lemo,yayin da hajiya ta ajjiye maganin ta basu wuri tana dauke da abdallah ko nauyinshi bata ji,yaron itama yana tuna mata mukhtar,akwai tsantsar kama mai yawa tattare da su.
"Malam yafi gaban komai amira,sai kin dawo Allah ya kiyaye,amma don Allah ki dawo da wuri,sannan kimin alqawari zaki shiga ayi komai da ke,zaki dauki kanki kamar diyar baabaa,wallahu tun wancan satin baabaa ke tsokanata,wai idan baki dawo ba baisan ya zanyi ba,qila saidai ya daga bikin ko?" Murmushi tayi,alqawarin yayi mata girma da yawa,amma tilas ta dauka,anayi da kai yafi ba'a yi da kai,masoyinka kuma yafi maqiyinka
"Kada ki damu,nayi alqawari in sha Allah"
"Amma kafin ki wuce zaki shigo ki gaida su ummee,daga nan kiga ankon da aka fitar ko,ku hudu amma kalar naku daban,ke da qawaye na su uku"
"Me zai hana,in sha Allah" ta fada kawai din a wuce gun,amma mai zai kaita gidan a irin wannan lokacin da wannan mutumin ke qasar,daga haka ta ware suka ci gaba da hirarsu.
******** ******** ********
Tun dare ta kasa bacci,gani take kamar gari bazai waye ba,bata ji kwanciyar hankali ba sai data ganta a mota sun dauki hanya,babu wanda ta gayawa tana zuwa don so take tayi masu ba zata.
Qarfe daya da minti ashirin na azahar a qofar gida tayi musu kasancewar sun fito ne da wuri,ita ta fara shiga kafin driver din su anty dijen ya soma shiga mata da akwatunta da qatuwar jakar dake dauke da kayan tsaraba.
Halima ce a kitchen,mama na bakin fanfo tana daura alwalar sallar azahar,yayin da zainab ke mopping falon mama wanda ta dage labulensa,hakimin abdallah na kwance abinsa saman kujera yana kallon cartoon,zainab na mopping din tana mitar ya hanasu kallon kowacce tasha sai ta 'yan aljanu,mama na fadin ai yafi,sunfi son suyita kallon waqe waqe da raye rayen banzan nan da wofi.
Tana sallamar halima ta saki kwashe miyar da takeyi ta fito,zainab ta saki mopper,yayin da mama tayi tsaye tana dubanta tare da amsa mata sallamar fuskarta dauke da madaukakin murmushi,kusan a tare suja ruqunqumeta suna ambatar sunanta,dadi ya cika kowannansu,sam abdallah bai fahimci me ake ba sai da suka shigo falon,dirowa yayi daga kan kujerar yayi kan sumayya yana kiran
"Mamiiiiiiii naaaaaaa" baki daya ya cukuikuyeta kamar zai shige jikinta,itama tsam ta rungumeshi tana dariya farinciki fal zuciyarta kamar an wanketa da ruwan qanqara.
Baki daya sun baibayeta,idanuwanta na kam abdallah,photocopy na mukhtar take kalla,cikin shekara guda tal ya sake wani girma da wayo na ban mamaki,ya fara zama dan saurayi,shekara kusan biyar ba wasa bace,girman dan mutum babu wuya,duba daya ya wadatar da kai ka gane yaron na samun gata da kulawa,don suturar jikinsa ma kadai amsa ce,zainab da halima kowa da abinda zai fadi
"Yaya sumayya kin ganki kuwa?,kamar irin hajiyoyin nan"
"Yaya sumayya kin zama budurwa wallahi,irin 'yammatan abujan nan,gaskiya tafiyan nan ta karbeki,kaman an canjoki baki daya" dariya take ta rasa abin cewa,tunda ta sauko daga mota ta lura da kallon da jama'ar unguwar tasu ke mata wasu ma kamar basu ganeta ba,haka su halina suka cikata da surutu har sai da mama ta korasu halima taje ta zubo abinci ta kaima driver a waje din da yayi salla zai koma,sannan ta zubowa sumayyan ma, zainab kuma ta kai mata kayan daki,sai bayan fitarsu sannan suka ji kunnuwansu,abdallah na maqale jikinta yana ta bare choculets yana gama musu aiki.
Haka suka wuni ba wanda ya fita a gidan,sai maqota dake shigowa jifa jifa yi mata sannu da zuwa,wanda wasunsu labarin yadda sumayyar ta koma suka ji suka zo ganewa idanuwansu.
Koda ya abbakar yazo shima baki ya saki
"Lallai nasan gobe mutuniyar anan zata wuni"
"Ni ya kamata naje yaya,ina babymu nasan ta fara wayi bata san mamarta ba(da yake matarsa ta haihu)"
"Ke dai kawai sai kin ganta,na tabbata ba zata iya haquri har kizo ba", malam ne kawai bai shigo da wuri ba amma ta gaza bacci sai da taga shigowarshi,kusan raba dare sukayi suna hira da shi,zuciyarsa na masa dadi duk sanda ya kalli diyar tashi,babu shakka rayuwa ta soma yi mata kyau,saidai a yanzun yana ganin ya kamata ta fidda abokin rayuwa ta sake aure,ko bai mata maganar yanzu ba zai fara yi mata jirwaye mai kama da wanka,zai tashi haiqan wajen yi mata addu'ar katari da miji na gari ita da 'yan uwanga baki daya,sai wajen sha biyu da rabi na dare suka rabu taje ta kwanta.
******** ******** *******
Washe gari a dakin malam din ta karya,ko wanka bata yi ba kayan bacci ne jikinta rida da dogon wando masu kauri,ta dora dogon hijabinta mai hannu,bayan sun kammala suka ci gaba da taba hirarsu,gayaran murya malam din yayi
"tunda gaki Allah ya dawo dake auren 'yar uwarki ina jin ba zai wuce wata biyu ba,dama su suka matsa da magiyar a bari ki dawo,basa son ayu bikin wai bakyanan,shima kuma abubakar ya goyi bayansu" murmushi tayi ta dan sadda kai a zuciyarta tana lissafin bayan bikin amira da sati hudu kenan?
"Alhamdulillahi,Allah ya tabbatar mana da alkhairi"
"Amin ya Allahu,gwara ayi,hankalina sai yafi kwanciya,burina naga kowacce dakin mijinta,shine cikakken mutuncin 'ya mace,duk inda kika kai ga isa da dukiya nasaba da ilimi matuqar baki da aure baki kammala zama cikakkiya ba,don shine rabin,sai muyita addu'a,shi dama ibada ne,idan ka dace ka godewa Allah,idan ya jarabceka kayi haquri ka kuma nemi lada a wajensa"
"Haka ne malam,Allah ya tabbatar da dukkan alkhairi" kai ta sunkuyar,jikinta yayi sanyi,ba shakka ta fuskanci zaurencan malam,gugar zana yake mata,ita kam ina zata tsomala rayuwarta a yanzu idan malam ya taso mata da batun aure,da sauri ta nemi tsari kada Allah ya karkato da hankalinsa.
Cikin siyasa da qwarewa ta cikim hirar da suke yake jan hankalinta dangane da halayen rayuwa,babu shakka dukkan maganarsa izina ce kuma abar dauka,sosai taji dadin hirar da shi saboda yadda yayi mata tuni sosai game da wasu lamura masu matuqar muhimmanci ga rayuwar diya mace,ranar malam bashi ya fita ba sai sha biyu na rana,tun mama na leqosu taga ko ya gama shirin fitar har ta gaji ta barsu.
Sanda ta fito zuwa falon mama ashe anty amina matar yaya abubakar har tazo,dariya ta saki tana dubanta
"Tab,wlh anty kwata kwata banji shigowarki"
"Ina zakiji 'yar gaban goshin malam" zainab tayi caraf ta karbe
"Wallahi anty kema kya fada,baki daya faadar malam tata ce" karyar da wuya amina tayi
"Dole malam yaji da sumayya don gaskiya ba daya kuke ba,kun manta yadda rayuwa tayi da ita ne,QADDARA ta wajiga ta?"
"gaya musu dau matar yaya" ta fada tana amsar babyn fuskarta qunshe da fara'a tana cewa
"Ga babbar jika,ga babbar jika a mata" yarinyar kuwa dariya ta dinga bangalawa kamar ta gane wace sumayyan a wajenta,yarinyar kyakkyawa sosai ta biyo jinin gidansu sumayya.
Amina ke ta bin sumayya da kallo har sai data tanka
"Wai sumayya me anty dije ke baki haka,kinga yadda kika koma kuwa?" Dariya ta saki
"Haka kowa ke fada anty"
"Wallahi kin sauya baki daya masha Allah,boyayyen kyawun nan duk ya fito,yau dai na yarda kinfi abban yusra kyau" dariya ta tuntsire da ita,sabida sau da dama suna musu kan hakan amma taqi yarda,sai gashi yau ta sallama.
******* ****** ******
Washe gari qarfe sha biyu na rana ta shirya tsaf cikin african abaya,abaya ce me mix da atamfa wadda tasha kwalliyar duwatsu,tayi kyau qwarai,jaka da takalminta duka marching colour,gidan hajiya tayi niyyar zuwa yau,hajiyan abdur rahman,so take ta wanke kanta,don tasan sam bata kyauta ba,shiru kawai wancan karon abdur rahman yayi mata.
Ita da halima zasu je,saboda zainab ita yau ke da girki,suka yiwa mama sallama suka fice bayan tace su gaida mata hajiyan da bahijja,don shima abdur rahman din kwana biyu kenan bai leqo ba,abinda idan yana gari bai taba tsallake kwanaki biyun bai leqo ba,ba wani tazara ce mai yawa tsakaninsu ba,hakan ya sanya cikin mintuna arba'in mai adaidaita sahu ya saukesu bakim get din gidan suka sallameshi suka nufi gidan.
Tun kafin su shiga abdallah ya soma fadin
"Zamu gun daddy A ko?,gun hajiya da bahijja" kallon mamaki sumayya ke masa kafin ta maida dubanta ga halima
"Kai,wai yaron nan har gidansu abdur rahman ya sani?" Murmushi halima tayi
"Me zai hana,yaron dake wuni a gidan" shuru kawai tayi tana kada kai har suka shiga gidan.
Daga can bakim setting room ta hangi takalma,wanda hakan ke alamta masu gidan na da baqi maza,babu kowa falon sai bahijja dake kwance kan doguwar kujera,sallamarsu ita ta sanyata miqewa zaune,fuskarta taf da fara'a takewa sumayya sannu da zuwa gami da miqewa tsaye saboda murna da mamakin ganin sumayyan,ana haka hajiyan ta fito daga dakin da yake mallakin bahijja hannunta dauke da magunguna,lale marhabin ta shiga yiwa su sumayya suna gaisawa da halima,yayin data ja abdallah jikinta tana fadin
"Matso mai gida na,kwana biyu ban ganka ba,daddynka ya shiga rububi bude asibiti ya hanashi sukuni,hala ma kun ganshi?,don yana sitting room tare da baqi" murmushi sumayyan tayi a aladabce
"Bamu ganshi ba,amma kamar akwai mutane a wajen"
"Masha Allah,mutanen uk,tafiya ba sallama" ta fada cikin zolaya,sai kunya ta kamata ta sadda kai
"Wallahi hajiya,shirin tafiyar duk shi ya cinye lokacin amma naso zuwa"
"Babu komai,ai komai sai Allah ya nufa,kun dawo lafiya yasu dijen,kina wajenta ko?" Kai ta kada tana fadin
"Eh,lafiya qalau suna gaisheku"
"To madalla muna amsawa,bahijja miqe ki sama musu wani abu a kitchen kafin a gama abinci"
"Halan bata da lafiya ne hajiya?" Sumayya ta tambaya tana duban bahijja
"Bata jin dadi,kuma saboda wani iya shege bata da lafiya amma taqi shan magani,ta ina lafiya zata samu"
"Gaskiya kam" sumayya ta fada,ita da halima suka shiga,haka suka fito da snacks ruwa da lemo,yayin da hajiya ta ajjiye maganin ta basu wuri tana dauke da abdallah ko nauyinshi bata ji,yaron itama yana tuna mata mukhtar,akwai tsantsar kama mai yawa tattare da su.