← Book details Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 225 OF 226

Sashe 225

Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

       Bayan amira wadda kwana zatayi ra saka duka yaran mata sunyi wanka sai ta fice zata wajen ummi ta bawa qaramin yaronta nono,wanda yaranta biyu,babbar itace farha sai qaramin hadim,sumayya ta bari da su tana tsakiyarsu tana fama da su kan kowanne ya nutsu,mai cin abinci yaci mai kwanciya ya kwanta,wahalar da ita suke sosai don amatur rahman ta hada gang sunata tayi,miqewa tsaye tayi kawai tana kallonsu
"Wannan yarinya halan fitinar amira ta dauko ne?" Ta raya haka cikin zuciyarta,qaramar dariya taji an saki a bayanta,hakan ya sanyata waiwayowa a hankali,almustapha ne tsaye ya jingina da qofa,hannayenshi harde a qirjinsa yana murmushi da alama ita yakewa dariya,sauke hannyen nashi yayi ya fitota da hannu,don tabbas idan ya sake ya shigo cikin dakin yaran ba zasu barshi ya fita da wuri ba,ta gane sarai me yake nufi,sau ta dubi jikinta,don tunda aka tashi daga wajen batayi wanka ba,abinda take ta sauri tayi kenan kada yazo ya sameta a hakan,sai gashi bata cimma nasara ba,kafadarshi ya dage hadi da girarahi ya watsa hannayenshi yana murmushi alamun babu ruwanshi,ta nuna kanta da yatsa alamar niko?,ya kada mata kai yana nufin eh din,sai kawai ta juya ta dubi su amatallah tace
"Amatu.....ga abul_aulad" take kowa hankalinsa yayo kan qofar,kafin kace meye sun moqe aun dunguma kanshi,wayyo sumayyan ta gama masa tsiya,yau yasan ciwon kai babu fashi,idan ba'ayi da gaske ba ma duk yadda ya ciwa yau din buri bazai iya aikata komai ba,tana masa dariyan mugunta ta zame ta barshi da su,hakan ya bata damar yin wanka ta shirya tsaf,sannan a gurguje ta shirya masa abinda zaici sannan ta dawo wajensu.

       Daga bayansu ta tsaya tana kallonsu tana sakin murmushi a jejjere,babu shakka haihuwa rahama ce,yara ni'imah ce,koda shashancinsu kawai wani lokaci abun debewa zukata kewa ne,almustaphan da baison hayaniya ko kwaramniya ko qanqani yau sai gashi tsakiyar yara,ya bude musu kwalin chaculets wasu na cin gugguru(popcorn),wasu na fama da ice cream,baki daya sun bata mishi jiki,amma ba yadda ya iya haka yake biye musu,sai data gaji da kallonsu don kanta taga sun fara cakar da shi ya soma riqe kai sannan ta qarasa wajen tana masa dariya,ya daga kai suka hada ido,maimakon harar nuna ta masa laifi fa yayi niyya sai gashi ya buge da zuba mata idanu yana kallonta kaman zai cinyeta,sai data kada hannunta saitin fuskarshi,ta zauna gefan madina 'yar gidan abida ta biyu ta janyi guggurun ta soma ci,gardin madara dana zumar dake ciki na ratsata harda lumshe ido
"Madam,u r pregnant fa?kinsan yaushe nayi shi?,randa zamu baro dubai,unforgotable night din nan da kika bani"ya rada mata saitin kunnenta sanda yadda ba wanda zaiji sai su Cak ta tsaya da taunar ta waiwayo tana dubanshi,tasan tunda ya fada din mawuyacine idan ba hakan bane,saboda ba yau ya fara ba kamar wani mai gani har hanji,duk sanda yaui cikinsa shike gaya mata kuma daga qarshe ya tabbata hakanne,haka sukayi cikin qarami da cikin amir,tana son nuna alhinin dake cikin zuciyarta amma tasan sharadin yin hakan bata manta ba,yace duk sanda ta sake nuna bata son cikinsa ta tabbatar da cewa ta bashi license na qara aure ne,har yau diyar ambassador na nijer na nan,duk da an kusa bikinta idan yace yana so babu abinda zai hanasu bashi
"amma likita don Allah?"
"Na auro saliha?" Kada kai tayi da sauri
"Amir fa,shekararsa daya da rabi yanzu fa"
"Sanda kika haifi aboki shekarar su amatu daya da wata hudu,me ya sameki?" Kai ta kada
"Ba komai"
"Kada fa ki yiwa Allah butulci,kin manta sunan da ake kiranki a baya"
"Asragfurullah" ta ambata da sauri,har yau bata mance rigimar cikin qarami ba,anty ni'imah cewa tayi tana so a bata ita,tun a sannan jikinta ya sake sanyi,sai yanzu zata sake gwadawa abinka da dam adam kayan Allah
"Taimakeni ki sallami yarankin nan don Allah nima aji da ni" ya fada yana langabe kai gwanin tausayi kaman gaske,bushewa tayi da dariya don ya bata dariya,cikin wayo da dabara ta dinga kaisu daki suna kwanciya har da amir kuwa duk da dafarsa,amatur rahman kawai ta rage,ta kafe kai da fata sai an fara bude gifts da suka samu a daren,tun tana daurewa har ta bata haushi ta kai mata duka,tako sameta cinya da daku sosai,kuka ta saki ta soma sosa wajen yayin da sumayyan ta rufeta da hargowa kaman zata sake kai mata wani dukan,kallonta kawai almustaphan yayi sai ya dauke kai,ya janyo amatur rahman din ya yaye rigar jikinta,abinka da farar fata wajen kuwa yayi jazur sosai,shafa mata wajen ya aoma yi yana hura mata cikin salon nusarwa yace
"Ba'a yiwa mama musu da taurin kai,haba amatu...ke da kike babba....baku ganu su ikram da su affan duka kin girme musu kuma sun tagi sun kwanta,baki son mama ta huta ne itama?" Kai ta gyada alamar tana so a sanyaye
"tun jiya mama bata zauna ba uhm,ki bata haquri kuce ba zaki daina ba" a sanyaye ta dubi sumayya da tayi kicin kicin da rai,ranta na wanu irin baci,wanda abinda tayi mata baikai bacin ran da take ji ba,don idan da sabo da tasa ba da halin amatur rahman
"Ammi....kiyi haquri" da yake suna kiranta da sunan da abdallah ke kiranta ne,saboda duk hutu anan yake zuwa yayi,akwai sabo da shaquwa sosai tsakaninsu tamkar uwa daya uba daya,su kansun a yanzun sun dauka babansu shi ya haifeshi,an ce musu shine babbansu yana kano ne yana karatu sai ya gama zai dawo,qin amsa mata tayi sai data maimaita sannan tace
"Naji....tashi kije ki kwanta" miqewa tayi har ta soma takawa tace
"Ammi....amma yaya abdallah da yace zai kiramu bai kira ba fa"
"Ban gaya miki jarabawa yake ba baya waya sai ya gama?!" Ta fada mata a tsawace,sai ta juya sum sum ra fice zuwa dakin,yayin da almustapha ya zuba mata ido,sai da yarinyar ta fice sannan ta ja tsaki suka hada ido da shi,dauke kai yayi ya miqe ya wuce nashi bedroom din,sannan ta miqe ta bishi a baya.

       Sanda ta shiga har ya shiga wankanshi,qwafa tayi ganin ya hada ruwan wankan da kanshi kenan,abinda ya kasance aikinta ne ita keyi,hakan ya sanya ta zauna tana hade rau ta janyo wayarta ta soma neman mamanta,ba jimawa ta daga,sunyi hira sosai ta tambayeta 'yan jikokin nata tace duka sunyi bacci,suna gamawa ta katse ta kira halima suka gaisa ta hadata da abdallah wanda keta karatun common intrance za'a shiga secondry,suka gama hirarsu ta masa addu'a sannan ta kira zainab itama suka gaisa,tace gata kwance shiru gidan ba dadi duk sabida ba hayaniyar yara,gashi sabon gida suka koma sabuwar unguwa,dariya tayi tace idan zaki kwanta ma kiyi baccinku gwara kiyi,donsu yanzu haka ma sun jima da yin bacci,dariya tayi suka dan taba hira sannan ta katse ta kira nafisa,itama yaran nafisan na wajenta su biyu,sunyi hira abinsu sosai irinta qawaye kafin suyi sallama,daga qarshe ta kira yaya yahansu wadda a yanzun ta bata jari take business ba saida atamfofi,ba qaramin ciniki take ba,sosai rayuwarta data yaranta dake gidan aure ta inganta sai son barka,dai dai sanda ta ajjiye wayar ya fito yana tsabe jikinsa da towel,suka sakw hada ido ta kauda kai,dariya yake qoqarin boyewa amma ya kasa,ya sani cewa ta koyi fushi cikin kwanakin tun kafin tasan cewa tana da cikin,wanda yasan baya rasa nasaba da cikin da take da shi,kowanne ciki akwai irin yanayin da yake zuwa ma mace da shi,yadda ta hade rai ya sanya dariyar fitowa a dole,sai ta juyo ta dubeshi take ta saka kuka kaman qaramar yarinya,dariya yake sosai ya ajjiye towel din ya tako zuwa inda take
"U r craying like a baby,ko qarami bazayayi irin wannan kukan ba,wai mema aka miki,you beat my daughter bance dake komai ba,shi ya bata miki rai ko kuwa?"
"Wallahi hancina kakewa dariya" ta fada taba shafa hancin wanda sai yanzu taji alamun ya bude kaman cikin 'yan biyu,wata dariyar ce ta sake hardeshi,yayin data qara volume na kukanta,ganin tana kukan bilhaqqi ya sanya ya fara damunsa,sai ya sassauta dariyan ya tako gabanta,kan gwiwoyinshi ya durqusa,yasa duka hannyenshi ya kama kunnuwansa yana cewa
"Is ok...am sorry...am really sorry babe,idan baki huce ba kimin duk hukuncin da kike so" sai ta fara sassauta kukan tana kallonshi,tsahon minti biyar kafin tace
"Labari zaka ta bani har na awa daya" dariya ta sake kamashi wannan karon ya maidata,yasani sarai mugunta ta shirya masa,ra ina zai iya surutu na awa daya ai da sai yasha magani,sai ya narke mata kalan tausayi ya sanya tafin hannunshi duka biyu a kumatunsa alaman tagumi
"Wayyo ummina....kina ina ana punishing dina"salon yadda yayi maganan dole ya baka dariya,sai data daara sannan ta maze
"ba ruwan ummi a nan,ita ta aikeka kayi tsokana?....so tunda karanta labarai ya maka tsauri sai kayi kamun kunne ko tsallen kwado wanne yafi maka?" Hannayenshi ya hade waje daya yana jujjuya kai
"Almustapha yau kaga ta kanka wallahi,ka tabo uwar biyun nan" idanu ta zaro
"Wa ya gaya maka 'yan biyu zan haifa?"
"In sha Allahu,kisa ido ki gani,zuwana umara na qarshe kafin ki samu cikin su na roqa,kuma nasan in sha Allah Allah ya amsa" harararshi tayi,sai ya saki dariya ya miqe yana dagata
"Kinga....naga labarin babba ne,muje kiyi wanka kizo kiji" shi ya rakata ya kuna tsayata ta gama wankan suka dawo dakin tare.
Chapter 225 · 0% Book details