Sashe 45
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta karasa da fuskar tausayi, ni kam tuni hawaye sun cika min ido har sun fara wanke min fuska. Ban sake maida hankali akan duk wata fira da suke da Inna ba, domin tunani ya rabu biyu, makomata na ke hangowa da kuma kokarin wanke Abdallah da zuciyata ke yi. Anya zai iya aikata kisa? Taya mutum mai aikin kamarsa ma zai iya shiga fashi da makami? Me zai kai shi shiga? Yes wata kila ba shiga yai ba gaba daya ba, what if labawa yai a cikinsu saboda ya samu biyan bukatarsa? Can kuma wani bangare na zuciyata ya jefo min wata tambayar? Miyasa sai Abdallah na ke zargi? Mi zai saka dan'uwa yai ma matar dan'uwansa haka? Miyasa be min a lokacin da nake gidan Aminu ba sai a nan? Saboda a can yana ganin zan iya fitowa wata rana kamar haka na aureshi amman a yanzu babu wannan damar? Na riga na auri dan'uwansa dan uwan ma twins brother dinsa....
Na kasa yarda cewar shi kadai din ne, zuciyata kuma ta kasa natsuwa cewar ba shi din ne ba, na kasa zargin kowa sai shi.
Sai da Hajiya ta fice sannan na samu natsuwa da sukunin mikewa tsaye na nufi gurin windows domin ba Hajiya kadai ba, Inna bata cikin dakin a wannan lokacin, tsakanin kalaman Hajiya da zargin Abdallah da kuma tambayayin da mutumen yai min da kalaman Hajiya sai na rasa wanne zan fara tunani? Wasu abubuwa na ji suna min yawo a cikin kai ga wani uban nauyi da zuciyata tai. Kaina na jingina jikin window ya lumshe ido ina jin kamar zan samu mafita a nan. Ajiyar zuciya na sauke ya fi a kirga sannan bude idon da ke cike da hawaye ina ta kallon mutane da ke kai kawo harabar asibitin, duk wanda na hango burge ni yake domin na san damuwarsa ba ta kai kamar tawa ba, murmushi nake hangowa a fuskar wasu wasu kuma dariya na ke gani a fuskarsu abunda ni na gagara samu.
Wani na soma hangowa kamar Kabir kamar ba shi ba, sai da na kara maida hankalina sosai gurin kallonsa da yanayinsa na hauka da yake ciki ya tabbatar min da Kabir din ne, har yanzu tsingiltar take yana tafiya ya nufo cikin asibitin, sai ga securities din da sauri su ka zo suka rika shi suka fitar da shi daga asibitin.
Neman natsuwata da damuwata nai na rasa, gaba daya sai hankalina na koma gurin Kabir din. Ban san kuka nake mai sauti ba, har dai da yarana suka shogo na ji muryar Adnan yana min magana.
“Momy kuke kike yi?”
Juyowa nai na kallesu na gyada masa kai alamar eh kukan nake, domin a bayyana hake kuma ba zan iya boye shi ba a wannan lokacin, gaba dayansu suka fashe da kuka har Amal da take karama ganin nima ina kuka, risinawa nai a gurin na zauna a kasa sai suka zo kusa da ni suka zauna. Ni da su aka mai rarrashin wani, wani bangare na rayuwata ta baya ya fara fado min a rai, a lokacin da na samu cikina na farko cikin Adnan, ina farinciki ina jindadi saboda ina son ya'ya, amman Aminu ya nuna min ba haka ba sai dai a zubar shi be shirya haihuwa yanzu ba, rana za su tsufar da shi, za su hana shi shakatawa yadda ya kamata, daga lokacin komai ya sauya min na fara fuskantar kalubalen na rayuwa kala kala har na haifi Amal. Babu sunan da be kira ni da shi ba, yace min ina ta haihuwa kamar kaza, ina ta tara masa yaya saboda idan ya mutu na co gadonsa. Daga lokacin da na baro gidansa na yi zaton damuwar ta wuce na yi tsammani dadi zanji a gidan Abdulhamid ashe ba haka ne ba, wahalar bata kare ba damuwar ba ta wuce ba.
“Haba Halimatu ya za ki saka yaya a gaba kina kuka suna kuka? Miye haka?”
Maganar Inna ce ta saka na dawo hayyacina har na goge hawayena na mike tsaye na hau saman gadon na kwanta.
ABDALLAH POV.
Yana fitowa daga dakin theater ya nufi wani dakin dan tsabbace jikinsa da kuma cire tufafin da ya fito da su daga tiyatar, sai da ya cire komai ya wanke hannunsa sannan ya nufo office dinsa.
Zaunawa a saman kujerarsa sai ya ji kamar be zauna ba, sai da ya gyara zamansa sai yaji ba zaman ne abunda yake bukata ba. Tsaye yai dafe da kansa yana motsawa a hankali sai hawaye suka sauko masa.
“Why....?”
Jinginawa yai da ginar office din yana hawaye, he can't remember when last yai hawaye ko ya shiga damuwa irin haka, ko a lokacin da Halimatu ta auri dan'uwansa be samu kansa cikin damuwa kamar haka ba.
“I'm such a stupid.... Me yake damuna wai? What is wrong with me?”
Ya daga kansa sama hana hawaye tare da kuka marar sauti.
“Miyasa jabawata za ta zo a nan? Mi nai? Oh my God Allah kai kadai kasan dalilin da ya saka ka dora min son Halimatu....”
Juyawa yai yana kallon wayarsa da ke ringing.
“Kuskure ne abunda na ke yi, be kamata na bar Abdulhamid ya gano komai ba”
Ya busar da iskar bakinsa sannan ya nufi gaban teburin ya dauki tissue paper ya goge fuskarsa. Kiran na sake shigowa yai picking.
“Hello Hajiya”
“Na'am ya aikin?”
“Al-hamdulillah”
“Husaini na ce ka saka a yi ma Halimatu gwajin ciki da na hiv”
Mamaki ne ya cika fuskarsa.
“Why?”
“Why? Kamar ba ka san abunda ya faru ba?”
“Amman Hajiya kin ce ita da kanta ta ce ba su mata komai ba”
“Ai to fada za tai? Ai ba zata fada ba”
“Hajiya be kamata ki yi wannan maganar a yanzu ba, za ki kara sakata cikin damuwa ne, kar ma ki kawo ma Abdulhamid wannan tunanin dan Allah, ki aje wannan maganar na gafe”
“Wallahi ba zan aje ba, dan ba zan yarda ta cutar min da ɗa ba”
Tana fada hakan ta kashe wayar. Zaunawa yai a kujerar ya dafe kansa.
HALIMATU POV.
Da yamma Abdulhamid ya shigo asibitin, shi ma na ga damuwa da tausayi a fuskarsa da kuma kulawa a mu'amalarsa. Ni kuma na kasa sakewa da shi ko da na minti daya, irin kallon da nake ma Aminu na ke masa a yanzu. Bayan magariba polices suka zo suka suna min bincike sai a lokacin na yi dauriyar da na bude bakina na rika amsa musu tambayoyinsu, sun tambaya ko zan iya gane mutane na amsa musu da a a domin fuskokinsu a rufe suke kuma muryarsu ma a boye take, sun dauki duk bayanin da ya kamata su dauka sannan suka tafi.
Kwana na biyu a asibiti suka sallame ni ganin na samun sauki, sai dai a cikin magunguna da suka ba ni har da na hawan jini kamar yadda suka fada min cewar ina da shi, a ranar da zan koma gidan mijina sai na ji kamar zan koma a cikin wata duniyar ta dabam, domin a asibitin ina ganin mutane familyna abokaina da kuma yayana suna cire min kewa ba kamar a yanzu ba da zan koma ni kadai.
An gyara komai a gidan kamar babu wanda ya shigo, kofar ma an canja ta kamar yadda aka canja gate din, har na shiga dakina Abdulhamid be ce min komai ba, ni ma kuma ban ce masa ba, daman kuma ni me zan fada masa? Ce masa zan yi ka yarda da ni? Ko na tausaya min? Ko kuma ya zo mu yi kuka tare? A daren ranar ji nai kamar ba zan iya bachi ba dan haka na tashi nemam maganina da ke saka ni bachi amman ban samu ba. Na tsorota sosai rashin ganin maganin da nai domin na san akwai wanda ya ga maganin har ya saka hannu ya dauka. Wanin kuma ba zai wuce Abdulhamid ba domin shi kadai nake da tabbacin zai iya bincika duk abunda yake so a gidan nan.
A haka na kwana bachi ba bachi ba, minti daya biyu uku na farka, kamin ya sake daukata kuma sai an dade, da safe shi ya shirya mana abun karyawa da kansa ya shigo ya tashe ni na fito falo, amman sai na kasa cin komai, shi kan ya ci biredi ya sha tea sannan ya tambaye ni akwai wata matsala? Ko abunda na ke bukata na girgiza masa kai.
“Okay zan aiko miki da takeway da rana, da dare ma idan za a dawo zan siyo mana wani abu, me kika so ki ci?”
“Bana bukatar komai”
Kallo kawai yai ya dauke kai ya shiga dakinsa ya shirya ya fita. Daga lokacin sai zanantakewar mu ta sake sauya sabon salo baya bari nai girki sai dai ya siyo mana abinci, na sa yana min hakan ne domin ya nuna min ya damu da ni bayan kuma ya kasa kwanta a gadon da nake kwana kamar da, ya kasa sakewa da ni kamar da, sai yawan kallona da yake kamar mai tunani, zuciyata na raya min be natsu da ni ba, wani lokacin ina jin kamar barin gidan shine mafita a agare ni da kuma shi, Har nai sati da sallamowa Hajiyarsa bata sake daga waya ta kira da sunan ta tambaya ya jikina ba balle har ta zo ko ta aiko a dubani, Abdallah ma tun a lokacin da ya miko min waya a asibiti ban sake jin duriyarsa ba, ba ma wacce ta fi ba ni mamaki kamar Suwaiba matarsa wacce bata zo ba kuma bata kirani ta tambayi lafiyata ba balle tai min jaje, abun har ya daure min kai wata kila kuma ita ta fara bin bayan Hajiya ne wajen tsanata duk da ban san na musu komai ba, ni kam bana dacewa da iyyen miji, haka uwar Aminu da kanensa suka tsane ni, ko da yake bana da sa'a da dacen rayuwa shiyasa saka hakan yake faruwa da ni.
Na kasa yarda cewar shi kadai din ne, zuciyata kuma ta kasa natsuwa cewar ba shi din ne ba, na kasa zargin kowa sai shi.
Sai da Hajiya ta fice sannan na samu natsuwa da sukunin mikewa tsaye na nufi gurin windows domin ba Hajiya kadai ba, Inna bata cikin dakin a wannan lokacin, tsakanin kalaman Hajiya da zargin Abdallah da kuma tambayayin da mutumen yai min da kalaman Hajiya sai na rasa wanne zan fara tunani? Wasu abubuwa na ji suna min yawo a cikin kai ga wani uban nauyi da zuciyata tai. Kaina na jingina jikin window ya lumshe ido ina jin kamar zan samu mafita a nan. Ajiyar zuciya na sauke ya fi a kirga sannan bude idon da ke cike da hawaye ina ta kallon mutane da ke kai kawo harabar asibitin, duk wanda na hango burge ni yake domin na san damuwarsa ba ta kai kamar tawa ba, murmushi nake hangowa a fuskar wasu wasu kuma dariya na ke gani a fuskarsu abunda ni na gagara samu.
Wani na soma hangowa kamar Kabir kamar ba shi ba, sai da na kara maida hankalina sosai gurin kallonsa da yanayinsa na hauka da yake ciki ya tabbatar min da Kabir din ne, har yanzu tsingiltar take yana tafiya ya nufo cikin asibitin, sai ga securities din da sauri su ka zo suka rika shi suka fitar da shi daga asibitin.
Neman natsuwata da damuwata nai na rasa, gaba daya sai hankalina na koma gurin Kabir din. Ban san kuka nake mai sauti ba, har dai da yarana suka shogo na ji muryar Adnan yana min magana.
“Momy kuke kike yi?”
Juyowa nai na kallesu na gyada masa kai alamar eh kukan nake, domin a bayyana hake kuma ba zan iya boye shi ba a wannan lokacin, gaba dayansu suka fashe da kuka har Amal da take karama ganin nima ina kuka, risinawa nai a gurin na zauna a kasa sai suka zo kusa da ni suka zauna. Ni da su aka mai rarrashin wani, wani bangare na rayuwata ta baya ya fara fado min a rai, a lokacin da na samu cikina na farko cikin Adnan, ina farinciki ina jindadi saboda ina son ya'ya, amman Aminu ya nuna min ba haka ba sai dai a zubar shi be shirya haihuwa yanzu ba, rana za su tsufar da shi, za su hana shi shakatawa yadda ya kamata, daga lokacin komai ya sauya min na fara fuskantar kalubalen na rayuwa kala kala har na haifi Amal. Babu sunan da be kira ni da shi ba, yace min ina ta haihuwa kamar kaza, ina ta tara masa yaya saboda idan ya mutu na co gadonsa. Daga lokacin da na baro gidansa na yi zaton damuwar ta wuce na yi tsammani dadi zanji a gidan Abdulhamid ashe ba haka ne ba, wahalar bata kare ba damuwar ba ta wuce ba.
“Haba Halimatu ya za ki saka yaya a gaba kina kuka suna kuka? Miye haka?”
Maganar Inna ce ta saka na dawo hayyacina har na goge hawayena na mike tsaye na hau saman gadon na kwanta.
ABDALLAH POV.
Yana fitowa daga dakin theater ya nufi wani dakin dan tsabbace jikinsa da kuma cire tufafin da ya fito da su daga tiyatar, sai da ya cire komai ya wanke hannunsa sannan ya nufo office dinsa.
Zaunawa a saman kujerarsa sai ya ji kamar be zauna ba, sai da ya gyara zamansa sai yaji ba zaman ne abunda yake bukata ba. Tsaye yai dafe da kansa yana motsawa a hankali sai hawaye suka sauko masa.
“Why....?”
Jinginawa yai da ginar office din yana hawaye, he can't remember when last yai hawaye ko ya shiga damuwa irin haka, ko a lokacin da Halimatu ta auri dan'uwansa be samu kansa cikin damuwa kamar haka ba.
“I'm such a stupid.... Me yake damuna wai? What is wrong with me?”
Ya daga kansa sama hana hawaye tare da kuka marar sauti.
“Miyasa jabawata za ta zo a nan? Mi nai? Oh my God Allah kai kadai kasan dalilin da ya saka ka dora min son Halimatu....”
Juyawa yai yana kallon wayarsa da ke ringing.
“Kuskure ne abunda na ke yi, be kamata na bar Abdulhamid ya gano komai ba”
Ya busar da iskar bakinsa sannan ya nufi gaban teburin ya dauki tissue paper ya goge fuskarsa. Kiran na sake shigowa yai picking.
“Hello Hajiya”
“Na'am ya aikin?”
“Al-hamdulillah”
“Husaini na ce ka saka a yi ma Halimatu gwajin ciki da na hiv”
Mamaki ne ya cika fuskarsa.
“Why?”
“Why? Kamar ba ka san abunda ya faru ba?”
“Amman Hajiya kin ce ita da kanta ta ce ba su mata komai ba”
“Ai to fada za tai? Ai ba zata fada ba”
“Hajiya be kamata ki yi wannan maganar a yanzu ba, za ki kara sakata cikin damuwa ne, kar ma ki kawo ma Abdulhamid wannan tunanin dan Allah, ki aje wannan maganar na gafe”
“Wallahi ba zan aje ba, dan ba zan yarda ta cutar min da ɗa ba”
Tana fada hakan ta kashe wayar. Zaunawa yai a kujerar ya dafe kansa.
HALIMATU POV.
Da yamma Abdulhamid ya shigo asibitin, shi ma na ga damuwa da tausayi a fuskarsa da kuma kulawa a mu'amalarsa. Ni kuma na kasa sakewa da shi ko da na minti daya, irin kallon da nake ma Aminu na ke masa a yanzu. Bayan magariba polices suka zo suka suna min bincike sai a lokacin na yi dauriyar da na bude bakina na rika amsa musu tambayoyinsu, sun tambaya ko zan iya gane mutane na amsa musu da a a domin fuskokinsu a rufe suke kuma muryarsu ma a boye take, sun dauki duk bayanin da ya kamata su dauka sannan suka tafi.
Kwana na biyu a asibiti suka sallame ni ganin na samun sauki, sai dai a cikin magunguna da suka ba ni har da na hawan jini kamar yadda suka fada min cewar ina da shi, a ranar da zan koma gidan mijina sai na ji kamar zan koma a cikin wata duniyar ta dabam, domin a asibitin ina ganin mutane familyna abokaina da kuma yayana suna cire min kewa ba kamar a yanzu ba da zan koma ni kadai.
An gyara komai a gidan kamar babu wanda ya shigo, kofar ma an canja ta kamar yadda aka canja gate din, har na shiga dakina Abdulhamid be ce min komai ba, ni ma kuma ban ce masa ba, daman kuma ni me zan fada masa? Ce masa zan yi ka yarda da ni? Ko na tausaya min? Ko kuma ya zo mu yi kuka tare? A daren ranar ji nai kamar ba zan iya bachi ba dan haka na tashi nemam maganina da ke saka ni bachi amman ban samu ba. Na tsorota sosai rashin ganin maganin da nai domin na san akwai wanda ya ga maganin har ya saka hannu ya dauka. Wanin kuma ba zai wuce Abdulhamid ba domin shi kadai nake da tabbacin zai iya bincika duk abunda yake so a gidan nan.
A haka na kwana bachi ba bachi ba, minti daya biyu uku na farka, kamin ya sake daukata kuma sai an dade, da safe shi ya shirya mana abun karyawa da kansa ya shigo ya tashe ni na fito falo, amman sai na kasa cin komai, shi kan ya ci biredi ya sha tea sannan ya tambaye ni akwai wata matsala? Ko abunda na ke bukata na girgiza masa kai.
“Okay zan aiko miki da takeway da rana, da dare ma idan za a dawo zan siyo mana wani abu, me kika so ki ci?”
“Bana bukatar komai”
Kallo kawai yai ya dauke kai ya shiga dakinsa ya shirya ya fita. Daga lokacin sai zanantakewar mu ta sake sauya sabon salo baya bari nai girki sai dai ya siyo mana abinci, na sa yana min hakan ne domin ya nuna min ya damu da ni bayan kuma ya kasa kwanta a gadon da nake kwana kamar da, ya kasa sakewa da ni kamar da, sai yawan kallona da yake kamar mai tunani, zuciyata na raya min be natsu da ni ba, wani lokacin ina jin kamar barin gidan shine mafita a agare ni da kuma shi, Har nai sati da sallamowa Hajiyarsa bata sake daga waya ta kira da sunan ta tambaya ya jikina ba balle har ta zo ko ta aiko a dubani, Abdallah ma tun a lokacin da ya miko min waya a asibiti ban sake jin duriyarsa ba, ba ma wacce ta fi ba ni mamaki kamar Suwaiba matarsa wacce bata zo ba kuma bata kirani ta tambayi lafiyata ba balle tai min jaje, abun har ya daure min kai wata kila kuma ita ta fara bin bayan Hajiya ne wajen tsanata duk da ban san na musu komai ba, ni kam bana dacewa da iyyen miji, haka uwar Aminu da kanensa suka tsane ni, ko da yake bana da sa'a da dacen rayuwa shiyasa saka hakan yake faruwa da ni.