Sashe 55
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dariya yai ya tashi tureta daga jikinsa ya tashi zaune. Ni kuma na dago na shiga dakin Mama. A dare Mama bata iya hakura ba har sai da ta ji dalilin mutuwar auren, ni kuma ban boye mata komai ba cikin har da fyade da kai min da abubuwan da suka faru, sai dai ban yarda na fada mata cewar Abdallah na ke zargi ba.
Na ga rashin jindadin mutuwar auren a fuskarta, daman wace uwa ce zata zo auren yarta ya mutu? Balle Mama da take daukar abu ta saka a rai, su Salma da Hafiza ma da suke yan mata ba su yi aure ba abun ya dame ta balle kuma ji ace aure na biyu ya mutu. Sai dai duk da hakan ta nuna min zama da Abdulhamid din ba mafita ba ne sakin ya fi tunda har yana zargina. Da yamma Su Adnan suka dawo daga islamiya, ganina suka hau murna kamar wacce suka shekara ba su gani ba, ganin na kai har bayan i'shai yasa Namra ta fara tambaya wai nan zan kwana.
“ A nan zan kwana, yanzu na dawo kenan sai illla ma shaa Allahu”
Wani irin tsalle ta daka ta dire tana murna ta kama hannuna ta rike.
“Momy da gaske?”
Na gyada mata sai ta kara rumgume ni tana ta murna.
“Yeee mun huta Momy ta dawo”
Iya murnar da yata take na ganina a kusa da ita ya isa da tabbatar da cewar yarana sun yi marmarina duk kuwa da suna zuwa su ganni ko na gansu idan bukatar hakan ta kama, sai dai ko wane d'a yana bukatar mahaifiyarsa a kusa da shi, amman ni na bar su na auri Abdulhamid, a yau ya saka min da haka! Da tunanin abun na kwana a zuciyata har safe.
Washe gari Baba ya kira ni a dakinsa ya tambaye ni abunda ya faru, a nan na tsige masa tun daga biri har wutsiya, a ganina shi mahaifina ne be kamata na boye masa komai ba. Shi ya ba ni shawarar zuwa asibiti na sake yin gwajin hiv dan tabbatarwa. Ban yi wata wata ba na shirya na tafi gurin gwajin. Ban dawo ba sai yamma domin daga asibitin na wuce gidansu kawata Hajara, a lokacin da na labarta mata mutuwar auren sai ta fashe da kuka kamar an mata mutuwa.
“Wannan wane irin abu ne yake ta bibiyarki Halimatu? Tun farko sai da na ce ki auri Abban Ikram da yanzu duk wannan abun be faru ba kika ki”
Kai na girgiza mata.
“Wallahi sai ya faru, abunda Allah ya rubuta ya samu bawa babu mahani, na yarda da wannan”
“Allah sarki Halimatu, ga ki da tauhidi ga yarda da kaddara, Allah ya yaye miki wannan abu da yake bibiyarki”
Ta fada cikin kuka ni kuma na amsa da amin. Bayan sallah magariba na koma gida, sai na tararda tsakar gidamu cike da kayana na daki, alamar Abdulhamid ya aiko min da su kenan kamar yadda yai alkawari, mama ce take labarta min cewar a gurin kawo kayan har da mahaifiyarsa wai tai ma baba bayanin komai, wata kila shi ya turo ta dan ta wanke shi kar a ga laifinsa, wata kila kum ita ta saka kanta a tunanin ba zan fada musu gaskiyar lamarin ba, mama ta fada min har da cheque din kudi ta bawa baba ya ki ya karba, hakan kuma ba karamin dadi yai min, domin bana bukatar komai na Abdulhamid a yanzu.
Da kaina na shiga na fadawa Baba result dina cewar ban daukr da shi, yayi murna matuka dai kuma ya sake ba ni shawarar zuwa wata asibitin na sake yin gwaji. Ban watsar da shawararsa ba, na tafi kusa asibiti uku ana min gwaji result na fada cewar bana dauke da cutar, daman can ni hankali na be taba tashi akan hakan ba, ko da Abdulhamid ya fada min ban ji komai a raina kuma ban san dalilin hakan ba. A dakin da na bari cikina na koma da kaya na jera komai kamar wacan karon, a nan kam gaskiya na ji babu dadi sosai domin a takure na ke duk kuwa da kasancewar gidan ubana ne amman gidan yawa ne, ba irin gidan nan ne na masu kudi ba da za a ce kowa da dakinsa.
Ranar da na cika kwana uku da dawowa sai ga Aminu ya zo kofar gidan ya aiko da siyayya wai a bawa yaransa kuma yana kiransu, an fada min haka yake musu a yanzu duk bayan kwana biyu ko uku, ni kau na rasa dalilinsa na yin hakan bayan dacan ba haka ya saba ba. Be san ina cikin gidan ba na sani tun da ba kowa ya san aurena ya mutu ba, na san yana cikin mutunen da za su yi murna da mutuwar aurena domin ya sha fada min a lokacin da nake gidabsa cewar babu namijin da zai iya zama da ni sai shi saboda bakin halina. Fita yai da da su yai musu waya siyayyar ya hado musu da kudi sannan ya dawo da su suka shigo gida suna ta murna.
A daren mun dade muna tattaunar maganar yadda a yanzu hankalinsa ya dawo gurin yaransa, abunda ya bawa kowa mamaki a gidan mu, Mama ta karkarta min hankali da wata maganar wai ko shine mutumen da yai min fyade.
“A a mama ba Aminu ba ne, na san siffar Aminu ciki da waje, yadda yake idan ya saka tufafi kanana kaya ko manya kuma yadda yake mu'amalarsa, da shi ne da tuni zan gane, ko kadan wannan mutumen be yi min yanayi da Aminu ba, idan har shine dole zan gane, kuma me ma zai saka Aminu yai min haka, mutumen da baya kaunata, wanda ya kasa hakuri har ya dawo ya saki ni ta waya ya sake ni fa, mutumen ya wulakanta ni Mama Wallahi ko sunansa bana son ji”
“Ai saboda kiyayyar da yake miki na ke zaton haka, saboda ya jefa ki a matsala ki kasa zaman auren”
“Ko ma wanene ina rokon Allah ya bayyana min shi”
Na furta ina hawaye zuciyata cike da kuna, Mama ta amsa da amin. Mun dade muna fira a dakinta, cikin har da zancen Abdallah tana cewa da ma shi na aura ita tun farko shi ta so na aura amman na ki ni dai ban ce mata komai, saboda ban taba fada mata cewar Abdallah yayi ta neman na kashe aurena na aure shi ba....
AHMAD POV.
Tarin takardu ne a gabansa da laptop yana ta aikin cika wannan cire wannan saka wannan, aikin daya taru masa ne na satin daya shige wanda be be yi ba yake yi yau ganin yau assabar ce babu karatu.
Mug din coffee na gefensa lokaci zuwa lokaci ya ke dauka ya sha. Be tashi daga gurin ba sai da aka kira sallah azahar sannan na fito daga garden din
ya shiga part dinsa yai alwala ya nufi masallacin dake unguwar, after sun yi sallah ya shigo gida, as usual ya nufi part din Hajiya, yar aikinta kawai ya samu a falo hakan yasa ya nufi dakinta tun kan ya karasa ya jiyo muryarta ita da abokiyarta suna fira, har ya juyo da zimmar ya fasa shiga sai kuma ya juya ya shiga da zimmar ya tambaya iya Baby Namra.
Sai da ya gaishe da abokiyar Hajiyar sannan ya kalli Hajiya ya ce.
“Hajiya ina Baby?”
“Bata nan, wannan mahaifiyar Ikilima ce, Hajiya ga danki nan ko da yake ai kin san shi”
“Na san Gwarzo ai tun ba yau ba”
Cewar matar tana dariya, shi kuma ya saci kallonsa ya sake kallon Hajiya ya ce.
“Ina taje Hajiya?”
“Gidansu kawarta Namra”
Kansa ya daga sama ya saka hannunsa ya dafe.
“Oh Hajiya kin san na ce miki kar a kaita can, matar nan ba mutunci ne da ita ba wata kila ma kallon banza zata mata, shiyasa duk bibiyar da take min ban yarda na kai ta ba”
“To ina ruwan yara da lamarinku, ta sha mun kai tana son zuwa can sai a hana ta? Su fa yarane babu ruwansu da wannan, kuma dazu ta fada min cewar Momyn kawarta ba a gidan take ba”
“Hajiya dan Allah ki aika a dauko ta, ni dai bana son abotar nan, bana son yawan fitar nan da take Wallahi”
“Zan aika amman sai da yamma, abincin ka yana part dinka”
Be sake ce mata komai ba ya juyo ya baro jikin kofar, sai a yanzu yake mamaki no wonder yau weekend kuma bata zo ta dame shi ba, da yanzu tana nan ta saka shi gaba da hana shi aikin nan tace sai su yi game ko ya fita da ita kamar yadda ya saba mata every weekend. A dayan bangaren kuma yana ta ganin karfin halin Hajiya na zon hada shi aure da bazawara dan shi dai kam ya raya a ransa ba zai taba auren bazawara ba.
“Allah kadai ya sani wata kila ma yarta bata da miji, miye na wani zuwa gidan iyayen mai son yarki a yi maganar auren da ke”
Ya fada yana kokarin zama sai jin haushi yake kamar ance masa zancen aurensu ya kawo ta.
HALIMATU POV.
Washe gari ya kama Saturday babu scul sai islamiya, dan haka na tashi da wuri na gyarawa yarana suka tafi makaranta, har Amal a yanzu tana son zuwa islamiya duk wani kuiya da son jiki yanzu ta daina shi ganin babu ni a kusa da ita. Around 12 suka dawo daga islamiyar suka cire uniform suka saka kayan gida na zuba musu shinkafa da wake da akai a gidan, sai Amal ta murje ido ta kanne kafadarta ita sam ba zata ci wake ba, daman can na san Amal is not fan of wake da shimkafa amman na dauka ta canja ganin bana nan, a dole na tashi na dora mata indomie da kwai. Ina cikin kitchen din ta zo ta same ni ta rike rigata tana tabe baki.
“Momy za ki goyani”
Dariya yai ina mata kallon Mamaki.
“Wato kin ga Momy a banza ko? Amal kin fa girma yanzu ya kamata ki daina wani abun, yanzu ba kamar da kike ba”
Na ga rashin jindadin mutuwar auren a fuskarta, daman wace uwa ce zata zo auren yarta ya mutu? Balle Mama da take daukar abu ta saka a rai, su Salma da Hafiza ma da suke yan mata ba su yi aure ba abun ya dame ta balle kuma ji ace aure na biyu ya mutu. Sai dai duk da hakan ta nuna min zama da Abdulhamid din ba mafita ba ne sakin ya fi tunda har yana zargina. Da yamma Su Adnan suka dawo daga islamiya, ganina suka hau murna kamar wacce suka shekara ba su gani ba, ganin na kai har bayan i'shai yasa Namra ta fara tambaya wai nan zan kwana.
“ A nan zan kwana, yanzu na dawo kenan sai illla ma shaa Allahu”
Wani irin tsalle ta daka ta dire tana murna ta kama hannuna ta rike.
“Momy da gaske?”
Na gyada mata sai ta kara rumgume ni tana ta murna.
“Yeee mun huta Momy ta dawo”
Iya murnar da yata take na ganina a kusa da ita ya isa da tabbatar da cewar yarana sun yi marmarina duk kuwa da suna zuwa su ganni ko na gansu idan bukatar hakan ta kama, sai dai ko wane d'a yana bukatar mahaifiyarsa a kusa da shi, amman ni na bar su na auri Abdulhamid, a yau ya saka min da haka! Da tunanin abun na kwana a zuciyata har safe.
Washe gari Baba ya kira ni a dakinsa ya tambaye ni abunda ya faru, a nan na tsige masa tun daga biri har wutsiya, a ganina shi mahaifina ne be kamata na boye masa komai ba. Shi ya ba ni shawarar zuwa asibiti na sake yin gwajin hiv dan tabbatarwa. Ban yi wata wata ba na shirya na tafi gurin gwajin. Ban dawo ba sai yamma domin daga asibitin na wuce gidansu kawata Hajara, a lokacin da na labarta mata mutuwar auren sai ta fashe da kuka kamar an mata mutuwa.
“Wannan wane irin abu ne yake ta bibiyarki Halimatu? Tun farko sai da na ce ki auri Abban Ikram da yanzu duk wannan abun be faru ba kika ki”
Kai na girgiza mata.
“Wallahi sai ya faru, abunda Allah ya rubuta ya samu bawa babu mahani, na yarda da wannan”
“Allah sarki Halimatu, ga ki da tauhidi ga yarda da kaddara, Allah ya yaye miki wannan abu da yake bibiyarki”
Ta fada cikin kuka ni kuma na amsa da amin. Bayan sallah magariba na koma gida, sai na tararda tsakar gidamu cike da kayana na daki, alamar Abdulhamid ya aiko min da su kenan kamar yadda yai alkawari, mama ce take labarta min cewar a gurin kawo kayan har da mahaifiyarsa wai tai ma baba bayanin komai, wata kila shi ya turo ta dan ta wanke shi kar a ga laifinsa, wata kila kum ita ta saka kanta a tunanin ba zan fada musu gaskiyar lamarin ba, mama ta fada min har da cheque din kudi ta bawa baba ya ki ya karba, hakan kuma ba karamin dadi yai min, domin bana bukatar komai na Abdulhamid a yanzu.
Da kaina na shiga na fadawa Baba result dina cewar ban daukr da shi, yayi murna matuka dai kuma ya sake ba ni shawarar zuwa wata asibitin na sake yin gwaji. Ban watsar da shawararsa ba, na tafi kusa asibiti uku ana min gwaji result na fada cewar bana dauke da cutar, daman can ni hankali na be taba tashi akan hakan ba, ko da Abdulhamid ya fada min ban ji komai a raina kuma ban san dalilin hakan ba. A dakin da na bari cikina na koma da kaya na jera komai kamar wacan karon, a nan kam gaskiya na ji babu dadi sosai domin a takure na ke duk kuwa da kasancewar gidan ubana ne amman gidan yawa ne, ba irin gidan nan ne na masu kudi ba da za a ce kowa da dakinsa.
Ranar da na cika kwana uku da dawowa sai ga Aminu ya zo kofar gidan ya aiko da siyayya wai a bawa yaransa kuma yana kiransu, an fada min haka yake musu a yanzu duk bayan kwana biyu ko uku, ni kau na rasa dalilinsa na yin hakan bayan dacan ba haka ya saba ba. Be san ina cikin gidan ba na sani tun da ba kowa ya san aurena ya mutu ba, na san yana cikin mutunen da za su yi murna da mutuwar aurena domin ya sha fada min a lokacin da nake gidabsa cewar babu namijin da zai iya zama da ni sai shi saboda bakin halina. Fita yai da da su yai musu waya siyayyar ya hado musu da kudi sannan ya dawo da su suka shigo gida suna ta murna.
A daren mun dade muna tattaunar maganar yadda a yanzu hankalinsa ya dawo gurin yaransa, abunda ya bawa kowa mamaki a gidan mu, Mama ta karkarta min hankali da wata maganar wai ko shine mutumen da yai min fyade.
“A a mama ba Aminu ba ne, na san siffar Aminu ciki da waje, yadda yake idan ya saka tufafi kanana kaya ko manya kuma yadda yake mu'amalarsa, da shi ne da tuni zan gane, ko kadan wannan mutumen be yi min yanayi da Aminu ba, idan har shine dole zan gane, kuma me ma zai saka Aminu yai min haka, mutumen da baya kaunata, wanda ya kasa hakuri har ya dawo ya saki ni ta waya ya sake ni fa, mutumen ya wulakanta ni Mama Wallahi ko sunansa bana son ji”
“Ai saboda kiyayyar da yake miki na ke zaton haka, saboda ya jefa ki a matsala ki kasa zaman auren”
“Ko ma wanene ina rokon Allah ya bayyana min shi”
Na furta ina hawaye zuciyata cike da kuna, Mama ta amsa da amin. Mun dade muna fira a dakinta, cikin har da zancen Abdallah tana cewa da ma shi na aura ita tun farko shi ta so na aura amman na ki ni dai ban ce mata komai, saboda ban taba fada mata cewar Abdallah yayi ta neman na kashe aurena na aure shi ba....
AHMAD POV.
Tarin takardu ne a gabansa da laptop yana ta aikin cika wannan cire wannan saka wannan, aikin daya taru masa ne na satin daya shige wanda be be yi ba yake yi yau ganin yau assabar ce babu karatu.
Mug din coffee na gefensa lokaci zuwa lokaci ya ke dauka ya sha. Be tashi daga gurin ba sai da aka kira sallah azahar sannan na fito daga garden din
ya shiga part dinsa yai alwala ya nufi masallacin dake unguwar, after sun yi sallah ya shigo gida, as usual ya nufi part din Hajiya, yar aikinta kawai ya samu a falo hakan yasa ya nufi dakinta tun kan ya karasa ya jiyo muryarta ita da abokiyarta suna fira, har ya juyo da zimmar ya fasa shiga sai kuma ya juya ya shiga da zimmar ya tambaya iya Baby Namra.
Sai da ya gaishe da abokiyar Hajiyar sannan ya kalli Hajiya ya ce.
“Hajiya ina Baby?”
“Bata nan, wannan mahaifiyar Ikilima ce, Hajiya ga danki nan ko da yake ai kin san shi”
“Na san Gwarzo ai tun ba yau ba”
Cewar matar tana dariya, shi kuma ya saci kallonsa ya sake kallon Hajiya ya ce.
“Ina taje Hajiya?”
“Gidansu kawarta Namra”
Kansa ya daga sama ya saka hannunsa ya dafe.
“Oh Hajiya kin san na ce miki kar a kaita can, matar nan ba mutunci ne da ita ba wata kila ma kallon banza zata mata, shiyasa duk bibiyar da take min ban yarda na kai ta ba”
“To ina ruwan yara da lamarinku, ta sha mun kai tana son zuwa can sai a hana ta? Su fa yarane babu ruwansu da wannan, kuma dazu ta fada min cewar Momyn kawarta ba a gidan take ba”
“Hajiya dan Allah ki aika a dauko ta, ni dai bana son abotar nan, bana son yawan fitar nan da take Wallahi”
“Zan aika amman sai da yamma, abincin ka yana part dinka”
Be sake ce mata komai ba ya juyo ya baro jikin kofar, sai a yanzu yake mamaki no wonder yau weekend kuma bata zo ta dame shi ba, da yanzu tana nan ta saka shi gaba da hana shi aikin nan tace sai su yi game ko ya fita da ita kamar yadda ya saba mata every weekend. A dayan bangaren kuma yana ta ganin karfin halin Hajiya na zon hada shi aure da bazawara dan shi dai kam ya raya a ransa ba zai taba auren bazawara ba.
“Allah kadai ya sani wata kila ma yarta bata da miji, miye na wani zuwa gidan iyayen mai son yarki a yi maganar auren da ke”
Ya fada yana kokarin zama sai jin haushi yake kamar ance masa zancen aurensu ya kawo ta.
HALIMATU POV.
Washe gari ya kama Saturday babu scul sai islamiya, dan haka na tashi da wuri na gyarawa yarana suka tafi makaranta, har Amal a yanzu tana son zuwa islamiya duk wani kuiya da son jiki yanzu ta daina shi ganin babu ni a kusa da ita. Around 12 suka dawo daga islamiyar suka cire uniform suka saka kayan gida na zuba musu shinkafa da wake da akai a gidan, sai Amal ta murje ido ta kanne kafadarta ita sam ba zata ci wake ba, daman can na san Amal is not fan of wake da shimkafa amman na dauka ta canja ganin bana nan, a dole na tashi na dora mata indomie da kwai. Ina cikin kitchen din ta zo ta same ni ta rike rigata tana tabe baki.
“Momy za ki goyani”
Dariya yai ina mata kallon Mamaki.
“Wato kin ga Momy a banza ko? Amal kin fa girma yanzu ya kamata ki daina wani abun, yanzu ba kamar da kike ba”