Sashe 83
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Na fada ina fashewa da kuka, ruwa na ta dukan kaina. Kasa na fara tafiya daman tazarar dake tsakanin inda ya sauke ni da gidanmu babu nisa sosai, tun ina tafiya ruwan na sauka da karfi har suka rage, ban daina tunani da kuka ba. Ruwan da ke saukowa ya taimaka min da ya hana a gane ina hawaye saboda yana dukan kaina. A lokacin da na shiga gida kowa yana daki ya fake, kai tsaye na nufi dakin Mama, ban saba shiga ba sallama ba amma a yau haka na shiga babu sallama mana ma iya kallon wake falon waye baya ciki.
Dakin Mama na shiga na cire tufafin jikina na dauki zanenta na daura, tana ta kallona da yadda nake motsa jiki babu kuzari.
“Lafiya kike yau kuwa?”
“Nima ban sani ba, ko lafiya nake ko ba lafiya nake ba”
Na amsa mata ina hawaye.
“Miya faru”
Juyowa nai na kalleta.
“Mama ni ce babba a cikin yayanki, ya kamata na zama mai hankali da tunani ko? Da hangen nesa amman duk ban zama ba”
Zaunawa nai kusa da ita na kai jikina a cinyarta na kwanta ina kuka.
“Fada min matsalarki miya faru”
“Mama Abdallah..... Ya fada min a yau ba zai aureni ba”
Murmushi tai.
“Halimatu kenan, daman taya za'ayi Abdallah ya aure ki? Bayan dan'uwansa ya aure ki? Kuma dan'uwan nasa yana nan a raye? Mu ma ai ba zamu bari ki aikata wannan kuskuren ba, domin na san kiyayya da gaba ce zata shiga tsakaninsu wanda mahaifiyarsu ba zata so hakan ba”
“Amman.... Ba.... Haramun...ba ne... ”
“Ke kika san wannan, abubuwa da yawa yanxu al'adarmu ta mayarda su haram saboda kunya da gudun samun tsabani, kin yi kuskure Halimatu da dai tun farko ne kina da damar zabar Abdallah ki bar Abdulhamid amman ba ki yi ba, tun farko Abdallah ya kamata ki aura na ta nuna miki amman kika kasa ganewa, mutum da be taba kyamar yayanki ba, be taba nuna gajiyawa a taimakonki ba, shine mutumen da ya kamata ya zama abokin rayuwarki tun farko”
Dagowa nai na kalleta.
“Amman wani abu be taba shiga tsakanina da Abdulhamid ba....”
“Mutane ba su san da wannan ba”
Tashi nai daga dakin gaba daya, na nufi dakina, na zauna saman katifata ban ji ina bukatar komai ba sai kuka da nadama. A ranar ban rumtsa ba har sai da na rubuce labarin kaddarar rayuwata tas a jikin takardar da Abraham ya karbo min.
Da akam ban yi niyar zuwa ba, amman yanzu zanje saboda yara wadanda ke ta daukin zuwan.
Misalin takwas da rabi na dare aka aiko ana kirana, na san be wuce Abraham ba, wannan karon ban musa ba na saka Hijabina na fita, a inda ya saba tsayuwa na nufa yana tsaye a gurin jimgine da motarsa yana kallona har na karaso.
“Ya kike?”
“Ina lafiya”
Na amsa ba tare da na kalleshi ba. Sai kuma yai shiru yana kallona.
“Kamar kina cikin damuwa”
Sai a lokacin na kalleshi.
“Kaine karin damuwata, da zaka daina bibiyata da na samu salama, ka tafi na yafe maka, kaima kana cikin kaddara ta ne”
“Za ki aureni kenan?”
“Ba zan aureka ba”
Na amsa masa ina kuka.
“Ko da zan musulunta?”
“Ko da zaka aikata abunda ya fi musulunta, idan zaka musulunta ka musulunta saboda Allah kawai, saboda gudun azabarsa, saboda tsoronsa saboda kaunar Annbinsa, karka musulunta dan ni domin ni bana tabbata amman Allah tabbatacce ne, wanzanje wadatacce, tsarkaken, tsabtatacen, ka musulunta saboda tsoron wuta da kwadayin aljanna, zaka iya musulunta a yau saboda ni gobe Allah ya karbi rayuwata, shi zaka ci gaba da musuluncin ne ko zaka daina? Amman idan ka yi saboda Allah shi Allah tabbatacce ne, imaninka zai tabbata har Aljanna, kada kai komai saboda ni a yanzu ba aurene a gaba na ba, bana jin zan sake soyayya ma balle aure”
“Saboda me....?”
“Saboda mutumen da nke so, ba zai taba aurena ba, ya fada min zai mutu da so na a ransa, ni kuma zan rayu da kaunarsa har izuwa ranar da ajalina zai riske ni... ”
Na karasa cikin kuka.
“Wane mai sa'a ne wannan?”
“Wani ne wanda ya so ni a lokacin da duniya ta guje ni, ya taimaka a lokacin da bana da mai tsaya min, ya so yayana a lokacin da ubansu ya guje su”
“Then miyasa yanzu ba zai aureki ba?”
“Saboda na auri dan'uwansa, mutumen da ka keta min haddi a gidansa, dan Allah wannan zuwan ya zama na karshe a gurina, ka barni na ji da damuwata”
Na karasa ina hade hannayena ina rokonsa.
“Ke ba ki yarda haduwar mu kaddara ba ce? Taya za ka yi mace fyade a dare a lokacin da kake boyon kanka, sai kuma ka dawo da rana ka kawo kanka ba tare da fargabar komai ba? Da zaki buda zuciya babu abunda za ki gani sai kaunarki, son ki yasa na ke sha'awar barin addinina na dawo na ki, zan iya hakurin zama da ke a haka da soyayyar wani a ranki, da sannu zan koya miki so na har ki aminta....”
“Babu namijin da zai koya min so a yanzu, sai da safe.... ”
Ina fadar hakan na juyo na nufo gida ina jinsa yana kirana na kina amsa har na shigo gida.
Tun daga ranar babu ranar da bana bachi da bakinciki, sai a yanzu na gane cewar na yi kuskure a lokacin da babu hanyar gyara kuskuren.
Daga lokacin ban sake zuwa aiki ba, umarnin Abdallah ya hau kaina na cewar na bar aikin idan ba za su canja min tufafi ba, ban tafi na fada musu ba sai dai na san mawuyacin abu ne su yarda su canja min, balle kuma na jawa mai kamfanin fada da mahaukaci ko ya ma suka kare oho.
A ana gobe children day, Aminu ya sallamo min, ban fita ba hakan yasa ya nemi izinin shigowa cikin gidan ya shigo ya same a falo ina gyara tufafin su Aiman. Da sallama ya shigo na amsa masa kaina babu dankwalina ga gashin kaina ya sha tsiro kanana gwanin sha'awa.
Tashi nai naje na dauko Hijabina na saka sannan na dawo na zauna.
“Yanzu Halima kin fi son rayuwar yaran nan ta tagayyara? Ba sa nan basa can? Haba Halima ko ba dan ni ba ko dan yara ai kamata ki duba...”
“Kamin ka sake ni ya kamata kai wannan tunanin ba a yanxu ba, a iya tunani baka shaye shaye Aminu sai neman mata miyasa kwakwalwarka take ta nuna maka cewar zan dawo gareka?”
“Shi ma Wallahi na daina, na riga na gane kuskurena Halima, kuma na yarda abunda ka aikatawa yar wani za a aikatawa, kuma zaka dandani dacin abunda ka aikatawa matar wani a gurin matarka”
“Shiyasa ka rabu da ita kenan? A lokacin ne ka gane cewar ina da matsayi a rayuwarka, shiyasa na dawo gareni, na jidadi idan har ka shiryu da gaske, domin har gobe kai ubansu Namra ne”
“Ban taba ganin mace mai hakuri da kawaici ba irinki Halimatu, wata mace bata taba so na kamar yadda kika so ni ba, ban gane hakan ba sai byan na rabu da ke, da farko arzikina ya fara karaya, sai aka fada min saboda na rabu da ke ne, arzikin yana tare da ke, amman kin san me? A yanzu na gane mutanen nan karya suke fada, ba saboda na rabu da ke na sara wasu abubuwan ba, saboda na ci amanarki ne kuma a maimakon na zauna da ke a haka sai na sake ki, na kuma kyale ki da hidimar yara, wanda hakkina ne, shiyasa Allah ya nuna min sakamakona tun a nan duniya”
“Hakan yana da kyau ko ba komai ai yasa ka shiryu, ina maka murna”
“Ba murna kadai nake son ki taya ni ba, ina son ki dubeni da idon rahama ki tausaya min dan Allah”
“Idan ma ka zo nn ne saboda ka fada min ka shiryu to ka yi kuskure, ka daina dogon mafarki a kaina, ni a yanzu na maka nesa, tun daga lokacin da na baro gidanka ban sake sha'awar zama da kai ba”
“Yaran mu hudu fa Halima, kin fison ki auri wani ki bar uban diyanki? Wa zai kula da su kamar yadda ke za ki yi?”
“Ka auro musu wata uwar mana, idan baka da wacce kake so ni zan iya nemo maka”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Dakin Mama na shiga na cire tufafin jikina na dauki zanenta na daura, tana ta kallona da yadda nake motsa jiki babu kuzari.
“Lafiya kike yau kuwa?”
“Nima ban sani ba, ko lafiya nake ko ba lafiya nake ba”
Na amsa mata ina hawaye.
“Miya faru”
Juyowa nai na kalleta.
“Mama ni ce babba a cikin yayanki, ya kamata na zama mai hankali da tunani ko? Da hangen nesa amman duk ban zama ba”
Zaunawa nai kusa da ita na kai jikina a cinyarta na kwanta ina kuka.
“Fada min matsalarki miya faru”
“Mama Abdallah..... Ya fada min a yau ba zai aureni ba”
Murmushi tai.
“Halimatu kenan, daman taya za'ayi Abdallah ya aure ki? Bayan dan'uwansa ya aure ki? Kuma dan'uwan nasa yana nan a raye? Mu ma ai ba zamu bari ki aikata wannan kuskuren ba, domin na san kiyayya da gaba ce zata shiga tsakaninsu wanda mahaifiyarsu ba zata so hakan ba”
“Amman.... Ba.... Haramun...ba ne... ”
“Ke kika san wannan, abubuwa da yawa yanxu al'adarmu ta mayarda su haram saboda kunya da gudun samun tsabani, kin yi kuskure Halimatu da dai tun farko ne kina da damar zabar Abdallah ki bar Abdulhamid amman ba ki yi ba, tun farko Abdallah ya kamata ki aura na ta nuna miki amman kika kasa ganewa, mutum da be taba kyamar yayanki ba, be taba nuna gajiyawa a taimakonki ba, shine mutumen da ya kamata ya zama abokin rayuwarki tun farko”
Dagowa nai na kalleta.
“Amman wani abu be taba shiga tsakanina da Abdulhamid ba....”
“Mutane ba su san da wannan ba”
Tashi nai daga dakin gaba daya, na nufi dakina, na zauna saman katifata ban ji ina bukatar komai ba sai kuka da nadama. A ranar ban rumtsa ba har sai da na rubuce labarin kaddarar rayuwata tas a jikin takardar da Abraham ya karbo min.
Da akam ban yi niyar zuwa ba, amman yanzu zanje saboda yara wadanda ke ta daukin zuwan.
Misalin takwas da rabi na dare aka aiko ana kirana, na san be wuce Abraham ba, wannan karon ban musa ba na saka Hijabina na fita, a inda ya saba tsayuwa na nufa yana tsaye a gurin jimgine da motarsa yana kallona har na karaso.
“Ya kike?”
“Ina lafiya”
Na amsa ba tare da na kalleshi ba. Sai kuma yai shiru yana kallona.
“Kamar kina cikin damuwa”
Sai a lokacin na kalleshi.
“Kaine karin damuwata, da zaka daina bibiyata da na samu salama, ka tafi na yafe maka, kaima kana cikin kaddara ta ne”
“Za ki aureni kenan?”
“Ba zan aureka ba”
Na amsa masa ina kuka.
“Ko da zan musulunta?”
“Ko da zaka aikata abunda ya fi musulunta, idan zaka musulunta ka musulunta saboda Allah kawai, saboda gudun azabarsa, saboda tsoronsa saboda kaunar Annbinsa, karka musulunta dan ni domin ni bana tabbata amman Allah tabbatacce ne, wanzanje wadatacce, tsarkaken, tsabtatacen, ka musulunta saboda tsoron wuta da kwadayin aljanna, zaka iya musulunta a yau saboda ni gobe Allah ya karbi rayuwata, shi zaka ci gaba da musuluncin ne ko zaka daina? Amman idan ka yi saboda Allah shi Allah tabbatacce ne, imaninka zai tabbata har Aljanna, kada kai komai saboda ni a yanzu ba aurene a gaba na ba, bana jin zan sake soyayya ma balle aure”
“Saboda me....?”
“Saboda mutumen da nke so, ba zai taba aurena ba, ya fada min zai mutu da so na a ransa, ni kuma zan rayu da kaunarsa har izuwa ranar da ajalina zai riske ni... ”
Na karasa cikin kuka.
“Wane mai sa'a ne wannan?”
“Wani ne wanda ya so ni a lokacin da duniya ta guje ni, ya taimaka a lokacin da bana da mai tsaya min, ya so yayana a lokacin da ubansu ya guje su”
“Then miyasa yanzu ba zai aureki ba?”
“Saboda na auri dan'uwansa, mutumen da ka keta min haddi a gidansa, dan Allah wannan zuwan ya zama na karshe a gurina, ka barni na ji da damuwata”
Na karasa ina hade hannayena ina rokonsa.
“Ke ba ki yarda haduwar mu kaddara ba ce? Taya za ka yi mace fyade a dare a lokacin da kake boyon kanka, sai kuma ka dawo da rana ka kawo kanka ba tare da fargabar komai ba? Da zaki buda zuciya babu abunda za ki gani sai kaunarki, son ki yasa na ke sha'awar barin addinina na dawo na ki, zan iya hakurin zama da ke a haka da soyayyar wani a ranki, da sannu zan koya miki so na har ki aminta....”
“Babu namijin da zai koya min so a yanzu, sai da safe.... ”
Ina fadar hakan na juyo na nufo gida ina jinsa yana kirana na kina amsa har na shigo gida.
Tun daga ranar babu ranar da bana bachi da bakinciki, sai a yanzu na gane cewar na yi kuskure a lokacin da babu hanyar gyara kuskuren.
Daga lokacin ban sake zuwa aiki ba, umarnin Abdallah ya hau kaina na cewar na bar aikin idan ba za su canja min tufafi ba, ban tafi na fada musu ba sai dai na san mawuyacin abu ne su yarda su canja min, balle kuma na jawa mai kamfanin fada da mahaukaci ko ya ma suka kare oho.
A ana gobe children day, Aminu ya sallamo min, ban fita ba hakan yasa ya nemi izinin shigowa cikin gidan ya shigo ya same a falo ina gyara tufafin su Aiman. Da sallama ya shigo na amsa masa kaina babu dankwalina ga gashin kaina ya sha tsiro kanana gwanin sha'awa.
Tashi nai naje na dauko Hijabina na saka sannan na dawo na zauna.
“Yanzu Halima kin fi son rayuwar yaran nan ta tagayyara? Ba sa nan basa can? Haba Halima ko ba dan ni ba ko dan yara ai kamata ki duba...”
“Kamin ka sake ni ya kamata kai wannan tunanin ba a yanxu ba, a iya tunani baka shaye shaye Aminu sai neman mata miyasa kwakwalwarka take ta nuna maka cewar zan dawo gareka?”
“Shi ma Wallahi na daina, na riga na gane kuskurena Halima, kuma na yarda abunda ka aikatawa yar wani za a aikatawa, kuma zaka dandani dacin abunda ka aikatawa matar wani a gurin matarka”
“Shiyasa ka rabu da ita kenan? A lokacin ne ka gane cewar ina da matsayi a rayuwarka, shiyasa na dawo gareni, na jidadi idan har ka shiryu da gaske, domin har gobe kai ubansu Namra ne”
“Ban taba ganin mace mai hakuri da kawaici ba irinki Halimatu, wata mace bata taba so na kamar yadda kika so ni ba, ban gane hakan ba sai byan na rabu da ke, da farko arzikina ya fara karaya, sai aka fada min saboda na rabu da ke ne, arzikin yana tare da ke, amman kin san me? A yanzu na gane mutanen nan karya suke fada, ba saboda na rabu da ke na sara wasu abubuwan ba, saboda na ci amanarki ne kuma a maimakon na zauna da ke a haka sai na sake ki, na kuma kyale ki da hidimar yara, wanda hakkina ne, shiyasa Allah ya nuna min sakamakona tun a nan duniya”
“Hakan yana da kyau ko ba komai ai yasa ka shiryu, ina maka murna”
“Ba murna kadai nake son ki taya ni ba, ina son ki dubeni da idon rahama ki tausaya min dan Allah”
“Idan ma ka zo nn ne saboda ka fada min ka shiryu to ka yi kuskure, ka daina dogon mafarki a kaina, ni a yanzu na maka nesa, tun daga lokacin da na baro gidanka ban sake sha'awar zama da kai ba”
“Yaran mu hudu fa Halima, kin fison ki auri wani ki bar uban diyanki? Wa zai kula da su kamar yadda ke za ki yi?”
“Ka auro musu wata uwar mana, idan baka da wacce kake so ni zan iya nemo maka”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”