Sashe 96
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Hajiya tace kar na koreki, yanzu ko kin min laifi bana da halin korarki tun da Hajiya ta shiga tsakani, kin shiga ranta sosai kusan kullum zancen ki muke.....”
Na yi murmushi ina murza yatsun hannuna, yatsun nawa ya kalla sannan ya kalli fuskata kamin ya juya zuwa gurin teburinsa.
“Na gode”
Daga can inda yake tsaye ya dago ya kai ya kalleni.
“Da me?”
“Da komai da komai, na gode Allah ya saka da alheri”
“Amin Allah ya bamu hakuri we almost sharing the same journey, yanzu kin fahimci yadda rashin mahaifi yake kamar ni, gashi kece babba duk wanda zai miki magana zai ce ki yi kokarin hada kan yan'uwanki right”
Ya karasa yana murmushi kamin ya cigaba.
“Haka akai ta min sai nake jin kamar an dora min wani nauyi akai, na rika ganin kamar ba gaske ba ne, ina ta ganin kamar idan na shiga gida zan ga Abbah, idan na kalli Hajiya ta bani tausayi haka ma Siyama, yanzu da nai hakuri na dauki nauyin sai abun ya zo kin da sauki, amman fa har yanzu Hajiyata bata yarda na girma ba, idan zan fita zata bani time din dawowa idan na dade zata kirani tace na dawo dare yayi ko rana, babban mutum kamar ni”
Daga ni har shi murmushi muke sai ya tako ya karaso kusa da ni ya miko min tissue, ashe ya lura da hawayen da suka taru a idona.
“Miyasa ba ki koma gurin Doc ba?”
Na yi shiru ban ce komai ba, be kuma be fasa kallona ba, can kuma ya karasa ya dauki wayarsa ya taba sannan ya kalleni.
“Zaki iya zuwa office dinki”
“Na gode”
Na fada sannan na juya na fito daga office dinsa na nufi nawa office din, ko da na shiga matar bata nan, sai na suke jakata na zauna a kujerar ina ta tunanin mahaifina.
Ban yi aikin kamar yadda na saba ba, domin rashin kowa a kusa da ni sai ya kara saka ni cikin damuwa da tunani kala kala ciki har da na rayuwata da kuma Kabir ko yana ina ma yanzu Allah masani.
Misalin biyu da rabi Ahmad ya shigo office dina ganinsa yasa na tashi tsaye.
“Wata takardar nake nema, ta green light company”
A take na fara duba takardun da suke gaban teburin sai kuma nai arba da ita.
“Takardun da kika san zan yi amfani da su ki rika kai min ko kuma ki bawa sakatarena”
“Okay In-Sha-Allah zan kiyaye”
Har na mika masa takardar ya juya nace.
“Ranka ya dade ina son tambaya”
Juyowa yai yana kallona.
“Dan Allah Kabir nake tambaya, wani mahaukaci wanda ya makure ni ka”
Murmushi yai.
“Mutumen da kika ja min ya naushe ni ido kenan”
Nima murmushin nai.
“Kina son ganinsa ne?”
“Eh tun ranar ban sake ganinsa ba”
“Na saka a dauke ke shi ne akai shi gidan mahaukata”
Na ji ba dadi har hakan ya kasa boyu a a fuskata, sai kallonsa nake na rasa abunda zan ce masa. Dawowa yai gaban teburin nawa ya tsaya yana kallona.
“Karki damu, ina son ki samu natsuwa ne sai mu fara processing din nema masa lafiya, tun da naga ciwonsw ya dame ki”
Da sauri na mike tsaye baki sake ina zaro ido.
“Da gaske?”
“Da karya”
Ita ce amsar daya bani ya juya ya fice daga office din yana murmushi.
__________________
Assalamu Alaikum.
Ban yi niyar cewa komai akan littafin nan ba, duk kuwa da irin comments din da nake gani musamman whatsapp, wasu na complain abunda nake ma Halima yayi yawa so so this and that, akwai ma wacce tace min tana kwankwanton imani akan irin halin da nake saka Halima, na ji zafin maganar amman nai mata uzuri saboda ina daukar tana cikin irin mutanen da ke karatu basa daukar darasi burinsu kawai a samu nishadi.
Ina son ku sani idan ma baku sanin ba, idan kuma kun manta na tuna muku tun farkon fara labarin nan sai da na fada cewar ban sani ba ko zai muku dadi ba labari ne na soyayya ba kamar yadda aka saba, labari ne na fadi tashin rayuwa, kalubalen rayuwar da na aure wanda zai tabo wani bangare na rayuwarmu ta yau da kullum.
Duk yadda kike jin dadi Wallahi baki kamo wata ko a farce da jindadi ba, haka duk yadda kika a cikin tsanani baki kai kan akaifar wata shiga kunci rayuwa ba, labarin nan kirkiren labari ne amman ni nasan ba za a rasa wandanda suke rayuwa irin ta Halima ba, domin na ci karo da wasu a lokacin da nake rubutun nan, wani jarabarwarsa kadan ne wani da yawa, kuma kowa da inda Allah yake jarrabarsa. Idan baki cikin matsala wata na ciki, kuma ban cilastawa kowa karantawa ba sai wanda yaji yana ra'ayi, dan haka dan Allah kar wacce ta sake yi min wata magana marar dadi akan rayuwar Halimatu, duk wanda ya sake fada min rashin arziki goma billahil azeem zan fada masa ashiri, ba dole sai rai na so.
And wandanda suka tuna mahaifansu jiya, wasu har da kuka, ina addu'ar Allah ya jikansu, mu kuma ya sa mu cika da imani.
Ameen thumma Ameen.
7/21/21, 10:47 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
4️⃣8️⃣
Tun daga yanayin tafiyata zaka fahimci ina cikin wani irin nishadi marar misaltuwa, na fito daga cikin gidan na nufo inda motar Ahmad take fake ya sauke gilashin motar yana kallona har na karaso, da kansa ya miko hannunsa ya bude min motar, na shiga ciki na zauna ina gyara jakata. Sai yai motar key muka hau titi sannan ya kalleni.
“Happy?”
Na gyada masa kai idanuwana suna kokarin cika da hawayen jindadi.
“Yes”
Sai yai kyakkyawan murmushin daya karawa fuskarsa kyau.
“Thank You”
“No thank you da kika amince, hop dai kin fada musu ke za ki yi ba ni ba”
Na yi shiru ina kallon gorar ruwan daya dauka zai sha.
“Sun jidadi sosai, kuma sun yi supporting”
Murmushi kawai yai ya kalle ya karasa kurbe ragowar ruwan, ba mu yi wata tafiya mai nisa ba ya faka gefen titi yana kallona.
“Bari na karbo ruwa shagon can, bana iya zama ba ruwa a mota”
Bude motar yai ya fita, da wani irin kallo na bishi na jindadin daukar nauyin duba lafiyar Kabir da yai, haka Allah yake lamarinsa idan ya zo taimaka maka sai ya maka hanyar samun abun ko ta ta silar wani ne, and farincikin dana gani a fuskar yan'uwan Kabir a yau da naje musu da labarin ya kara faranta min rai fiye da kima. Wata farar mota ce ta faka gaban ta Ahmad sam ban kawo komai a raina ba, har sai da na hango Aminu ya fito daga cikin motar a fusace ya nufo inda nake, ganin hakan yasa na bude motar na fito na rufe tun kan ya karaso.
“Halima me kike a cikin motar nan?”
Haka ya aiko min da tambaya kamar wani ubana.
“Ban gane mi nake a ciki ba?”
“Abunda kike be dace ba, tun dazun na hango ki a cikin motar nan ina biye da ku har kika shiga wani gida kika fito, ya kamata ki san abunda kike fa wannan ba muharramin ki bane, kuma ki rika tunawa cewa kina da yara”
“Wace irin magana kake yi haka Aminu?”
“Kin san me nake nufi”
Ya fada yana kara hade fuska, sai wani huci yake kamar ba shi ba.
“Ya akai?”
Ahmad ya tambaya yana kallona hannunsa rike da gorar ruwa biyu.
“Ba komai”
Na fada ina dauke idona daga barin kallon Aminu.
“Oh ba komai za ki ce masa? Malam akwai komai wannan mata ta ce, miye hadin ka da ita?”
“Who's this?”
Ahmad ya tambaya yana kallona. Sai Aminun ya amsa masa da kansa cikin fusata.
“Mijinta ne uban yayanta”
Wani kallon uku saura kwata Ahmad yai masa.
“Sannu Uban yaya, da alama dai kana shaye shaye, domin mai hankali ba zai yi abunda kake yi ba”
“Ba shaye-shaye nake ba, ciye ciye nake, ka fita hanyar tun kamin dare yai ma, domin matata ce”
“Babu wani abu a tsakanina da shi Aminu, boss dina ne a gurin aiki, kuma kai baka isa ka hanani magana da wani namijin ba, domin babu igiyar aurenka a kaina”
“Amman akwai yaya a tsakaninmu ko?”
Ya fada cikin daga murya mutane har sun fara mana taro, Ahmad ya bude min front seat.
“Shiga ki zauna”
Ina kokarin zaunawa Aminu ya fisgo Hijabina har sai da fuskata ta daki ganbun motar.
A take Ahmad ya wulgar da gorar ruwan dake hannunsa ya zabgawa Aminu mari cikin zafin nama.
“You're very very stupid”
Aminu ya zaburo zai rama Ahmad ya rike masa hannu ya wulgar.
“Ni ka mara? Ni ka mara? Na san ko ni wanene? Akan matata?”
Shine abunda yake ta fada yana nufi gurin motarsa ya dauko wayarsa daga can gurin motar ya tsaya yana wayar, kamar yadda Ahmad din ma yake waya a kusa da ni. Faruk naji ya kira sunan mutumen sannan ya fada masa abunda yake bukata tare da bashi addireshin inda mike. Sannan ya juyo ya kalli gefen goshina dake zubar da jini. Zagayawa yai ya bude motar ya dauko tissue ya mika min.
“Sannu”
Ya fada cike da nuna danuwarsa. Sannan ya kalli Aminu dake kokarin shiga motarsa yace.
“Indai ka cika kai dan iska ne ka tsaya nan”
A take Aminu ya rufe motar ya sake nufo inda muke.
“Me kake nufi? Tsoronka ake ji? Uban waye kai a cikin garin nan? I warning you Wallahi Wallahi idan na sake ganinka da matata sai na halaka ka, dan iska kawai marar mutunci mai neman matar mutane”
Uffan Ahmad be sake ce masa ba, sai danna wayarsa yake. Aminu kam duk maganar daya yago sa ya yabawa Ahmad, ban tana ganin bacin ran Aminu irin na yau ba, tun da be tana fada a kaina ba, be tana nuna damuwarsa dan wani ya kula ni ba sai yanzu, jikinsa har wani rawa yake, kana kallonsa ka san kishi ne ke dawainiya da shi, kuma na banza domin a yanzu kam na masa nisa.
“Ina kokarina ashe kai ke dauke mata hankali, wawa kawai”
Na yi murmushi ina murza yatsun hannuna, yatsun nawa ya kalla sannan ya kalli fuskata kamin ya juya zuwa gurin teburinsa.
“Na gode”
Daga can inda yake tsaye ya dago ya kai ya kalleni.
“Da me?”
“Da komai da komai, na gode Allah ya saka da alheri”
“Amin Allah ya bamu hakuri we almost sharing the same journey, yanzu kin fahimci yadda rashin mahaifi yake kamar ni, gashi kece babba duk wanda zai miki magana zai ce ki yi kokarin hada kan yan'uwanki right”
Ya karasa yana murmushi kamin ya cigaba.
“Haka akai ta min sai nake jin kamar an dora min wani nauyi akai, na rika ganin kamar ba gaske ba ne, ina ta ganin kamar idan na shiga gida zan ga Abbah, idan na kalli Hajiya ta bani tausayi haka ma Siyama, yanzu da nai hakuri na dauki nauyin sai abun ya zo kin da sauki, amman fa har yanzu Hajiyata bata yarda na girma ba, idan zan fita zata bani time din dawowa idan na dade zata kirani tace na dawo dare yayi ko rana, babban mutum kamar ni”
Daga ni har shi murmushi muke sai ya tako ya karaso kusa da ni ya miko min tissue, ashe ya lura da hawayen da suka taru a idona.
“Miyasa ba ki koma gurin Doc ba?”
Na yi shiru ban ce komai ba, be kuma be fasa kallona ba, can kuma ya karasa ya dauki wayarsa ya taba sannan ya kalleni.
“Zaki iya zuwa office dinki”
“Na gode”
Na fada sannan na juya na fito daga office dinsa na nufi nawa office din, ko da na shiga matar bata nan, sai na suke jakata na zauna a kujerar ina ta tunanin mahaifina.
Ban yi aikin kamar yadda na saba ba, domin rashin kowa a kusa da ni sai ya kara saka ni cikin damuwa da tunani kala kala ciki har da na rayuwata da kuma Kabir ko yana ina ma yanzu Allah masani.
Misalin biyu da rabi Ahmad ya shigo office dina ganinsa yasa na tashi tsaye.
“Wata takardar nake nema, ta green light company”
A take na fara duba takardun da suke gaban teburin sai kuma nai arba da ita.
“Takardun da kika san zan yi amfani da su ki rika kai min ko kuma ki bawa sakatarena”
“Okay In-Sha-Allah zan kiyaye”
Har na mika masa takardar ya juya nace.
“Ranka ya dade ina son tambaya”
Juyowa yai yana kallona.
“Dan Allah Kabir nake tambaya, wani mahaukaci wanda ya makure ni ka”
Murmushi yai.
“Mutumen da kika ja min ya naushe ni ido kenan”
Nima murmushin nai.
“Kina son ganinsa ne?”
“Eh tun ranar ban sake ganinsa ba”
“Na saka a dauke ke shi ne akai shi gidan mahaukata”
Na ji ba dadi har hakan ya kasa boyu a a fuskata, sai kallonsa nake na rasa abunda zan ce masa. Dawowa yai gaban teburin nawa ya tsaya yana kallona.
“Karki damu, ina son ki samu natsuwa ne sai mu fara processing din nema masa lafiya, tun da naga ciwonsw ya dame ki”
Da sauri na mike tsaye baki sake ina zaro ido.
“Da gaske?”
“Da karya”
Ita ce amsar daya bani ya juya ya fice daga office din yana murmushi.
__________________
Assalamu Alaikum.
Ban yi niyar cewa komai akan littafin nan ba, duk kuwa da irin comments din da nake gani musamman whatsapp, wasu na complain abunda nake ma Halima yayi yawa so so this and that, akwai ma wacce tace min tana kwankwanton imani akan irin halin da nake saka Halima, na ji zafin maganar amman nai mata uzuri saboda ina daukar tana cikin irin mutanen da ke karatu basa daukar darasi burinsu kawai a samu nishadi.
Ina son ku sani idan ma baku sanin ba, idan kuma kun manta na tuna muku tun farkon fara labarin nan sai da na fada cewar ban sani ba ko zai muku dadi ba labari ne na soyayya ba kamar yadda aka saba, labari ne na fadi tashin rayuwa, kalubalen rayuwar da na aure wanda zai tabo wani bangare na rayuwarmu ta yau da kullum.
Duk yadda kike jin dadi Wallahi baki kamo wata ko a farce da jindadi ba, haka duk yadda kika a cikin tsanani baki kai kan akaifar wata shiga kunci rayuwa ba, labarin nan kirkiren labari ne amman ni nasan ba za a rasa wandanda suke rayuwa irin ta Halima ba, domin na ci karo da wasu a lokacin da nake rubutun nan, wani jarabarwarsa kadan ne wani da yawa, kuma kowa da inda Allah yake jarrabarsa. Idan baki cikin matsala wata na ciki, kuma ban cilastawa kowa karantawa ba sai wanda yaji yana ra'ayi, dan haka dan Allah kar wacce ta sake yi min wata magana marar dadi akan rayuwar Halimatu, duk wanda ya sake fada min rashin arziki goma billahil azeem zan fada masa ashiri, ba dole sai rai na so.
And wandanda suka tuna mahaifansu jiya, wasu har da kuka, ina addu'ar Allah ya jikansu, mu kuma ya sa mu cika da imani.
Ameen thumma Ameen.
7/21/21, 10:47 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
4️⃣8️⃣
Tun daga yanayin tafiyata zaka fahimci ina cikin wani irin nishadi marar misaltuwa, na fito daga cikin gidan na nufo inda motar Ahmad take fake ya sauke gilashin motar yana kallona har na karaso, da kansa ya miko hannunsa ya bude min motar, na shiga ciki na zauna ina gyara jakata. Sai yai motar key muka hau titi sannan ya kalleni.
“Happy?”
Na gyada masa kai idanuwana suna kokarin cika da hawayen jindadi.
“Yes”
Sai yai kyakkyawan murmushin daya karawa fuskarsa kyau.
“Thank You”
“No thank you da kika amince, hop dai kin fada musu ke za ki yi ba ni ba”
Na yi shiru ina kallon gorar ruwan daya dauka zai sha.
“Sun jidadi sosai, kuma sun yi supporting”
Murmushi kawai yai ya kalle ya karasa kurbe ragowar ruwan, ba mu yi wata tafiya mai nisa ba ya faka gefen titi yana kallona.
“Bari na karbo ruwa shagon can, bana iya zama ba ruwa a mota”
Bude motar yai ya fita, da wani irin kallo na bishi na jindadin daukar nauyin duba lafiyar Kabir da yai, haka Allah yake lamarinsa idan ya zo taimaka maka sai ya maka hanyar samun abun ko ta ta silar wani ne, and farincikin dana gani a fuskar yan'uwan Kabir a yau da naje musu da labarin ya kara faranta min rai fiye da kima. Wata farar mota ce ta faka gaban ta Ahmad sam ban kawo komai a raina ba, har sai da na hango Aminu ya fito daga cikin motar a fusace ya nufo inda nake, ganin hakan yasa na bude motar na fito na rufe tun kan ya karaso.
“Halima me kike a cikin motar nan?”
Haka ya aiko min da tambaya kamar wani ubana.
“Ban gane mi nake a ciki ba?”
“Abunda kike be dace ba, tun dazun na hango ki a cikin motar nan ina biye da ku har kika shiga wani gida kika fito, ya kamata ki san abunda kike fa wannan ba muharramin ki bane, kuma ki rika tunawa cewa kina da yara”
“Wace irin magana kake yi haka Aminu?”
“Kin san me nake nufi”
Ya fada yana kara hade fuska, sai wani huci yake kamar ba shi ba.
“Ya akai?”
Ahmad ya tambaya yana kallona hannunsa rike da gorar ruwa biyu.
“Ba komai”
Na fada ina dauke idona daga barin kallon Aminu.
“Oh ba komai za ki ce masa? Malam akwai komai wannan mata ta ce, miye hadin ka da ita?”
“Who's this?”
Ahmad ya tambaya yana kallona. Sai Aminun ya amsa masa da kansa cikin fusata.
“Mijinta ne uban yayanta”
Wani kallon uku saura kwata Ahmad yai masa.
“Sannu Uban yaya, da alama dai kana shaye shaye, domin mai hankali ba zai yi abunda kake yi ba”
“Ba shaye-shaye nake ba, ciye ciye nake, ka fita hanyar tun kamin dare yai ma, domin matata ce”
“Babu wani abu a tsakanina da shi Aminu, boss dina ne a gurin aiki, kuma kai baka isa ka hanani magana da wani namijin ba, domin babu igiyar aurenka a kaina”
“Amman akwai yaya a tsakaninmu ko?”
Ya fada cikin daga murya mutane har sun fara mana taro, Ahmad ya bude min front seat.
“Shiga ki zauna”
Ina kokarin zaunawa Aminu ya fisgo Hijabina har sai da fuskata ta daki ganbun motar.
A take Ahmad ya wulgar da gorar ruwan dake hannunsa ya zabgawa Aminu mari cikin zafin nama.
“You're very very stupid”
Aminu ya zaburo zai rama Ahmad ya rike masa hannu ya wulgar.
“Ni ka mara? Ni ka mara? Na san ko ni wanene? Akan matata?”
Shine abunda yake ta fada yana nufi gurin motarsa ya dauko wayarsa daga can gurin motar ya tsaya yana wayar, kamar yadda Ahmad din ma yake waya a kusa da ni. Faruk naji ya kira sunan mutumen sannan ya fada masa abunda yake bukata tare da bashi addireshin inda mike. Sannan ya juyo ya kalli gefen goshina dake zubar da jini. Zagayawa yai ya bude motar ya dauko tissue ya mika min.
“Sannu”
Ya fada cike da nuna danuwarsa. Sannan ya kalli Aminu dake kokarin shiga motarsa yace.
“Indai ka cika kai dan iska ne ka tsaya nan”
A take Aminu ya rufe motar ya sake nufo inda muke.
“Me kake nufi? Tsoronka ake ji? Uban waye kai a cikin garin nan? I warning you Wallahi Wallahi idan na sake ganinka da matata sai na halaka ka, dan iska kawai marar mutunci mai neman matar mutane”
Uffan Ahmad be sake ce masa ba, sai danna wayarsa yake. Aminu kam duk maganar daya yago sa ya yabawa Ahmad, ban tana ganin bacin ran Aminu irin na yau ba, tun da be tana fada a kaina ba, be tana nuna damuwarsa dan wani ya kula ni ba sai yanzu, jikinsa har wani rawa yake, kana kallonsa ka san kishi ne ke dawainiya da shi, kuma na banza domin a yanzu kam na masa nisa.
“Ina kokarina ashe kai ke dauke mata hankali, wawa kawai”