Sashe 2
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta amsa tana tambayar ina na baro su Namra da Salim.
“Suna gidan kanen babansu kin san yau weekend ne wai yace zai kaisu yawo tare da yaransa shine suka tafi Amal ce kawai ta ki zuwa”
“Ita sarkin lakuwa daman kullum tana nan manne da ke, idan kika haifo wani sai na ga yadda za tai”
Cewar kanwata Amina, ni kuma nai dariya na ce.
“Aa yar auta ce ai”
Kausar ta ce
“Ba wani auta wata zaki haihu mu ga karshen lakuwa”
Ban bi ta kansu ba na kalli Mama ina dariya na ce
“Ga sabulu nan na kawo muku, sauran siyayyar ssai wani watan”
“Babu komai Allah ya miki albarka”
Daman haka nake wata siyayar da ban yi ba a wani watan na ke musu ita saboda ni ma kaina ina yi ma kaina wata lalurar domin ba komai namiji yake dauke ma ba, balle miji irin nawa, daman kuma can maza ba sa son ba ni ba ni wannan yasa na tsaya kai da fata akan aikina, a duk lokacin da an karbi albashina sai nai ma kaina da iyayena lalurar da bata gagareni ba.
Bayan sallah la'asar na shiga dakin Baba na gaishe shi na bashi dubu biyar a cikin albashina kamar yadda na saba masa ko wane wata bayan siyayyar da na ke, yayi murna kuma ya min addu'a sannan na taso na fito harabar gidan inda kanenna suke zaune na zauna muna ta fira, a gurin Maryam na ga wani slim tea da kawarta ke saidawa na siye daya, ba dan ina da tabbacin yana yi ba sai dan neman rabuwa da kibar da na ke ko dan na huta da ci mun fuska da Abbah Adnan ke yi.
“Wai Anty Halima kin gama karanta Littafin Zaki kuwa?”
Jawahir ta tambaye ni. Ni ko na tabe baki ina murmushi.
“Hmmm na karanta gaskiya ba laifi littafin yayi dadi, wannan iya gata da soyayya da Aliyu ke nuna ma Ataa”
“Wallahi nima soyayyarsu ta tafi da ni, idan nai aure haka zan yi da mijina”
Ta karasa tana rage murna dan kar Inna ko Mama su jiyota. Sai muka kwashe da dariya.
“Ai auren yanzu ba wani soyayya a ciki Jawahir sai dai kawai hakuri da neman aljanna, amman duk wata soyayya ta littafi karki saka ran samunta a gaske, ban ce ba a samu ba ana samu amman kadan ba da yawa ba”
Na fada ina tuna irin tsarin rayuwar da na shirya ma kaina da mijin da na aura kamin aure, sai dai ina yin aure sai na tarar da ba haka ba daga lokacin da na fara haihuwa kuma sai na ga canji a gurin mijina, har ta kai yanzu bana burge shi saboda na yi kiba na yi fadi litattana ta canja daga budurwa zuwa mai aure da yara hudu.
Haka dai muka cigaba da firarmu gurin dariya mu yi har akai magariba, bayan na yi sallah na shiga dakin Mama na bata dubu biyar na bawa Inna budu biyu sannan na dauko Amal muka fito kannena biyu suka rakoni. Na samu napep nai min jinga daga unguwar zuwa igala quarters zai kawo ni dari biyu, a take na shiga su kuma suka kama hanya.
Ko da muka isa na tarar Abban Adnan ya dawo domin na ga motarsa a harabar gidan tun kamin na shiga, da sallama na tura kofar falon na shiga, sai dai be amsa min ba kuma be dago ya kalli inda na ke ba, yana zaune saman cushion idonsa akan tv yana kallon hausa bakwai suna haska wani hausa film da ban tantance shi ba, jin muryar yara a upstairs ya tabbatar min da sun dawo kenan suna dakinsu domin shi kadai ne a falon.
“Sannu da zuwa yanzu ka dawo?”
Be amsa ni ba sai wani cin magani da yai ya kalleni.
“Karki sake tura min yara gurin yawo, kin tura su kuma kema kin fita yawon ki”
“Ba yawo naje ba gida naje kuma na fada maka kamin na tafi”
“Na dai fada miki, bana son yarana suna zuwa gidan kowa, kuma na fada miki ki aje aikin nan bana so saboda aure na auro ki ba dan ki rika fita zuwa aiki ba”
Bance masa uffan ba, idan sabo na saba da jin maganarsa ta na aje aiki, ni kuma na gagara ajewar kamar yadda yake bukata saboda be dauke min duka lalurorina ba, kuma ga iyayena suna da bukatar taimakona a yanzu, aikin ma da be fi shekara uku da farawa ba. Amal ta tafi kusa da shi ta zauna shi ko hankalinsa na kan tv sai yabon kyau Fati washe yake, na san yana yin hakan ne saboda na ji haushi kuma na ji, domin har yanzu na kasa sabawa da halinsa na yabon kyawun wasu matan a gabana. Ina jin ba dadi idan ya yabi wace bata da jiki ko ya nuna yana son mace marar jiki saboda na san ni din ba siririya ce ba, duk kuwa da kasancewar ba wata shahararriyar kiba ce da ni ta kaico ba, kuma na san matukar mutun be ce min kyakkyawa ba to ko ba zai kira ni da mummuna ba, domin ni ma ina da kyau na iya yadda Allah ya ga zai dace da ni, ina da haske sai dai ba can sosai ba.
Upstairs na nufa dakin yarana na fara shiga na sai na samu Adnan da Aiman suna buga game a system dina, Namra kuma tana kwance saman gado ta rufe ido sai juyi take, cike da damuwa na zauna kusa da ita na kai hannu ina shafa bayanta.
“Namra lafiya?”
“Momy cikina ke ciwo sosai”
“Me kika ci?”
“Banci komai ba”
Ta fada cikin kuka ba tare da ta bude idon ba.
“Adnan me Namra ta ci? Ta ci yaji ko?”
Sai a lokacin ya dago har ya lura da ba dawo, ya zo inda nake da murnarsa shi da Aiman suka dafa ni.
“Momy kin dawo?”
“Eh me Namra ta ci?”
Adnan ya ce
“Wallahi ban sani ba, Baba Sadi ya kai mu gurin wasa yara ita kuma ya fita da ita yace zata raka shi wani guri kila can ta taci wani abun, domin da suka dawo ta rika cewa cikina na ciwo”
“Namra kin ci wani abu a can?”
“Ya siya min nama na ci kuma da yaji a ciki amman kadan ne yajin na ci saboda kin ce na daina cin yaji”
“To yajin ne ya saki ciwon ciki, bari na jika miki kanwa”
Ya fada ina mikewa tsaye na nufi kofar fita, Aiman ta biyo ni a bayana yana fadin shi ma zai sha, daman haka yake duk abunda ya ga yar'uwarsa Namra ta sha shi ma sai ya sha komai dacin abun saboda tsabar rigima.
*If you want to subscribe pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*
7/20/21, 8:28 AM - Buhainat: Ziyarci YouTube channel dina mai suna Taskar Khadeeja Candy domin samu duka littafaina a Kyauta
https://youtu.be/P9GOP9cqP6Y karku manta ku danna min subscribe Comment & Share.
*GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
2️⃣
Sai da na jika mata kanwar ta sha na shiga dakina nai sallah isha'i, ina sallamewa nai saurin mikewa tsaye na nufi inda wayata take tana ringing na duba na yi zaton ko Abban Namra ne da farko sai dai ganin bakuwar number yasa ni aje wayar har sai na koma saman carpet har sai da na gama tasbihina nai addu'a ma mijina nai ma kaina da iyayena sannan na nemawa yara na shiriya. Daga bisani na mike tsaye na nufi inda wayar take aje na dauka na sake kiran layin da aka kirani da shi.
“Assalamu Alaikum”
Ni na fara mika sallamar kamin wanda na kiran ya fara min sallamar.
“Wa'alaikissalam Halimatu”
“Na'am Ranka ya dade”
Na gane cewar ogana ne na gurin aiki wato oga Dahiru.
“Ki yi kokarin hada document dinka kamin gobe ina da bukatarsu”
“To ranka ya dade”
“Kuma ki yi saving din wannan number ita ma number ta ce”
“To ranka ya dade”
Daga haka ya kashe wayar be sake ce min komai ba, ni ma kuma ban ce ba, daman kuma me zan ce masa, bayan kiran da yake min ma yana damuna balle kuma har nai wata magana da shi, zauna nai bakin gadon ina ta mamakin dalilin kiran da oga Dahiru yake yawan min a duk lokacin da yake bukatar wani abun, shin yana manta cewar ni ma ina da aure da iyali kamar shi, ban san miyasa yake son kira akan abunda be kai ya kawo ba, ba kira kadai ba har wasu abubuwna da yake min bana jindadinsu, domin duk abunda na ke ina kokarin kare mutuncin aure da kuma na yayana da mijina.
“Momy ni dai gobe idan mun dawo daga scul gidan zan dawo ba zan je gidan Baba Sadi ba”
Namra ce ta shigo tana wannan maganar tana wani bata fuska kamar zata fashe da kuka.
“Saboda me?”
“Bana son zawa can Momy dan Allah”
“Ki yi hakuri Mamana, idan kun dawo nan gidan ba wani abun za ku yi ba, kuma kin ga ba girki balle ku ci, amman can Momy Hassana tana girkawa, za ku samu ku ci”
“Momy to ki daina zuwa aikin nan pls ko kuma mu rika zama a gida a haka muna jiranki ki dawo”
“Mamana akwai abunda ake miki a gidan ne da baki so?”
Ta girgiza kai alamar aa sannan ta kwantar da kanta jikina.
“Cikin ya daina ciwo?”
“Eh amman yana min kadan-kadan ba sosai ba”
“Zai daina In-Sha-Allah, na zubo miki abinci za ki ci?”
“Za mu ci tare Momy zan wanke hannuna ba zan saka miki datti ba”
“Suna gidan kanen babansu kin san yau weekend ne wai yace zai kaisu yawo tare da yaransa shine suka tafi Amal ce kawai ta ki zuwa”
“Ita sarkin lakuwa daman kullum tana nan manne da ke, idan kika haifo wani sai na ga yadda za tai”
Cewar kanwata Amina, ni kuma nai dariya na ce.
“Aa yar auta ce ai”
Kausar ta ce
“Ba wani auta wata zaki haihu mu ga karshen lakuwa”
Ban bi ta kansu ba na kalli Mama ina dariya na ce
“Ga sabulu nan na kawo muku, sauran siyayyar ssai wani watan”
“Babu komai Allah ya miki albarka”
Daman haka nake wata siyayar da ban yi ba a wani watan na ke musu ita saboda ni ma kaina ina yi ma kaina wata lalurar domin ba komai namiji yake dauke ma ba, balle miji irin nawa, daman kuma can maza ba sa son ba ni ba ni wannan yasa na tsaya kai da fata akan aikina, a duk lokacin da an karbi albashina sai nai ma kaina da iyayena lalurar da bata gagareni ba.
Bayan sallah la'asar na shiga dakin Baba na gaishe shi na bashi dubu biyar a cikin albashina kamar yadda na saba masa ko wane wata bayan siyayyar da na ke, yayi murna kuma ya min addu'a sannan na taso na fito harabar gidan inda kanenna suke zaune na zauna muna ta fira, a gurin Maryam na ga wani slim tea da kawarta ke saidawa na siye daya, ba dan ina da tabbacin yana yi ba sai dan neman rabuwa da kibar da na ke ko dan na huta da ci mun fuska da Abbah Adnan ke yi.
“Wai Anty Halima kin gama karanta Littafin Zaki kuwa?”
Jawahir ta tambaye ni. Ni ko na tabe baki ina murmushi.
“Hmmm na karanta gaskiya ba laifi littafin yayi dadi, wannan iya gata da soyayya da Aliyu ke nuna ma Ataa”
“Wallahi nima soyayyarsu ta tafi da ni, idan nai aure haka zan yi da mijina”
Ta karasa tana rage murna dan kar Inna ko Mama su jiyota. Sai muka kwashe da dariya.
“Ai auren yanzu ba wani soyayya a ciki Jawahir sai dai kawai hakuri da neman aljanna, amman duk wata soyayya ta littafi karki saka ran samunta a gaske, ban ce ba a samu ba ana samu amman kadan ba da yawa ba”
Na fada ina tuna irin tsarin rayuwar da na shirya ma kaina da mijin da na aura kamin aure, sai dai ina yin aure sai na tarar da ba haka ba daga lokacin da na fara haihuwa kuma sai na ga canji a gurin mijina, har ta kai yanzu bana burge shi saboda na yi kiba na yi fadi litattana ta canja daga budurwa zuwa mai aure da yara hudu.
Haka dai muka cigaba da firarmu gurin dariya mu yi har akai magariba, bayan na yi sallah na shiga dakin Mama na bata dubu biyar na bawa Inna budu biyu sannan na dauko Amal muka fito kannena biyu suka rakoni. Na samu napep nai min jinga daga unguwar zuwa igala quarters zai kawo ni dari biyu, a take na shiga su kuma suka kama hanya.
Ko da muka isa na tarar Abban Adnan ya dawo domin na ga motarsa a harabar gidan tun kamin na shiga, da sallama na tura kofar falon na shiga, sai dai be amsa min ba kuma be dago ya kalli inda na ke ba, yana zaune saman cushion idonsa akan tv yana kallon hausa bakwai suna haska wani hausa film da ban tantance shi ba, jin muryar yara a upstairs ya tabbatar min da sun dawo kenan suna dakinsu domin shi kadai ne a falon.
“Sannu da zuwa yanzu ka dawo?”
Be amsa ni ba sai wani cin magani da yai ya kalleni.
“Karki sake tura min yara gurin yawo, kin tura su kuma kema kin fita yawon ki”
“Ba yawo naje ba gida naje kuma na fada maka kamin na tafi”
“Na dai fada miki, bana son yarana suna zuwa gidan kowa, kuma na fada miki ki aje aikin nan bana so saboda aure na auro ki ba dan ki rika fita zuwa aiki ba”
Bance masa uffan ba, idan sabo na saba da jin maganarsa ta na aje aiki, ni kuma na gagara ajewar kamar yadda yake bukata saboda be dauke min duka lalurorina ba, kuma ga iyayena suna da bukatar taimakona a yanzu, aikin ma da be fi shekara uku da farawa ba. Amal ta tafi kusa da shi ta zauna shi ko hankalinsa na kan tv sai yabon kyau Fati washe yake, na san yana yin hakan ne saboda na ji haushi kuma na ji, domin har yanzu na kasa sabawa da halinsa na yabon kyawun wasu matan a gabana. Ina jin ba dadi idan ya yabi wace bata da jiki ko ya nuna yana son mace marar jiki saboda na san ni din ba siririya ce ba, duk kuwa da kasancewar ba wata shahararriyar kiba ce da ni ta kaico ba, kuma na san matukar mutun be ce min kyakkyawa ba to ko ba zai kira ni da mummuna ba, domin ni ma ina da kyau na iya yadda Allah ya ga zai dace da ni, ina da haske sai dai ba can sosai ba.
Upstairs na nufa dakin yarana na fara shiga na sai na samu Adnan da Aiman suna buga game a system dina, Namra kuma tana kwance saman gado ta rufe ido sai juyi take, cike da damuwa na zauna kusa da ita na kai hannu ina shafa bayanta.
“Namra lafiya?”
“Momy cikina ke ciwo sosai”
“Me kika ci?”
“Banci komai ba”
Ta fada cikin kuka ba tare da ta bude idon ba.
“Adnan me Namra ta ci? Ta ci yaji ko?”
Sai a lokacin ya dago har ya lura da ba dawo, ya zo inda nake da murnarsa shi da Aiman suka dafa ni.
“Momy kin dawo?”
“Eh me Namra ta ci?”
Adnan ya ce
“Wallahi ban sani ba, Baba Sadi ya kai mu gurin wasa yara ita kuma ya fita da ita yace zata raka shi wani guri kila can ta taci wani abun, domin da suka dawo ta rika cewa cikina na ciwo”
“Namra kin ci wani abu a can?”
“Ya siya min nama na ci kuma da yaji a ciki amman kadan ne yajin na ci saboda kin ce na daina cin yaji”
“To yajin ne ya saki ciwon ciki, bari na jika miki kanwa”
Ya fada ina mikewa tsaye na nufi kofar fita, Aiman ta biyo ni a bayana yana fadin shi ma zai sha, daman haka yake duk abunda ya ga yar'uwarsa Namra ta sha shi ma sai ya sha komai dacin abun saboda tsabar rigima.
*If you want to subscribe pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*
7/20/21, 8:28 AM - Buhainat: Ziyarci YouTube channel dina mai suna Taskar Khadeeja Candy domin samu duka littafaina a Kyauta
https://youtu.be/P9GOP9cqP6Y karku manta ku danna min subscribe Comment & Share.
*GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
2️⃣
Sai da na jika mata kanwar ta sha na shiga dakina nai sallah isha'i, ina sallamewa nai saurin mikewa tsaye na nufi inda wayata take tana ringing na duba na yi zaton ko Abban Namra ne da farko sai dai ganin bakuwar number yasa ni aje wayar har sai na koma saman carpet har sai da na gama tasbihina nai addu'a ma mijina nai ma kaina da iyayena sannan na nemawa yara na shiriya. Daga bisani na mike tsaye na nufi inda wayar take aje na dauka na sake kiran layin da aka kirani da shi.
“Assalamu Alaikum”
Ni na fara mika sallamar kamin wanda na kiran ya fara min sallamar.
“Wa'alaikissalam Halimatu”
“Na'am Ranka ya dade”
Na gane cewar ogana ne na gurin aiki wato oga Dahiru.
“Ki yi kokarin hada document dinka kamin gobe ina da bukatarsu”
“To ranka ya dade”
“Kuma ki yi saving din wannan number ita ma number ta ce”
“To ranka ya dade”
Daga haka ya kashe wayar be sake ce min komai ba, ni ma kuma ban ce ba, daman kuma me zan ce masa, bayan kiran da yake min ma yana damuna balle kuma har nai wata magana da shi, zauna nai bakin gadon ina ta mamakin dalilin kiran da oga Dahiru yake yawan min a duk lokacin da yake bukatar wani abun, shin yana manta cewar ni ma ina da aure da iyali kamar shi, ban san miyasa yake son kira akan abunda be kai ya kawo ba, ba kira kadai ba har wasu abubuwna da yake min bana jindadinsu, domin duk abunda na ke ina kokarin kare mutuncin aure da kuma na yayana da mijina.
“Momy ni dai gobe idan mun dawo daga scul gidan zan dawo ba zan je gidan Baba Sadi ba”
Namra ce ta shigo tana wannan maganar tana wani bata fuska kamar zata fashe da kuka.
“Saboda me?”
“Bana son zawa can Momy dan Allah”
“Ki yi hakuri Mamana, idan kun dawo nan gidan ba wani abun za ku yi ba, kuma kin ga ba girki balle ku ci, amman can Momy Hassana tana girkawa, za ku samu ku ci”
“Momy to ki daina zuwa aikin nan pls ko kuma mu rika zama a gida a haka muna jiranki ki dawo”
“Mamana akwai abunda ake miki a gidan ne da baki so?”
Ta girgiza kai alamar aa sannan ta kwantar da kanta jikina.
“Cikin ya daina ciwo?”
“Eh amman yana min kadan-kadan ba sosai ba”
“Zai daina In-Sha-Allah, na zubo miki abinci za ki ci?”
“Za mu ci tare Momy zan wanke hannuna ba zan saka miki datti ba”