Sashe 86
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cike da kunya girmamawa da mutun tawa ta isa gabanshi kanta a qaaa,kwarjini dattijon yake mata kamar malam dinta,cikin ban girma ta gaidashi sannan ta gaida ummee dake zaune gefansa,ta amsa itama fuska sake,hakanan take jin nauyin mutanen,duk da baki dayansu baifi gani biyu zuwa uku tayi musu ba
"Da tafiya zaki mama na bakimin sallama ba?,haba,shekara daya ba nan kusa bace bafa?,kika sani ko kafin ki dawo ta Allah ta kasance a kanmu" sai taji ba dadi,ita din saurin karayar zuciya,zuciyar tata ta karye,duk sai taji babu dadi har sai data dago ta dubeshi,ya tuna mata da mukhtar dinta yayin da mutuwa ta daukeshi a ranar da yake shirin sake angwancewa da ita,tabbas mutuwa bata da sabo,amma bata fatan hakan ta kasance kan dattijon,tana jin qaunarsa a ranta kamar malam dinta,duk sanda ta kalleshi yana tuna mata da malam din
"Bama fatan haka baabaa,Allah qara muku tsawon kwana da lafiya mai amfani"
"Amin amin" umme amira da baban suka amsa baki daya,amira ke turo baki tunda baban ya fadi maganar,ta kasa shiru sai data tanka
"Wai baabaa fata kake ne ka mutu ka barmu,kullum sai kayi zancan mutuwa,bayan ko aurena ni auta baka gani ba,ga yaya mahmoud da usama" dariya yayi irinta dattawa sannan yace
"Mama na kenan,banda abinki ita mutuwa ina ruwanta da wanu tsari naka,duk sanda tazo daukarka zata yi bafa zata fasa ba,ko babu ita akwai rabuwa,zaka rabu da mutum wanda ba lallai ka sake ganinsa,kamar yadda har yau nake burin ganin wani tsohon abokina da mukayu rayuwa a karkara tare,har yau Allah bai nufi zan ganshi ba,har yau kuma yana raina" tuni idanunta ya soma digar hawaye kanta na a qasa,baabaa yayi mata fami sosai,baima lura da ruwan hawayen nata ba,ya ciro wasu kudade irin na qasar engaland din masu kauri ya miqa mata
"Ungo wannan mamana,kiyi amfani da su kinji sune tsarabata" bata son ta daga kai yaga hawayenta,sabida haka ta sanya hannu bibbiyu ta amsa tana masa godiya mai cike da fatan alkhairi sannan ta miqe ta juya ta fita,amira ce ta kalli baabaa
"Baabaa,zan rakasu airphort don Allah" umme ce ta cafe zancen
"Umhummm,wato zaki raka qawarki ko?,ina cewa nan su'ad tayi tayi ki rakata randa zasu tafi kika qi,sai yanzu jikinki na rawa zaki ce zaki,to ba inda zaki din"
"Saurara KILISHI,Allah shike hada qauna tsakanin mutum da mutum,haka kawai Allah ya hada jininta da yarinyar,barta taje,mama na sai kun dawo,daga nan kada ki biya ko ina,ki dawo kizo kimin lissafin me kike buqata na komawa makaranta kinji" cikin murna kamar qaramar yarinya tace
"Yauwa baabaa na,na gode"ta juya da sauri don ta ruski su sumayya.
Cikin motar amiran ke basu labarin yadda garin yake,duk da yake akwai banbancin gari,garin data zauna su ba nan zasu zauna ba,su laila an kasa kunne ana kwashewa,murna da doki sun cikata burinta kawai su isa.
Cikin qanqanin lokaci suka isa filin sauka da tashin jiragen sama na Nnmdi azikwe dake garin abuja,bai wuce mintuna talatin ba lokacin tafiyarsu yayi,sabida haka uncle farouq ya sallami driver din wanda ya tilasta amira yiwa sumayya sallama saboda tare zasu koma,duj fuskarta ta nuna rashin jin dadin tafiyar tasu,kai kace sunyi mugun sabo da juna
" nikam irin wannan qauna haka da amira ke gwada miki,bata da saurin sabi da sakin jiki wa mutane fa,amma ke naga ta sake miki"murmushi sumayya tayi kawai tana miqawa anty dije kudaden da baaban ya bata,kanta qulle tamau da mamakin wanne irin arziqi baabaa ke dashi haka,duk da batasan kan kudaden waje ba amma tana jin labarin darajarsu fiye da namu na naija,kuma yanzu haka wadanda ke hannunta ba daya biyu uku biyar bane,sunfi haka,ido itama ta zaro
"Wa ya miki kyautar wadan nan kudin?"
"Baabaa ne"
"Kai baabaa,baabaa,alkhairinsa yawa gareshi,Allah ya saka masa da alkhairi"
"Amin,amma anty su basujin kyauta haka" murmushi ta kuma
"Haka suke,hannun kyauta garesu,suna da mutunci da karamci,yaci ace kisan ko su waye su din,amma bari mu shiga jirgi zan gaya miki su waye su" bata kai ga amsawa ba wayarta da zuci zucin ta kashe ta soma ruri,number amira ce,cikin mamaki ta daga
"Ya mahmoud ne zai magana da ke" ta fada tana hadata da shi
"Babu fada me ya kawo gaba gimbiyarmu,yanzu fi sabilillih zaki bar naija amma ko ki sanar da abokina why?" Murmushi ta danyi
"Tunda ka sani ka wakilceshi ya mahmoud,kaa gaya masa"
"A'ah,wannan saqon ai na masoya ne,amma tunda kince haka zan gaya masa,ta inda kuma zaki wanke kanku guna indai ni yayanne ki bada num dinki idan kun isa na bashi" dariya ma ya bata,saidai yana da qima idanuwanta,shine mutum na farko da ya fara tararta cikin fara'a da girmamawa sanda ta tsoma qafarta gidan baabaa prof
"Babu matsala"
"To ina godiya,inawa umman khalipha fatan alkhairi ki sanar mata" ya datse layin,tana shirin maida wayar jaka saqon fatan alkahiri daga abdur rahman ya shigo mata,ta karanta a gurguje ta mayar masa da reply.
Idanu sumayyan ta shiga bazawa bayan tsintar kanta da tayi cikin jirgi ya soma dagawa da ita zuwa sararin subhana,bata samu nutsuwa ba sai bayan shudewar wasu lukatai sannan,anty dije ce a damanta
"Bari na cika alqawa ko,na gaya miki tarihin gidan baabaa prof"
"To anty ina jinki"
*IYALAN GIDAN BAABAA*
BAABA prof ba shine asalin sunanshi ba,suna ne da ya samu ta dalilin zuzzurfan ilimin boko da yayi har ya kaishi ga zama professor,cikakken sunansa shine MUKHTAR MUHAMMAD ADAM GWAMBE,haiffen wani qauye da ke cikin pantami,mahaifinsa Adamu wanda aka fi sani da mai dabba,wanda ya ci sunan nashi ne sabida yadda Allah dora masa so da iya kiwon dabbobi tun yana qanqaninsa,ga tausayi ga dabbobi,bama dabbobi kadai ba hatta da mutane,ana amfana qwarai da tarin dukiyar da Allah ya huwace masa,wajen taimako ga mabuqata,bafulatani ne gaba da baya,ma'abocin iya kiwo,wanda kuma Allah ya albarkaceshi da tarin dabbobi,kama daga tumakai awakai raguna tinkiyoyi da shanu bila addin,wand kaf qauyensu da kewayenshi babu wanda ya kaishi yawan garke,matarshi daya khadijatu,ita ta haifa masa muhammadu da yayyensa guda biyu,dukkaninsu suna ganiyar samartaka suka rasu sai muhammadun kadai da Allah ya bar masa,yaro ne da yafi shiga ransa duk cikin yaranshi,ya debo kyawawan halayensu tsaf har da ma qari,sannu a hankali muhammadu ya girma aka hadashi aure da wata yarinyar wani malami maqocinsu mai suna naja'atu,cikin watanni tara kacal Allah ya albarkaceta ta haifi MUKHTAR baabaa prof,wanda ba'a jima da haihuwarsa ba Allah ya yiwa mai dabba rasuwa,ya rasu ya bar matarshi,bayan share makoki aka raba gado aka baiwa khadija matarsa da dansa muhammadun,ya karbi dukiyar mahaifinsa kuwa a sa'a don habaka tayi tayi,abu ya dinga dad gaba,saidai daga baya ya fuskanci kamar kiwon wahala ce kawai,ya saida shanun ya rage wasu daga ciki ya barwa mukhtar kyauta halak malak,yace shima ya taba aikin gado,dama can shi mai son kiwo ne,tare suke fita da shaqiqin abokinsa wanda tun yana da shekara daya a duniya baida aboki sama da SULAIMAN sule,babu abinda ke rabashi da sule,hatta bacci ma wani sa'i tare suke,musamman idan matar babanshi taso tsiyar tata,tausayinsa yake,qaunarsa yaje fusabilillah,mahaifiyarsa ta raau tun randa ta haifeshi ko waiwayowa batayi taga abinda ta haifa din bata yi ba,sai suka qulle sosai,muntari baida qani balle ya debe masa kewa,haka sule ma baida dan uwa sai hashimu,shi kuwa bai isa ya rabeshi ba don tuni altine ta shiga tsakaninsu ta raba zumuncin Allah qarfi da yaji,duk da hashimun na qaunar dan uwansa,tare suka dinga fita kiwo shi da sule,yayin da babansa muhammadu kuma ya soma saida zannuwa a cikin garin gwambe,dukkaninsu Allah ya sanya musu albarka baki dayansu,har mamakin yadda dabbobin muntarin keta habaka babansa muhammadu keyi,shida sule kiwo suke haiqan,duk da babu dabbar sulen ko daya a ciki amma sabida qaunar dake tsakaninsu wani lokaci a shike fitar ma muntarin da su,altine tayi dukan,tayi dukan don ta raba tsakninsu saboda yadda taga suke na samun kulawa a gidansu muntarin amma a banza wai man kare,saboda tare malam muhammadu ke musu komai,bai rasa ci ko sha ba balle sutura,ba'a rabasu a gidan sule dai dai yake da muntaru,data gama dukan zata kuma gansu tare,abun ya tsaya mata a rai,sai ta koma ziga gun babansa,to shi din ma baici nasarar rabasu din ba,saboda yadda qauyen aka soma zaginsa shi da matarsa kan yadda suka qwallafawa dan marayan Allahn.
Cikin haka turawa suka shigo qauyen nasu,suka kawo musu makarantar boko har cikin garin nasu,kowa ya tsame dansa yace babu shi a wannan batu,muntari na bala'in sha'awar karatun,ya samu babansa ya sanar masa kan ya sanyasu shi da sule,da fari shima yace sam kada muntarin ya sake wannan magana,bayan dogon nazari da malam muhammadun yayi sai ya amince,ya hadasu da sule ya kaisu amma yace saidai suyi jeka ka dawo(day),altine zani a hannu ta shaidawa mahaifin sule abinda malam mahammadu yayi,ai kuwa ya wanke qafa yaje har gida ya ciwa malam mahammadu mutunci,a lokacin sule na gidan tare da muntari,kuka ya dinga yi yana jan baban nasa kan ya daina zaginsa amma ya mangareshi ya qara gaba,tilas malam ya lallashi sule kan yayi haquri tunda babansa baya so,haka ya haqura ba don rai naso ba,ya ci gaba da fitar da shanun muntari kafin ya dawo daga makaranta sai ya taddashi a jeji suci gaba da kiwon tare da yammaci su dawo gida,malam muhammadu yace ya ya daina,ya bari idan muntarin ya dawo sa fita tare su dawo tare,amma sam yace a'a,ai shi da muntarin duka daya ne,duka a lokacin basu wuce shekara goma sha uku uku ba.
A haka shanun muntari suka sake yawa,ga cikakkiyar lafiya dake garesu,ganin haka ya sanya muntari ya shawarta da malam muhammadu zai raba dabbobin biyu ya baiwa sule rabi,saboda wahalar da yake da su ko shi sai haka,ba musu dukka suka amince har da mahaifiyarsa,randa ya sanar da sule cewa yayi bazai karba,shi don Allah don qauna da amincin dake tsakaninsu yake masa,tilas daga qarshe malam muhammadu ya tilas ta shi ya karba,godiya ya dinga musu harda hawaye,din suna da yawa baiyi tsammanin mallakar wani abun duniya kwatankwacin haka ba.
"Da tafiya zaki mama na bakimin sallama ba?,haba,shekara daya ba nan kusa bace bafa?,kika sani ko kafin ki dawo ta Allah ta kasance a kanmu" sai taji ba dadi,ita din saurin karayar zuciya,zuciyar tata ta karye,duk sai taji babu dadi har sai data dago ta dubeshi,ya tuna mata da mukhtar dinta yayin da mutuwa ta daukeshi a ranar da yake shirin sake angwancewa da ita,tabbas mutuwa bata da sabo,amma bata fatan hakan ta kasance kan dattijon,tana jin qaunarsa a ranta kamar malam dinta,duk sanda ta kalleshi yana tuna mata da malam din
"Bama fatan haka baabaa,Allah qara muku tsawon kwana da lafiya mai amfani"
"Amin amin" umme amira da baban suka amsa baki daya,amira ke turo baki tunda baban ya fadi maganar,ta kasa shiru sai data tanka
"Wai baabaa fata kake ne ka mutu ka barmu,kullum sai kayi zancan mutuwa,bayan ko aurena ni auta baka gani ba,ga yaya mahmoud da usama" dariya yayi irinta dattawa sannan yace
"Mama na kenan,banda abinki ita mutuwa ina ruwanta da wanu tsari naka,duk sanda tazo daukarka zata yi bafa zata fasa ba,ko babu ita akwai rabuwa,zaka rabu da mutum wanda ba lallai ka sake ganinsa,kamar yadda har yau nake burin ganin wani tsohon abokina da mukayu rayuwa a karkara tare,har yau Allah bai nufi zan ganshi ba,har yau kuma yana raina" tuni idanunta ya soma digar hawaye kanta na a qasa,baabaa yayi mata fami sosai,baima lura da ruwan hawayen nata ba,ya ciro wasu kudade irin na qasar engaland din masu kauri ya miqa mata
"Ungo wannan mamana,kiyi amfani da su kinji sune tsarabata" bata son ta daga kai yaga hawayenta,sabida haka ta sanya hannu bibbiyu ta amsa tana masa godiya mai cike da fatan alkhairi sannan ta miqe ta juya ta fita,amira ce ta kalli baabaa
"Baabaa,zan rakasu airphort don Allah" umme ce ta cafe zancen
"Umhummm,wato zaki raka qawarki ko?,ina cewa nan su'ad tayi tayi ki rakata randa zasu tafi kika qi,sai yanzu jikinki na rawa zaki ce zaki,to ba inda zaki din"
"Saurara KILISHI,Allah shike hada qauna tsakanin mutum da mutum,haka kawai Allah ya hada jininta da yarinyar,barta taje,mama na sai kun dawo,daga nan kada ki biya ko ina,ki dawo kizo kimin lissafin me kike buqata na komawa makaranta kinji" cikin murna kamar qaramar yarinya tace
"Yauwa baabaa na,na gode"ta juya da sauri don ta ruski su sumayya.
Cikin motar amiran ke basu labarin yadda garin yake,duk da yake akwai banbancin gari,garin data zauna su ba nan zasu zauna ba,su laila an kasa kunne ana kwashewa,murna da doki sun cikata burinta kawai su isa.
Cikin qanqanin lokaci suka isa filin sauka da tashin jiragen sama na Nnmdi azikwe dake garin abuja,bai wuce mintuna talatin ba lokacin tafiyarsu yayi,sabida haka uncle farouq ya sallami driver din wanda ya tilasta amira yiwa sumayya sallama saboda tare zasu koma,duj fuskarta ta nuna rashin jin dadin tafiyar tasu,kai kace sunyi mugun sabo da juna
" nikam irin wannan qauna haka da amira ke gwada miki,bata da saurin sabi da sakin jiki wa mutane fa,amma ke naga ta sake miki"murmushi sumayya tayi kawai tana miqawa anty dije kudaden da baaban ya bata,kanta qulle tamau da mamakin wanne irin arziqi baabaa ke dashi haka,duk da batasan kan kudaden waje ba amma tana jin labarin darajarsu fiye da namu na naija,kuma yanzu haka wadanda ke hannunta ba daya biyu uku biyar bane,sunfi haka,ido itama ta zaro
"Wa ya miki kyautar wadan nan kudin?"
"Baabaa ne"
"Kai baabaa,baabaa,alkhairinsa yawa gareshi,Allah ya saka masa da alkhairi"
"Amin,amma anty su basujin kyauta haka" murmushi ta kuma
"Haka suke,hannun kyauta garesu,suna da mutunci da karamci,yaci ace kisan ko su waye su din,amma bari mu shiga jirgi zan gaya miki su waye su" bata kai ga amsawa ba wayarta da zuci zucin ta kashe ta soma ruri,number amira ce,cikin mamaki ta daga
"Ya mahmoud ne zai magana da ke" ta fada tana hadata da shi
"Babu fada me ya kawo gaba gimbiyarmu,yanzu fi sabilillih zaki bar naija amma ko ki sanar da abokina why?" Murmushi ta danyi
"Tunda ka sani ka wakilceshi ya mahmoud,kaa gaya masa"
"A'ah,wannan saqon ai na masoya ne,amma tunda kince haka zan gaya masa,ta inda kuma zaki wanke kanku guna indai ni yayanne ki bada num dinki idan kun isa na bashi" dariya ma ya bata,saidai yana da qima idanuwanta,shine mutum na farko da ya fara tararta cikin fara'a da girmamawa sanda ta tsoma qafarta gidan baabaa prof
"Babu matsala"
"To ina godiya,inawa umman khalipha fatan alkhairi ki sanar mata" ya datse layin,tana shirin maida wayar jaka saqon fatan alkahiri daga abdur rahman ya shigo mata,ta karanta a gurguje ta mayar masa da reply.
Idanu sumayyan ta shiga bazawa bayan tsintar kanta da tayi cikin jirgi ya soma dagawa da ita zuwa sararin subhana,bata samu nutsuwa ba sai bayan shudewar wasu lukatai sannan,anty dije ce a damanta
"Bari na cika alqawa ko,na gaya miki tarihin gidan baabaa prof"
"To anty ina jinki"
*IYALAN GIDAN BAABAA*
BAABA prof ba shine asalin sunanshi ba,suna ne da ya samu ta dalilin zuzzurfan ilimin boko da yayi har ya kaishi ga zama professor,cikakken sunansa shine MUKHTAR MUHAMMAD ADAM GWAMBE,haiffen wani qauye da ke cikin pantami,mahaifinsa Adamu wanda aka fi sani da mai dabba,wanda ya ci sunan nashi ne sabida yadda Allah dora masa so da iya kiwon dabbobi tun yana qanqaninsa,ga tausayi ga dabbobi,bama dabbobi kadai ba hatta da mutane,ana amfana qwarai da tarin dukiyar da Allah ya huwace masa,wajen taimako ga mabuqata,bafulatani ne gaba da baya,ma'abocin iya kiwo,wanda kuma Allah ya albarkaceshi da tarin dabbobi,kama daga tumakai awakai raguna tinkiyoyi da shanu bila addin,wand kaf qauyensu da kewayenshi babu wanda ya kaishi yawan garke,matarshi daya khadijatu,ita ta haifa masa muhammadu da yayyensa guda biyu,dukkaninsu suna ganiyar samartaka suka rasu sai muhammadun kadai da Allah ya bar masa,yaro ne da yafi shiga ransa duk cikin yaranshi,ya debo kyawawan halayensu tsaf har da ma qari,sannu a hankali muhammadu ya girma aka hadashi aure da wata yarinyar wani malami maqocinsu mai suna naja'atu,cikin watanni tara kacal Allah ya albarkaceta ta haifi MUKHTAR baabaa prof,wanda ba'a jima da haihuwarsa ba Allah ya yiwa mai dabba rasuwa,ya rasu ya bar matarshi,bayan share makoki aka raba gado aka baiwa khadija matarsa da dansa muhammadun,ya karbi dukiyar mahaifinsa kuwa a sa'a don habaka tayi tayi,abu ya dinga dad gaba,saidai daga baya ya fuskanci kamar kiwon wahala ce kawai,ya saida shanun ya rage wasu daga ciki ya barwa mukhtar kyauta halak malak,yace shima ya taba aikin gado,dama can shi mai son kiwo ne,tare suke fita da shaqiqin abokinsa wanda tun yana da shekara daya a duniya baida aboki sama da SULAIMAN sule,babu abinda ke rabashi da sule,hatta bacci ma wani sa'i tare suke,musamman idan matar babanshi taso tsiyar tata,tausayinsa yake,qaunarsa yaje fusabilillah,mahaifiyarsa ta raau tun randa ta haifeshi ko waiwayowa batayi taga abinda ta haifa din bata yi ba,sai suka qulle sosai,muntari baida qani balle ya debe masa kewa,haka sule ma baida dan uwa sai hashimu,shi kuwa bai isa ya rabeshi ba don tuni altine ta shiga tsakaninsu ta raba zumuncin Allah qarfi da yaji,duk da hashimun na qaunar dan uwansa,tare suka dinga fita kiwo shi da sule,yayin da babansa muhammadu kuma ya soma saida zannuwa a cikin garin gwambe,dukkaninsu Allah ya sanya musu albarka baki dayansu,har mamakin yadda dabbobin muntarin keta habaka babansa muhammadu keyi,shida sule kiwo suke haiqan,duk da babu dabbar sulen ko daya a ciki amma sabida qaunar dake tsakaninsu wani lokaci a shike fitar ma muntarin da su,altine tayi dukan,tayi dukan don ta raba tsakninsu saboda yadda taga suke na samun kulawa a gidansu muntarin amma a banza wai man kare,saboda tare malam muhammadu ke musu komai,bai rasa ci ko sha ba balle sutura,ba'a rabasu a gidan sule dai dai yake da muntaru,data gama dukan zata kuma gansu tare,abun ya tsaya mata a rai,sai ta koma ziga gun babansa,to shi din ma baici nasarar rabasu din ba,saboda yadda qauyen aka soma zaginsa shi da matarsa kan yadda suka qwallafawa dan marayan Allahn.
Cikin haka turawa suka shigo qauyen nasu,suka kawo musu makarantar boko har cikin garin nasu,kowa ya tsame dansa yace babu shi a wannan batu,muntari na bala'in sha'awar karatun,ya samu babansa ya sanar masa kan ya sanyasu shi da sule,da fari shima yace sam kada muntarin ya sake wannan magana,bayan dogon nazari da malam muhammadun yayi sai ya amince,ya hadasu da sule ya kaisu amma yace saidai suyi jeka ka dawo(day),altine zani a hannu ta shaidawa mahaifin sule abinda malam mahammadu yayi,ai kuwa ya wanke qafa yaje har gida ya ciwa malam mahammadu mutunci,a lokacin sule na gidan tare da muntari,kuka ya dinga yi yana jan baban nasa kan ya daina zaginsa amma ya mangareshi ya qara gaba,tilas malam ya lallashi sule kan yayi haquri tunda babansa baya so,haka ya haqura ba don rai naso ba,ya ci gaba da fitar da shanun muntari kafin ya dawo daga makaranta sai ya taddashi a jeji suci gaba da kiwon tare da yammaci su dawo gida,malam muhammadu yace ya ya daina,ya bari idan muntarin ya dawo sa fita tare su dawo tare,amma sam yace a'a,ai shi da muntarin duka daya ne,duka a lokacin basu wuce shekara goma sha uku uku ba.
A haka shanun muntari suka sake yawa,ga cikakkiyar lafiya dake garesu,ganin haka ya sanya muntari ya shawarta da malam muhammadu zai raba dabbobin biyu ya baiwa sule rabi,saboda wahalar da yake da su ko shi sai haka,ba musu dukka suka amince har da mahaifiyarsa,randa ya sanar da sule cewa yayi bazai karba,shi don Allah don qauna da amincin dake tsakaninsu yake masa,tilas daga qarshe malam muhammadu ya tilas ta shi ya karba,godiya ya dinga musu harda hawaye,din suna da yawa baiyi tsammanin mallakar wani abun duniya kwatankwacin haka ba.