Sashe 149
Imaan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru Mujaheed yyi yana kallonta, can ya karasa kusa da ita yace "Saboda me baxa ki ci ba?" Kin cewa komai tayi, yyi murmushi ya xauna kusa da ita ya jawo cup da flask ya fara hada shayin, yana gamawa ya ajiye cup din shayin gabanta da plate din dankali, dauke kai tayi xata mike ya rikota, ta shiga kokarin kwace kanta tana cewa "Nace maka ni ba yunwa...." muryar Inna suka ji tace "Lafiya?? meye haka??" Saketa Mujaheed yyi da sauri, Inna na xaro ido tace "Lafiya kake matse yar mutane Mujaheed?" Ta gefen ido ya kalleta bai dai ce komai ba, Inna ta kalli Imaan tace "Me kika masa?" Kamar xata yi kuka tace "Inna nace masa na koshi fa shine wai sai na ci" Inna ta bude ido sosai tace "A'a toh ke kuma baki da tsoron Allah, kika koshi a Ina? Uban me kika ci? Bata fa karya ba Mujaheed... Ni dai ba ruwana, ka rabu da ita ka kada min nawa shayin in sha, ya wuce Allah ya masu hisabi da hanjin cikin nata" Murmushi kawai Mujaheed yake ya gama hada ma Inna shayin ya ajiye gabanta ya debar mata dankalin ta sakko kasa tace "Toh burodi fa?" Yace "Bari in fita in siyo yanxu" Inna tace "Atoh, na taba ganin inda aka sha shayi ba burodi dama" mikewa yayi ya fita parlon Inna ta bi sa da kallo ta rike ha6a tace "Ikon Allah, aure mai saita mutum ya gyara sa, dubi fa wani biyayya na musamman da Mujaheed yake yi yanxu daga ya kwana daki daya da mace, Ikon Allah ya fi gaban haka.... Mujaheed ne xan aika da ya tafi babu musu?? Lallai kamar Rukayya ta tsine masa, ai baxai ma je bane sai ya gama ja min rai ya gama min walakanci, ke ma dai Bulasawa yayi yayi ya yunkuro ayi auren nan ko kya yi hankalin, kinsan fa da ace ke ce kika yi aure da har na gama tarewa can gidan naki, toh wai yaushe ne wannan kaddararren jarabawan sakandarin ne ni patuu, wllh su Ahmadu da Bukar dama can basa tsoron Allah tun tasowarsu kamar dai ba ni na haifesu, Banda haka wani shegen jarabawa ne ya isa ya hana sunnar manzon Allah S.A.W.... Ni dai ba ruwana" Imaan dai bata tanka Inna ba sai fiffita shayin da Mujaheed ya hada mata take ta sha da sauri kafin ya dawo, Inna ta saki baki tana kallonta da sauri tace "Ya haka xa ki handame dankalin gaba daya Imaan, ba namu bane mu biyu" sosai ta ba Imaan da ta cika baki da dankali da kwai dariya, ko sauraranta bata yi ba ta dinga turawa har sai da ta ci kusan rabin plate din da kwai, Inna dai sai kallonta take baki bude, Imaan ta dau wani cup ta dinga fiffita shayin har ya huce ta kwankwade da sauri ta ajiye kusa da Inna tana goge bakinta, Inna ta rufe bakin da ta sake tace "Kunyar Mujaheed din kike yanxu ko me?" Da sauri Imaan tace "Kunya Kuma??? Ni dai kar ma ki ce masa na ci komai a nan, don ba abinda na ci" Bata jira cewar Inna ba ta koma kujera ta xauna tana goge bakinta da kyau, Inna tace "Dama mana, ya xa ayi ki iya cin rabin plate din dankali kamar jaka ai sai dai ni din..." Imaan dai bata kulata ba ta mayar da hankalinta kan Tv, Da sallama Mujaheed ya shigo parlon rike da ledan bread l, ya karaso ciki yana kallon empty cup din shayin da ya hada kafin ya fita, Imaan ta wani daure fuska tana kallon TV, Inna tace "Toh ba kya daure fuska ba dama kin handame komai kamar mayunwaciya, wllh Mujaheed yanda ka san ta shekara bata ci abinci ba, dubi abinda ta bar min fisabilillahi, ko mage aka bar ma wannan xata koshi balle mutum irina, yarinya dai sai ci kamar saniya" Imaan sai kallon Inna take kamar xata yi kuka, Mujaheed dai yayi murmushi ya ajiye bread din hannunsa yace "Toh tunda dai ba da kudin ki aka siyo kayan abincin ba kuma ba Amadun ki ko Bukar suka siyo ba me xai dameki? Gidan yayanta ne fa" Bai jira cewarta ba ya wuce sama, imaan ta dinga kallonta tana murmushi ranta fess, tabe baki Inna tayi ta bude bread din ta yagi kato a ciki a hankali tace "Toh da ban haifesu ba xa su haife ku?? da na sani ma in ki haifan nasu in ga ta tsiya, sai in ga ta yanda xa a same ku gantalallu kawai marasu tarbiya" sakkowa kasa imaan tayi ta dinga 6a66aka dariya, ita dai Inna bata ko kalleta ba ta tsuke fuska tana cin bread. Sai da tayi nakk dama ta mike ta kai plate da cup kitchen duk ta wanke duk abinda aka bata ta kife ruwan ya tsane sannan aka fara goge gogen kitchen din har wall din kitchen dai sai da ta goge sannan ta fito ta share parlorn tasss, sannan aka fara goge goge, tana goge sabbin kujerun da d'an kyallen da take goge goge tace "Babu wanda xai ce datti baxai fito daga parlon nan ba, kaii aji tsoron datti, datti ba kyau...." Ita dai Imaan kallonta kawai take, Inna ta gama goge goge ta wuce dakin su Hansai ta kwanta saman gado, nan ta dinga sharar bacci uwa tana dakinta. Sha daya da kusan rabi Mujaheed ya sakko parlon sanye da kananun kaya da suka amshe sa sosai, ya dinga kallon Imaan yana tsaye kusa da stairs, can yace "Ina Innar" ba tare da ta kallesa ba tace "Nima ban sani ba" juyawa yyi yana kallon Safeenah dake sakkowa a bayansa kamar mai tausayin stairs din, riga da skirt ne jikinta na atamfa da suka amsheta matuka, kayan ya haska ta ba kadan ba, she's really beauty.... fuskarta babu walwala har ta karasa sakkowa, tunda suka hada ido sau daya Imaan ta dauke kanta ta wani tamke fuska, ita ma Safeenar haka tayi tana jin wani mugun tsanar imaan har xuciyarta, Mujaheed ya karasa ya bude dakin dake downstairs yana kallon ciki, ganin Inna na bacci ya rufe ya dawo yana kallon Safeenah da fuskarta ke dauri tana kallon direction daban yace "She is sleeping" kamar jira take ta Juya da sauri ta koma sama, kallon Imaan yyi sai kuma ya bi bayanta, Imaan ta mike a hankali ta tafi dakin da Inna ke kwance ta bude jakarta ta dau dari biyar da ta gani a ciki ta rufe jakar sannan ta fito, kofa ta nufa direct ta fita parlon tana murguda baki, Mai gadi ya tashi ya bude mata gate tayi ficewarta tana ce masa sai anjima yayi mata Allah ya kiyaye, tana isa babban titi ta samu adaidaita ta shiga ta gaya masa anguwarsu. Safeenah na shiga bedroom dinta Mujaheed ma ya shigo ya rufe kofar ya juya yana kallonta yace "Toh girkin fa...." Xaunawa tayi gefen gado tana cire dankwalin kanta dogon gashin ya sauka kasa, a d'an fusace tace "Toh wai ba cewa kayi tana bacci ba, and you brought the idea of asking her first before cooking, plss Mujaheed let me... Sannan gaskiya kada yarinyar nan ta sake xuwa min gidana daga yau, am sorry to say this wllh I dislike her with passion, I don't know why amma gaba daya naji na tsaneta with all my heart" Kallonta Mujaheed ya dinga yi da wani expression, fuska daure yace "You are looking into my face and telling me u dislike my blood, are you on ur right senses Safeenah??? meye damuwar ki da ita, to bari ki ji, ba ki isa ki hana imaan shigowa gidan nan ba tunda ba gidan ki bane.... Kuma ki sakko yanxu ki girka ma grandmum dita lunch" a mugun fusace tace "It's better ka fita ka tafi eatry ka samo masu lunch don wllh wlh baxan yi ba, Banda hauka ma ni na taba jin inda ake tilasta amarya sai ta yi girki on her third day a gidan miji, to baxan yi ba, ka fita ka siyo masu ko kasa blood din taka ta girka" tana kai wa nan ta mike a fusace ta tafi can karshen gado ta xauna, shi dai kallonta kawai yake trying hard to control his temper, underneath his breathe yace "I will treat ur f**kup soon" daga haka ya fice daga dakin, ta bi sa da harara murya can kasa tace "Xaka san blood din ka ce" Mujaheed na sauka downstairs ganin Imaan bata parlor ya tafi kitchen nan ma bai ganta ba, dakin da inna ke kwance ya shiga nan ma bai ganta ba, Inna ta d'an bude ido cikin muryar bacci tace "Azahar yayi Mujaheed?" Yace "Imaan fa?" A firgice ta mike xaune tace "Wacece kuma Imaan" bai ce komai ba ya fito dakin ya tafi compound nan ma bai ga alamanta ba, juyowa yayi da mamaki xai dawo parlor ya kusa cin karo da Inna tana xaro ido tace "Ina take?" Yace "Yanxu na sakko ban ganta ba" salati Inna ta saki ta fashe da kuka tace "Ai ni na shiga uku daga fito da yar mutane ta min rakiya ta 6ata, toh Ina ta shiga Mujaheed, ka rufa min asiri ita kenan Allah ya ba Bukar, har a koma ga Allah Bukar baxai taba yafe min ba wllh, ka cece rayuwata Mujaheed a nemo ta" Wani kallo Mujaheed ya dinga yi mata ta bangajesa ta nufi gun mai gadi da gudu tana hawaye tace "Yaro wata yarinya fara yar doguwa siririya kamar xata karye ta fita ta get din nan daxu??" Mai gadi yace "Ehh ta fita, har ma mun yi sallama" Inna ta saki wani dogon salati a rude tana tafe hannu tace "Amma kai d'an banxa ne sakarai gantalalle, ya xaka bar yarinya ta fita bayan tare kaga muka shigo, ita kenan fa gun uban a duniya, mutane dai ba tsoron Allah, ya bar yar mutane ta fita ta shiga gari, yanxu ta ina xan fara nemo Imaan ni patuu, ya ubangijina ka dubeni....." fashewa tayi da kuka ta fice daga gate din da gudu ko Hijabi babu, Mujaheed dai ya koma ciki ya dauko makullin mota ya