Sashe 184
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Lokaci ta bata sosai a toilet tana murje jikinta,ita kanta mamakin yadda fatarta ke sheqi da laushi tayi,saidai tana ganin kayan gyaran jikin data yi amfani da su ne suka amsheta,kwalliya tayi maras yawa saidai ta dace da kyakkyawar madaidaiciyar fuskarta,ta sake kuma fito da armashin kyanta,ta jima tana saqe saqen wanne kaya zata saka,wando ta ciro belted high top wide leg trouser ash colour ta hadashi da long sleeve t.shirt fara qal wadda aka yiwa adon ash daga wuyan rigan zuwa qasanta,kisonta ta raba jelar gida biyu ta kama kowanne da qaramin ribbom ash,ba qaramin kyau tayi ba,duk wani tudu da kwari na jikinta ya fito turarukanta na musamman tayi amfani da shu,wadanda qamshinsu ke tashi a hankali har su gama cika hancin mutum,kwalabar turarenta babba ta dauka bayan ta kammala komai,ta zira wani irin plate din farin takalmi mai taushi ta soma bin duk inda burner take a gidan tana zuba turaren,a haka har ta qaraso falon.
Tana durqushe kusa da burner din dake bakin matattakala tana zuba turare a ciki taji an bude qofar sashen,batayi tsammanin ganin kowa ba hakan ya sanya ta fito haka,a nutse ta juya,almustapha ne a gaba su'ad na biye da shi
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" ya ambata yana lunahe idain nasa sanda idanunshi sukayi tozali da nata,karon farko da ya soma ganinta cikin suturar da ta bayyana duk wani structure ta jikinta,su'ad dinma idanuwanta na kanta,mamaki da kishi suka cikata,take wani bacin rai ya lullubeta,dama yarinyar tasan sanya ire iren kayansu?,ba sai an gaya mata tahowarta din nan taga shigen kayan a shagon da take siyayya acan,taso siyosu saboda tasan zasu burge almustapha kuma sun burheta itama,bugu da qari kayan sabbin design ne da suka fito sati sati uku kacal da suka wuce,amma saboda kudin hannunta yayi qasa ta haqura,kishin yanayin halittar da Allah yayi mata ya cika mata zuciya,ba zata manta ba har mai ta saya na qara mazaunai da qirji amma almustapha ya hanata shafawa,ya zaunar da ita yana gaya mata irin illolin dake tattare da irin wadan nan mayukan da kuma na bleeching,duk da bata taba bleeching ba ita,natural farinta ne,to amma ko banza yau gashi ya dauko mai abun,ita tana zaune,kewayeshi tayi ta wuce corridor dinta da zaya kaita ga dakinta kai tsaye,zuciyarta na tafasa,kamar ta shaqe kanta,ta wurga jakarta saman gado tare da tuje mayafin kanta ta wurgar shima tana yamutsa gashin kanta
"No....no,it can't" ta dinga maimaitawa tana girgiza kai,sai ta sake takowa a hankali ta dawo corridor din nata,ta tsaya tsakanin labulayen da suka rabata da hango falon kai tsaye,ta sanya hannu ta yaye labulen ta yadda zata iya hangosu.
Tattausan murmushi ya soma sakin mata idanunshi cike taf da mayen qaunarta,ita dinma duban shi take fuskarta dauke da murmushi,duban cikin idanunshi kadai sun gamsaf da ita,wani irin qauna take ji na daban na ratsata,qwafin gwiwa game da shi take ji,ya bude dukka hannayenshi yana mata alama ta taho,sai ta noqe kai kamar qaramin yaro yaso quya cikin wani salo na daban,ya motsa bakinsa cikin muryarsa da har gobe take sake daukaka darajarshi cikin idanunta
"Don't kill me babe,taho please" a yangance ta soma takowa,sai ya kasa jiranta har ta qaraso inda yake,ya soma shima takawa a hankali suka hade tsakiyan falon,kyakkyawan masauki yayi mata a qirjinsa yana sakin wawuyar ajiyar zuciya,baisan ta taka wannan matsayin cikin zuciyarsa ba karo na biyu sai a yau ya sake tabbatarwa,qamshin dake tashi kawai jikinta ya isar masa samun nutsuwa da kwanciyar hankali,sumbarta ya soma yi a ajejjere tako ina cikin nuna zallar soyayya da shauqi.
Cikin matsanancin tashin hankali ta saki labulen ta shiga dakinta a sukwane ta soma ball da jakarta data yar a bakin qofa
"No almustapha,no,why u r doing this" ta ambata tana dukan bango da hannunta,kana ta tafi saman madubinta ta soma watsar da dukkan abinda ta gani samanshi suna sauka qasa gami da tarwatsewa saman tiles,wannan bai isheta ba sai data dauki kwalbar turarenta ta doka jikin madubi,tunu ya tarwatse dai dai ya kuma yi silar yankarta.
Qarar wannan fashewar kayayyaki ita ta dawo da almustapha hayyacinsa,idan dai dai kunnuwansa ke jiye masa daga dakin su'ad ne,cikin hanzari ya raba sumayya daga jikinsa ya juya zuwa dakin,hawaye shabe shabe ya sameta tanayi bayan tarwatsa gashin ta dake daure da tayi,bata damu ba tana ci gaba da jifa da dauk abinda hannunta ya kai kai ciki har da t.v plasma dake manne a bangon dakin ta kwada mata make up kit din data wawuro,riqota yayi yana ambatar
"Meye haka su'ad,hankalinki daya kuwa" yunqurin qwacewa take
"Leave me almustapha,leave me" ganin haukar tata da gasje take ya sanyashi daka mata tsawa wadda ta sanya sumayya dake tsaye falo hankalinta yayi matuqar tashi
"U r mad?!,baki ganin wai me kike yi ne?"
"I know almustapha,am going to kill my self ma gaba daya" tsatstsauran riqo yayi mata sanda yaga tana laluben kwalabar dake farfashe a wajen,ya damqeta baki daya ya hankadata saman yamutsatstsen gadonta,ranshi ya kai qololuwar baci,sai kace tabin jinnu?,yanzun nan fa suka shiga gidan tare lafiya lau,binta gadon yayi ya mata riqon tsauri tana gunjin kuka tare da yunqurin qwacewa.
A qalla sun tasamma kashe mintuna goma a haka kafin ta soma sassauta haukan da take yi,sai kuma kuka da taci gaba da yi,cikin fargaba da nutsuwa sumayya tayi sallama bakin qofar dakin,a karon farko kenan,sanye da dogon hijabinta har qasa,waiwayowa yayi da jajayen idanunshi ya zubeta kanta,wadda ita kuma idanunta ke qarewa yadda dakin ya hargitse kallo,ko bai bata amsa ba ta soma hasashen abinda ke faruwa,ba zata manta ba,ba zata manya daren data yankeshi a hannu ba sanadin kishi
"Jeki am comming,everything will be okey" kai ta jinjina ta juya ta fice,idan da tasan ma abinda ke faruwa kenan ba zata bata lokaci ta shigo duba abinda ke faruwa ba,ranta ya dinga baci,me mata suka mayarda kishi ne?,tabbas babu halittar da bata da kishi,kishi halitta ce,kuma dole kayi kishin abinda kake so,hatta dabba tana da kishi,to amma meye amfanin hankali kenan?,meye amfanin ilimi?,meye amfanin girma da shekaru?,sai ta tsinci kanta ta mai jan tsaki data tuna zainab fa'iza karima ga kuma su'ad.
Miqewa yayi cikin takatsantsan don ma qafanshi da sau ciki ya laluba inda suka ajiyan kayan akwatin taimakon gaggawa,ya qaraso inda take,har yau qwalla na bin idanunta,tsugunnawa yayi ya soma mata dressing inda ta yanke ba tare da yace komai ba,idonta na kanshi ta soma maganganu cikin dashewar murya,tsaf ya fahimci abinda ya jawo mata aikata hakan,baya ga kishi har labe kenan ta soma?,abinda ya tunzura shi kenan,yana jin kamar ya dauketa da mari zuciyarsa na tausarshi,har ya kammala wanke mata tsaf,yayi kama hannunta ba tare da ya dubeta ba yayi mata allurar rage radadin ciwo ya maida akwatin muhallinsa ya juya da niyyar ficewa,qam ta riqe hannunshi ciki marairaicewa
"Kada ka tafi ka barni na roqeka almustapha,kada kaje wajen yarinyar nan,duk abinda kake so zan maka" idanunsa da suka sauyi launi kadai da ya watsa mata ya sata laushi kaso hamsin cikin dari
"Sake ni!" Ya fada a tsawace,sakin nasa tayi yaja baya baki bude tana kallonshi har ya fice a dakin,a falo ya tsaya ya fiddo wayarsa ya kira ummee yace ta turo ma'aikatan nan dakin su'ad zasuyi dan wani aiki,ya gama ya maida wayar aljihunsa ya wuce bedroom dinshi.
Tana durqushe kusa da burner din dake bakin matattakala tana zuba turare a ciki taji an bude qofar sashen,batayi tsammanin ganin kowa ba hakan ya sanya ta fito haka,a nutse ta juya,almustapha ne a gaba su'ad na biye da shi
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" ya ambata yana lunahe idain nasa sanda idanunshi sukayi tozali da nata,karon farko da ya soma ganinta cikin suturar da ta bayyana duk wani structure ta jikinta,su'ad dinma idanuwanta na kanta,mamaki da kishi suka cikata,take wani bacin rai ya lullubeta,dama yarinyar tasan sanya ire iren kayansu?,ba sai an gaya mata tahowarta din nan taga shigen kayan a shagon da take siyayya acan,taso siyosu saboda tasan zasu burge almustapha kuma sun burheta itama,bugu da qari kayan sabbin design ne da suka fito sati sati uku kacal da suka wuce,amma saboda kudin hannunta yayi qasa ta haqura,kishin yanayin halittar da Allah yayi mata ya cika mata zuciya,ba zata manta ba har mai ta saya na qara mazaunai da qirji amma almustapha ya hanata shafawa,ya zaunar da ita yana gaya mata irin illolin dake tattare da irin wadan nan mayukan da kuma na bleeching,duk da bata taba bleeching ba ita,natural farinta ne,to amma ko banza yau gashi ya dauko mai abun,ita tana zaune,kewayeshi tayi ta wuce corridor dinta da zaya kaita ga dakinta kai tsaye,zuciyarta na tafasa,kamar ta shaqe kanta,ta wurga jakarta saman gado tare da tuje mayafin kanta ta wurgar shima tana yamutsa gashin kanta
"No....no,it can't" ta dinga maimaitawa tana girgiza kai,sai ta sake takowa a hankali ta dawo corridor din nata,ta tsaya tsakanin labulayen da suka rabata da hango falon kai tsaye,ta sanya hannu ta yaye labulen ta yadda zata iya hangosu.
Tattausan murmushi ya soma sakin mata idanunshi cike taf da mayen qaunarta,ita dinma duban shi take fuskarta dauke da murmushi,duban cikin idanunshi kadai sun gamsaf da ita,wani irin qauna take ji na daban na ratsata,qwafin gwiwa game da shi take ji,ya bude dukka hannayenshi yana mata alama ta taho,sai ta noqe kai kamar qaramin yaro yaso quya cikin wani salo na daban,ya motsa bakinsa cikin muryarsa da har gobe take sake daukaka darajarshi cikin idanunta
"Don't kill me babe,taho please" a yangance ta soma takowa,sai ya kasa jiranta har ta qaraso inda yake,ya soma shima takawa a hankali suka hade tsakiyan falon,kyakkyawan masauki yayi mata a qirjinsa yana sakin wawuyar ajiyar zuciya,baisan ta taka wannan matsayin cikin zuciyarsa ba karo na biyu sai a yau ya sake tabbatarwa,qamshin dake tashi kawai jikinta ya isar masa samun nutsuwa da kwanciyar hankali,sumbarta ya soma yi a ajejjere tako ina cikin nuna zallar soyayya da shauqi.
Cikin matsanancin tashin hankali ta saki labulen ta shiga dakinta a sukwane ta soma ball da jakarta data yar a bakin qofa
"No almustapha,no,why u r doing this" ta ambata tana dukan bango da hannunta,kana ta tafi saman madubinta ta soma watsar da dukkan abinda ta gani samanshi suna sauka qasa gami da tarwatsewa saman tiles,wannan bai isheta ba sai data dauki kwalbar turarenta ta doka jikin madubi,tunu ya tarwatse dai dai ya kuma yi silar yankarta.
Qarar wannan fashewar kayayyaki ita ta dawo da almustapha hayyacinsa,idan dai dai kunnuwansa ke jiye masa daga dakin su'ad ne,cikin hanzari ya raba sumayya daga jikinsa ya juya zuwa dakin,hawaye shabe shabe ya sameta tanayi bayan tarwatsa gashin ta dake daure da tayi,bata damu ba tana ci gaba da jifa da dauk abinda hannunta ya kai kai ciki har da t.v plasma dake manne a bangon dakin ta kwada mata make up kit din data wawuro,riqota yayi yana ambatar
"Meye haka su'ad,hankalinki daya kuwa" yunqurin qwacewa take
"Leave me almustapha,leave me" ganin haukar tata da gasje take ya sanyashi daka mata tsawa wadda ta sanya sumayya dake tsaye falo hankalinta yayi matuqar tashi
"U r mad?!,baki ganin wai me kike yi ne?"
"I know almustapha,am going to kill my self ma gaba daya" tsatstsauran riqo yayi mata sanda yaga tana laluben kwalabar dake farfashe a wajen,ya damqeta baki daya ya hankadata saman yamutsatstsen gadonta,ranshi ya kai qololuwar baci,sai kace tabin jinnu?,yanzun nan fa suka shiga gidan tare lafiya lau,binta gadon yayi ya mata riqon tsauri tana gunjin kuka tare da yunqurin qwacewa.
A qalla sun tasamma kashe mintuna goma a haka kafin ta soma sassauta haukan da take yi,sai kuma kuka da taci gaba da yi,cikin fargaba da nutsuwa sumayya tayi sallama bakin qofar dakin,a karon farko kenan,sanye da dogon hijabinta har qasa,waiwayowa yayi da jajayen idanunshi ya zubeta kanta,wadda ita kuma idanunta ke qarewa yadda dakin ya hargitse kallo,ko bai bata amsa ba ta soma hasashen abinda ke faruwa,ba zata manta ba,ba zata manya daren data yankeshi a hannu ba sanadin kishi
"Jeki am comming,everything will be okey" kai ta jinjina ta juya ta fice,idan da tasan ma abinda ke faruwa kenan ba zata bata lokaci ta shigo duba abinda ke faruwa ba,ranta ya dinga baci,me mata suka mayarda kishi ne?,tabbas babu halittar da bata da kishi,kishi halitta ce,kuma dole kayi kishin abinda kake so,hatta dabba tana da kishi,to amma meye amfanin hankali kenan?,meye amfanin ilimi?,meye amfanin girma da shekaru?,sai ta tsinci kanta ta mai jan tsaki data tuna zainab fa'iza karima ga kuma su'ad.
Miqewa yayi cikin takatsantsan don ma qafanshi da sau ciki ya laluba inda suka ajiyan kayan akwatin taimakon gaggawa,ya qaraso inda take,har yau qwalla na bin idanunta,tsugunnawa yayi ya soma mata dressing inda ta yanke ba tare da yace komai ba,idonta na kanshi ta soma maganganu cikin dashewar murya,tsaf ya fahimci abinda ya jawo mata aikata hakan,baya ga kishi har labe kenan ta soma?,abinda ya tunzura shi kenan,yana jin kamar ya dauketa da mari zuciyarsa na tausarshi,har ya kammala wanke mata tsaf,yayi kama hannunta ba tare da ya dubeta ba yayi mata allurar rage radadin ciwo ya maida akwatin muhallinsa ya juya da niyyar ficewa,qam ta riqe hannunshi ciki marairaicewa
"Kada ka tafi ka barni na roqeka almustapha,kada kaje wajen yarinyar nan,duk abinda kake so zan maka" idanunsa da suka sauyi launi kadai da ya watsa mata ya sata laushi kaso hamsin cikin dari
"Sake ni!" Ya fada a tsawace,sakin nasa tayi yaja baya baki bude tana kallonshi har ya fice a dakin,a falo ya tsaya ya fiddo wayarsa ya kira ummee yace ta turo ma'aikatan nan dakin su'ad zasuyi dan wani aiki,ya gama ya maida wayar aljihunsa ya wuce bedroom dinshi.