Sashe 76
Kundin Qaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Biyu da rabi bayan sumayya ta kammala sallar azahar tana tilawar qur'ani anty dije ta taddata da hijabi jikinta itama da alama bata jima da gama sallarta ba,gefe ta zauna hakan ya nunawa sumayya magana tazo yi da ita saboda haka tana kaiwa qarshen shafin ta rufe tayi addu'a ta shafa ta waiwayo ga anty dijen
"Ya ibada,ke kam azumi nasaj gwaninki ne,tunda kina na litinin da alhamis dama" murmushi tayi
"Wallahi kam anty"
"Allah ya kawo min sauqi wannan karon shi yasa nace bari nazo na sameki,kinsan duk watan azumi nike wa baabaa prof abinci har a kammala azumin,abban laila ne yasa a dinga yi saboda karamcin dattijon,yana son abinciccikan gargajiya duk da kasancewarsa dan boko,to su mutan gidan sun fishi boko,da azumi basa wani abincin azo a gani sai abinciccikan zamani,ummee ce ke masa lokaci lokaci don itama tana so,to wannan karon ummee sun tafi umra mazan ne kawai suka rage a gidan,duk da kowa na da mai aikinsa amma shima baabaan baison girkin ma'aikata shi danshi ya gado" ta fada tana dariya data tuno shi
"nasa gwanar girkin gargajiya ce ke,ni ki barni da girkin gida ki dinga na baabaa" murmushi tayi
"To ai zan iya ma anty duka,haba,sai kace ba mace ba"
"Nasan zaki iya,ai ranon mama ce,amma kya dai tayani na gidan"
"Tom anty" miqewa anty dijen tayi
"Naga yau garin kam masha Allah akwai hadari,ko yau zamu samu ruwan farko a ranar farko?"
"Allah yasa anty,dama tun muna kano naga irin garuruwan nan kunfi ko ina samun ruwa,ga damunarku itace qarshe wajen tafiya"
"Wallahi masha Allah,muna shan ruwa kam,saidai zafi"
"A hakan anty,duk wannan ac da kuke kwankwada"
"Saikin fita ai sumayya zakiji a jikinki"
"Saidai haka" ta miqe itama tana nannade abun sallahr ta don shiga kitchen saboda su kammala komai kan lokaci.
Ana la'asar kuwa ruwan farko ya soma sauka zuwa qasa,tana kitchen din a lokacin,sai ta zuge glass tana kallon yadda ruwan ke juqa shukoki yana tayar da qamshin qasa,a rayuwarta tana son damina,murmushi ya subuce mata data tuna sanda suna tare da mukhtar,duk sanda baya gida takan fito ita da yaranta dake tayata zama susha wankansu a ruwan sama,kafin ya dawo ta share gidan ya sauya kayanta kamar bata shiga ruwa ba,amma kallon farko idan ya mata yake gane ta shiga ruwa,musamman gashinta dake saurin fallasata saboda cikarsa da tsahonsa bai bushewa da wuri,abinka da quruciya a lokacin yaron da bai saba qarya ba idan yayi ma sai an ganeshi,sai ta fitittike tace masa wankan tsarki tayi
"Wanne wankan tsarkin,me ya sameki bayan fitata da zakiyi wankan tsarki?" Narai narai take da ido tace itadai wankan tsarki tayi a tunaninta shi kadai ne mafitar da zai yadda ba wasan ruwa tayi ba tunda wankan tsarki ne kadai ake jiqa kai idan za'ayi,idan yaga ta dage sai kawai ya qyalqyale da dariya ita kuwa ta sake hade rai don kada ya gano,tilas yake sakin murmushi yace ya yadda,tana kawowa nan a tunaninta ta saki itama murmushin qwalla na bin kuncinta
"Allah ya gafarta maka ya mukhtar,ya kyauta makwancinka" tayi furucin tana goge hawayen da tafin hannunta,baki daya sai walwalarta ta tafi kamar yadda hakan ke faruwa yawancin lokuta idan ta tunashi,girkin take amma zuciyarta babu dadi,duk da haka hakan bai hanata hanzari ha,kafin kace me wannan ta gama girkin baabaa prof,dashishi ta masa da miyar ganye,wanda kallonta kadai ya isa ya tsinkar maka da yawu,tun ba yau ba tun tana qaramarta haka hannunta yake da iya sanwa,ballantana a shekaru takwas zuwa tara da tayi gidan aure ya sake maida ta gwana fagen iya girki.
Ko da anty dije tazo tayi mamakin saurin girkinta,don tuni suma ta musu miya,miyar qwaice da alayyahu tayi shar tayi kyau sosao,gun any dijen ta koya amma sai take ganin kamar ta fita ma iyawa,kasancewar sumayya bai bala'in qwaqwalwa da saurin dauke abu,cewa tayi ta bar mata sauran ta qarasa tunda tayi kusan rabin aikin gidan bayan na baabaan.
Daki ta shiga tayi wanka,saura kusan awa guda kafin a sha ruwa,ta fito ta shirya kanta cikin atamfa riga da zani,kanta ta daure da dan kwali ta dauki carbinta ta fito falo,dariya ta zo mata ganin yadda laila ta sake bajewa saman kujera,khalipha kuwa tuni bacci yayi awan gaba da shi,bata ce musu komai ba ta sauya tasha zuwa sunna t.v wanda suka sako tafsirij shehun malaminta sheik Ali ibrahim isah fantami,sosai take jin dadin tafsir din har zuwa wani lokaci data koma kitchen din ta tadda anty dije ta kammala komai,ita ta dinga kwaso kayan tana shiryawa saman dining anty dije kuma ta shiga wanka ganin saura mintuna akira sallah.
Lokaci qalilan gidan ya kacame,kowa na kaiwa baki,daga nan uncle farouq ya kada kansu zuwa masallaci sukayi sallar magariba.
Babu kowa gidan duka sun fita sallar asham tarawih,ta sanya hijabinta zata tada tata kenan cikin gidan anty dije ta shigo itama sanye da hijabi
"Sumayya,yanzu abban laila ya kirani,yace ki miqa abincin baabaa prof,ga driver nan yana waje zai amshi nashi abinci sai ya riqe miki wasu kwanukan" babu musu yau kam sai faduwar gaba jin an ambacin gidan tace to,dirvan nasu shi ya dauki kwandon ita kuma ta dauki flask daya da ya rage.
Tana gaba yana binta a baya har suka isa bakin qofar,a mutunce suka gaisa da baba harunaya bude mata qaramar qofar suka shiga,harabar gidan tarwai take da haske da fararen qwai,ko ina a haskake tamkar rana,ma'aikatan gidan sanye da unifoarm nata kaikawo kowa na aikinsa,grass carfet da shukokin dake jere a tsare sun samu ruwan sama sunyi kyau gwanin sha'awa,kamar yadda garin yayi dadi,iska mai dadi mai cakude da qamshin qasa na kadawa,sai ta dinga jin wani mishadi na shigarta,tana shaqar iskar tana mata dadi har cikin qirjinta,ta dinga takawa a hankali har zuwa tsakiyar harabar gidan,su biyu ta fara hangowa tsaye da alama magana suke kamar rannan,mahmoud din kawai ta iya ganewa saboda shike fuskantar qofar shigowar,kamar wancan karon dai dayan na fuskantar mahmoud sai bayansa kawai ta iya hangowa,yana sanye da jallabiya ta maza fara sol da silifas farare a qafarsa,hannunshi riqe da dadduma,tana gab da isa garesu ya juya ya shige ta wata qofa da zata iya sadashi da waje,yayin da mahmoud har ya juya sai ya hangeta,tsayawa yayi yana murmushi har ta qaraso,hanmunsa ya miqa zai amshi flask din hannunta yana fadin
"Bisa alamu abincin baabaa ne" murmushin itama tayi tana miqa masa
"Eh shine"
"Masha Allah,a gaida umman khalipha" sai ya dubi drivan yana miqa masa hannunshi alamar ya bashi ,rusunawa yayi cikin girmamawa ya miqa masan sannan ya juya zuwa qofar fitan,dubanta yayi
"Muje nayi sauri na rakaki kada liman ya tada salla na rasa wata raka'ar,don na tabbata ya isa masallaci saura minti biyar a tayar" dan baya ta ja kadan
"Ai ba sai na shiga ba ma,ina cewa ma duka masu gidan basa nan,ka kaima baaban kawai kace ina gaidashi" murmushi yayi
"Kamar ya sanki,na tabbata baki taba zuwa kin gaidashi ba,sannan ko ba kowa a gidan su anty farida da sauran yara na nan" murmushi ta sake yi
"Zanzo na gida baabaa in sha Allah,su anty farida kuwa ka gaishesu na tabbata suma basu sanni ba,amma kace ina gaishesu,nima sallah zanje nayi"
"Is ok,ki yiwa umman khaliphan sannu"
"Zata ji" ta fada tana juyawa a hankali ta fice daga gidan.
Tana shiga ta isarwa anty dije saqon,sannan ta shige dakinta,da hanzari ta tada isha jin an fara kiran sallar tarawih don sun gama isharsu,cak ta tsaya lokacin da limamin ya fara karanta fatiha,daina aiki qwaqwalwarta tayi na wucin gadi,babu abinda kunnuwanta ke ji sai karatun dake fitowa daga lasifiqar yana karade unguwar kasancewar masallacin na daura sa su ne,muryar da bazata iya mancewa da ita ba komai tsawon zamani,komai sauyawar yanayi,komai dadi komai wuya,muryar MUKHTAR dinta take ji tana karade kunnuwanta,wani irin faduwa gabanta ya dinga yi har ya haifarwa da gabban jikinta yin sanyi,tana so ta zauna amma ta kasa,jin kunnuwanta take kamar zasu zaunce,hannunta ta sanya ta toshe kunnen nata ko zata daina jin amsa kuwwar karatun amma hakan ya gagara,kanta ta shiga girgizawa
"A'ah,ba mukhtar bane,wanda ya mutu baya dawowa" ta fada tana ci gaba da girgiza kanta hawaye na shirin soma sauko mata,a sukwane ta juya ta fito zuwa falon gidan ba tare da tasan me zata aiwatar ba.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣9⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*KO KUNSAN RANAR QIYAMA ANA DAURE DAN WUTA DA SARQA MAI TSAHON ZIRA'I SAB'IN KAFIN A JASHI ZUWA JAHANNAMA*
*Astagfirullah wa'atubu ilaih*
___________________________________
Birki ta ja a falon zuciyarta na wata iriyar bugawa,idanu ta shiga rarrabawa qwaqwalwarta ta daure tamau,muryar na ci gaba da ratsa kunnuwanta cikin daddadan sautin karatun mai qunshe da muryar mukhtar,me zata aikata?,abinda ta kasa baiwa kanta amsa kenan
"Ya mukhtar,ya mukhtar" ta soma fada hawaye na zubo mata,shigowar laila a guje wadda fitsari ya korota daga wajen sallar ya dawo da ita hayyacinta,bata jirayi qarasowar lailan ba ta isa gareta ta riqe kafadarta
"Laila,wake karatun sallah a masallaci?,mukhtar ne?"dariya ta saki tana kallonta tare da yin tsalle alamar fitsarin ya matseta
"A'ah,yaya ne fa,duk azumi shi yake jan sallah" ta fada tana zillewa ta ruga bandaki,sam bata fuskanci bayanin laila ban ta ji anty dije na cewa
"Shike limanci fa,nan da goman qarshe zai tafi a saudiyya yake sallah sai dai malam usman ya qarasa" firgigit tayi tana duban anty dije,sai ta kada kai kawai ta juya jiki a sanyaye zuwa cikin dakin nata ba tare da ta furta komai ba,zama tayi bakin gado tana jingina da jikin gadon,tamkar wadda aka zarewa laka,ta kasa kowanne irin tunani,muryar ce kawai ke ratsa dodon kunnenta tana mata shawagi,runtse idanunta tayi ta koma ta kwanta a gefan hannun damanta,wani abu take ji yana yana zagaya kanta kamar ana yamutsa qwaqwalwarta,haka hawaye yaci gaba da tsiyaya ta gefan idanuwanta.
"Ya ibada,ke kam azumi nasaj gwaninki ne,tunda kina na litinin da alhamis dama" murmushi tayi
"Wallahi kam anty"
"Allah ya kawo min sauqi wannan karon shi yasa nace bari nazo na sameki,kinsan duk watan azumi nike wa baabaa prof abinci har a kammala azumin,abban laila ne yasa a dinga yi saboda karamcin dattijon,yana son abinciccikan gargajiya duk da kasancewarsa dan boko,to su mutan gidan sun fishi boko,da azumi basa wani abincin azo a gani sai abinciccikan zamani,ummee ce ke masa lokaci lokaci don itama tana so,to wannan karon ummee sun tafi umra mazan ne kawai suka rage a gidan,duk da kowa na da mai aikinsa amma shima baabaan baison girkin ma'aikata shi danshi ya gado" ta fada tana dariya data tuno shi
"nasa gwanar girkin gargajiya ce ke,ni ki barni da girkin gida ki dinga na baabaa" murmushi tayi
"To ai zan iya ma anty duka,haba,sai kace ba mace ba"
"Nasan zaki iya,ai ranon mama ce,amma kya dai tayani na gidan"
"Tom anty" miqewa anty dijen tayi
"Naga yau garin kam masha Allah akwai hadari,ko yau zamu samu ruwan farko a ranar farko?"
"Allah yasa anty,dama tun muna kano naga irin garuruwan nan kunfi ko ina samun ruwa,ga damunarku itace qarshe wajen tafiya"
"Wallahi masha Allah,muna shan ruwa kam,saidai zafi"
"A hakan anty,duk wannan ac da kuke kwankwada"
"Saikin fita ai sumayya zakiji a jikinki"
"Saidai haka" ta miqe itama tana nannade abun sallahr ta don shiga kitchen saboda su kammala komai kan lokaci.
Ana la'asar kuwa ruwan farko ya soma sauka zuwa qasa,tana kitchen din a lokacin,sai ta zuge glass tana kallon yadda ruwan ke juqa shukoki yana tayar da qamshin qasa,a rayuwarta tana son damina,murmushi ya subuce mata data tuna sanda suna tare da mukhtar,duk sanda baya gida takan fito ita da yaranta dake tayata zama susha wankansu a ruwan sama,kafin ya dawo ta share gidan ya sauya kayanta kamar bata shiga ruwa ba,amma kallon farko idan ya mata yake gane ta shiga ruwa,musamman gashinta dake saurin fallasata saboda cikarsa da tsahonsa bai bushewa da wuri,abinka da quruciya a lokacin yaron da bai saba qarya ba idan yayi ma sai an ganeshi,sai ta fitittike tace masa wankan tsarki tayi
"Wanne wankan tsarkin,me ya sameki bayan fitata da zakiyi wankan tsarki?" Narai narai take da ido tace itadai wankan tsarki tayi a tunaninta shi kadai ne mafitar da zai yadda ba wasan ruwa tayi ba tunda wankan tsarki ne kadai ake jiqa kai idan za'ayi,idan yaga ta dage sai kawai ya qyalqyale da dariya ita kuwa ta sake hade rai don kada ya gano,tilas yake sakin murmushi yace ya yadda,tana kawowa nan a tunaninta ta saki itama murmushin qwalla na bin kuncinta
"Allah ya gafarta maka ya mukhtar,ya kyauta makwancinka" tayi furucin tana goge hawayen da tafin hannunta,baki daya sai walwalarta ta tafi kamar yadda hakan ke faruwa yawancin lokuta idan ta tunashi,girkin take amma zuciyarta babu dadi,duk da haka hakan bai hanata hanzari ha,kafin kace me wannan ta gama girkin baabaa prof,dashishi ta masa da miyar ganye,wanda kallonta kadai ya isa ya tsinkar maka da yawu,tun ba yau ba tun tana qaramarta haka hannunta yake da iya sanwa,ballantana a shekaru takwas zuwa tara da tayi gidan aure ya sake maida ta gwana fagen iya girki.
Ko da anty dije tazo tayi mamakin saurin girkinta,don tuni suma ta musu miya,miyar qwaice da alayyahu tayi shar tayi kyau sosao,gun any dijen ta koya amma sai take ganin kamar ta fita ma iyawa,kasancewar sumayya bai bala'in qwaqwalwa da saurin dauke abu,cewa tayi ta bar mata sauran ta qarasa tunda tayi kusan rabin aikin gidan bayan na baabaan.
Daki ta shiga tayi wanka,saura kusan awa guda kafin a sha ruwa,ta fito ta shirya kanta cikin atamfa riga da zani,kanta ta daure da dan kwali ta dauki carbinta ta fito falo,dariya ta zo mata ganin yadda laila ta sake bajewa saman kujera,khalipha kuwa tuni bacci yayi awan gaba da shi,bata ce musu komai ba ta sauya tasha zuwa sunna t.v wanda suka sako tafsirij shehun malaminta sheik Ali ibrahim isah fantami,sosai take jin dadin tafsir din har zuwa wani lokaci data koma kitchen din ta tadda anty dije ta kammala komai,ita ta dinga kwaso kayan tana shiryawa saman dining anty dije kuma ta shiga wanka ganin saura mintuna akira sallah.
Lokaci qalilan gidan ya kacame,kowa na kaiwa baki,daga nan uncle farouq ya kada kansu zuwa masallaci sukayi sallar magariba.
Babu kowa gidan duka sun fita sallar asham tarawih,ta sanya hijabinta zata tada tata kenan cikin gidan anty dije ta shigo itama sanye da hijabi
"Sumayya,yanzu abban laila ya kirani,yace ki miqa abincin baabaa prof,ga driver nan yana waje zai amshi nashi abinci sai ya riqe miki wasu kwanukan" babu musu yau kam sai faduwar gaba jin an ambacin gidan tace to,dirvan nasu shi ya dauki kwandon ita kuma ta dauki flask daya da ya rage.
Tana gaba yana binta a baya har suka isa bakin qofar,a mutunce suka gaisa da baba harunaya bude mata qaramar qofar suka shiga,harabar gidan tarwai take da haske da fararen qwai,ko ina a haskake tamkar rana,ma'aikatan gidan sanye da unifoarm nata kaikawo kowa na aikinsa,grass carfet da shukokin dake jere a tsare sun samu ruwan sama sunyi kyau gwanin sha'awa,kamar yadda garin yayi dadi,iska mai dadi mai cakude da qamshin qasa na kadawa,sai ta dinga jin wani mishadi na shigarta,tana shaqar iskar tana mata dadi har cikin qirjinta,ta dinga takawa a hankali har zuwa tsakiyar harabar gidan,su biyu ta fara hangowa tsaye da alama magana suke kamar rannan,mahmoud din kawai ta iya ganewa saboda shike fuskantar qofar shigowar,kamar wancan karon dai dayan na fuskantar mahmoud sai bayansa kawai ta iya hangowa,yana sanye da jallabiya ta maza fara sol da silifas farare a qafarsa,hannunshi riqe da dadduma,tana gab da isa garesu ya juya ya shige ta wata qofa da zata iya sadashi da waje,yayin da mahmoud har ya juya sai ya hangeta,tsayawa yayi yana murmushi har ta qaraso,hanmunsa ya miqa zai amshi flask din hannunta yana fadin
"Bisa alamu abincin baabaa ne" murmushin itama tayi tana miqa masa
"Eh shine"
"Masha Allah,a gaida umman khalipha" sai ya dubi drivan yana miqa masa hannunshi alamar ya bashi ,rusunawa yayi cikin girmamawa ya miqa masan sannan ya juya zuwa qofar fitan,dubanta yayi
"Muje nayi sauri na rakaki kada liman ya tada salla na rasa wata raka'ar,don na tabbata ya isa masallaci saura minti biyar a tayar" dan baya ta ja kadan
"Ai ba sai na shiga ba ma,ina cewa ma duka masu gidan basa nan,ka kaima baaban kawai kace ina gaidashi" murmushi yayi
"Kamar ya sanki,na tabbata baki taba zuwa kin gaidashi ba,sannan ko ba kowa a gidan su anty farida da sauran yara na nan" murmushi ta sake yi
"Zanzo na gida baabaa in sha Allah,su anty farida kuwa ka gaishesu na tabbata suma basu sanni ba,amma kace ina gaishesu,nima sallah zanje nayi"
"Is ok,ki yiwa umman khaliphan sannu"
"Zata ji" ta fada tana juyawa a hankali ta fice daga gidan.
Tana shiga ta isarwa anty dije saqon,sannan ta shige dakinta,da hanzari ta tada isha jin an fara kiran sallar tarawih don sun gama isharsu,cak ta tsaya lokacin da limamin ya fara karanta fatiha,daina aiki qwaqwalwarta tayi na wucin gadi,babu abinda kunnuwanta ke ji sai karatun dake fitowa daga lasifiqar yana karade unguwar kasancewar masallacin na daura sa su ne,muryar da bazata iya mancewa da ita ba komai tsawon zamani,komai sauyawar yanayi,komai dadi komai wuya,muryar MUKHTAR dinta take ji tana karade kunnuwanta,wani irin faduwa gabanta ya dinga yi har ya haifarwa da gabban jikinta yin sanyi,tana so ta zauna amma ta kasa,jin kunnuwanta take kamar zasu zaunce,hannunta ta sanya ta toshe kunnen nata ko zata daina jin amsa kuwwar karatun amma hakan ya gagara,kanta ta shiga girgizawa
"A'ah,ba mukhtar bane,wanda ya mutu baya dawowa" ta fada tana ci gaba da girgiza kanta hawaye na shirin soma sauko mata,a sukwane ta juya ta fito zuwa falon gidan ba tare da tasan me zata aiwatar ba.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣9⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*KO KUNSAN RANAR QIYAMA ANA DAURE DAN WUTA DA SARQA MAI TSAHON ZIRA'I SAB'IN KAFIN A JASHI ZUWA JAHANNAMA*
*Astagfirullah wa'atubu ilaih*
___________________________________
Birki ta ja a falon zuciyarta na wata iriyar bugawa,idanu ta shiga rarrabawa qwaqwalwarta ta daure tamau,muryar na ci gaba da ratsa kunnuwanta cikin daddadan sautin karatun mai qunshe da muryar mukhtar,me zata aikata?,abinda ta kasa baiwa kanta amsa kenan
"Ya mukhtar,ya mukhtar" ta soma fada hawaye na zubo mata,shigowar laila a guje wadda fitsari ya korota daga wajen sallar ya dawo da ita hayyacinta,bata jirayi qarasowar lailan ba ta isa gareta ta riqe kafadarta
"Laila,wake karatun sallah a masallaci?,mukhtar ne?"dariya ta saki tana kallonta tare da yin tsalle alamar fitsarin ya matseta
"A'ah,yaya ne fa,duk azumi shi yake jan sallah" ta fada tana zillewa ta ruga bandaki,sam bata fuskanci bayanin laila ban ta ji anty dije na cewa
"Shike limanci fa,nan da goman qarshe zai tafi a saudiyya yake sallah sai dai malam usman ya qarasa" firgigit tayi tana duban anty dije,sai ta kada kai kawai ta juya jiki a sanyaye zuwa cikin dakin nata ba tare da ta furta komai ba,zama tayi bakin gado tana jingina da jikin gadon,tamkar wadda aka zarewa laka,ta kasa kowanne irin tunani,muryar ce kawai ke ratsa dodon kunnenta tana mata shawagi,runtse idanunta tayi ta koma ta kwanta a gefan hannun damanta,wani abu take ji yana yana zagaya kanta kamar ana yamutsa qwaqwalwarta,haka hawaye yaci gaba da tsiyaya ta gefan idanuwanta.