Sashe 89
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Oga ya kamata ki yiwa godiya”
“Dan Allah ina rokon alfarma”
“Na san kai ma oganka ne, amman kuna da kyakkyawar fahimta wata kila za ka iya yi masa magana ya ji, dan Allah ka saka ba ki ya saki matar da ya saka a ka kulle”
“Ya sake ta ai, tun dazun mijinta ya tafi da ita”
“Da gaske? Amman cewa yai ba zai barta ta tafi ba”
“Gaskiya tun dazun aka wuce da ita”
Dan murmushi nai na juya ina kallon office din. Shi kuma ya juya fice ya bar a gurin tsaye n rasa abunda zan yi murna ko kuka ko mamaki?
Kasa komai nai a cikin office din sai kawai nai zaune ina ta kallon office din, misalin daya da mintuna wata ta shigo da abinci ta ba aje min, takeway ne na jalof da naman kaza a ciki. Nikam ban ci ba duk kuwa da kasancewar ni kadai ce a dakin sai na saka abina a jaka.
Biyu na yi na shiga bandakin da ke office din nai alwala na fito nai sallah sannan na dauki wayata na kira gida na fadawa Hafiza ta fadawa Mama an canja min aiki dan haka yau sai 5pm zan dawo.
Har karfe uku ban duba email din ba ban kuma tura komai ba, har sai da Yunus din ya sake dawowa ya nuna min yadda ake da kuma wandanda ya kamata a turawa Ahmad din.
Karfe biyar na yi na dauki jakata na fito daga office din, ko da na fito Rilwal da Blessed basa gurin sun gama aikinsu sun tafi.
A lokacin da na isa gida na labartawa Mama da dukan yan gidan abunda ya faru tsakanina da Ahmd da kuma abunda Suwaiba tai, a nan Hafiza take fadar wai Suwaiba ta kirata kwanan baya tana tambayar inda nake aiki ita kuma ta fada mata ba ta yi tunanin wani abun ba ashe dan ta samu zuwa ta ci min mutunci ne.
Su namra na bawa abincin office din, suna ta murna sun ga har da nama a cikin gurin rabon abun har ya so zame musu fada sai da Husna ta shiga tsakani.
Bayan na huta na ci abincin da aka girka gida, na watsa ruwa na sake shiryawa cikin wasu tufafin na nufi bankin da ke kusa da mu, kudin gasar da na ci nake son cirowa na samma kowa wani abu a ciki sannan nai sauran lalurorin da suke gabana. 200,000 na ciro na saka a jaka ta cikin tsoro domin a lokacin an fara kiran sallah sai nake ganin kamar akwai wasu a biye da ni duk kuwa da ba ni kadai na ciri kudi a atm din ba.
Ina yin gaba kadan sai wata farar mota mai bakin gilashi ta faka a gabana, na san ba zai wuce Abraham ba amman hakan be saka ni jin tsoro ba har sai da ya bude motar ya fito.
“Ki daina cirar kudi a atm idan yamma yayi, wani zai iya sa miki ido wasu ma ba diban kudin suka je yi ba kallon masu cire kudin suka je yi”
Ban ce masa komai ba nai gaba kamar zan wuce sai ya saka ya cin min.
“Kin gani jin labarin ki ya kara min kaunarki, kuma ya kara kafafa min guiwar aurenki, ni kadai zan rayu dake ba wata kyama ba wani tunani, ina da kudi zan sakar miki su ki jidadin rayuwarki”
“Ba kudi ne jindadin rayuwa ba, da su ne da masu kudin ba su shiga kunci ba, ni farinciki nake nema da kwanciyar hankali”
“Na sani shiyasa zan baki ai”
“Baka isa ka bani farinciki ba, baka isa ka keta min haddi da aurena ba har nai ciki yanzu kuma ka biyo ni kace zaka aureni, addininmu dabam al'adarmu dabam, baka san zafin da nake ji a raina ba, baka san yadda mace take ji idan an keta haddinta ba, saboda kai namiji ne, mace tana jin matukar bakinciki ko hannunta a rike balle a keta haddinta, kasan saboda me? Saboda martabarta kimarta mutuncinta jindadinta farincikinta yana a nan ne, to kai ka zubar min da duka wannan ka saka uwar mijina da mijin da ya sake ni suna min kallon karuwa wacce ta zubar da mutuncinta tai fasikanci da wani namijin har ta samu ciki, wannan tabon ba zai taba gogewa ba, idan kuma ka zo ne saboda ka kashe ni da bakincikin kallonka da nake kana da dama”
Na karasa cikin kuka.
“Idan nisanta kaina da ke zai saka ki farinciki, i will do that, amman bana da niyar saka ki bakinciki, sai dai sama miki farinciki ada bakincikin fyaden da nai miki kawai yake damuna, amman a yanzu har da rayuwar kuncin da kike ciki, kina da zuciya mai kyau kuma kina da hakuri”
Bayan ya fadi haka ya bude motarsa ya shiga yai mata key ya bar ni a gurin tsaye. Sai da na daina hango motarsa sannan tari napep na shiga. Ko da na isa gida har an gama magariba, bayan na sallame mai napep na lura da motar Abdallah, na yi zaton yana cikin gidan ne sai ji nai ya kirani, ina juyowa na hango shi ya fito hanyar masallacin unguwar sai ya nufi gurin motarsa ya tsaya, hakan yasa nima na karasa kusa da shi na tsaya.
“Ki yi hakuri da abunda Suwaiba tai miki, ban san yadda akai taje gurin ba kuma ban fada mata cewar kina kawo min abinci ba, kin san zuciya kowa da irin tasa ba tai tunani ba a lokacin da ta aikata abunda ta aikata dazun kuma ban jidadi ba”
“Tana da gaskiya Abdallah, tana tsoron wata ta karbe nata miji mai karamci da sanin ya kamata, mai kula, mai tausayi, mai taka tsantsan akan komai, kai kadai ka yarda da ni Abdallah baka taba yarda cewar na aikata laifi ba, kai kadai ka yarda cewar ban aikata zina, kai ne kadai ka yarda fyade ka min har na samu ciki, amman Hajiyarka da Abdulhamid ba su yarda da ni ba, kai na zarga a lokacin da aka min fyaden kuma na fada maka, amman gujeni ba baka kyamace ni ba, baka fasa so na ba, baka kasa taimaka min ba, so na be taba sa ka nemi aikata alfasha da ni ba, baka taba kyamar yayana ba, Wallahi ina son ka Abdallah ina son ka har kasan raina”
Na karasa cikin kuka mai tsanani. Har ga Allah ban taba jin son wani da namijin a raina kamar yadda nake jin Abdallah a raina ba, sai bayan komai ya lalace na gano shine mutumen da ya dace da ni.
“Ke dai ba kya gajiya da kuka, shiga ciki Suwaiba tana jiranki”
“Ina son na fada maka wani abu, mutumen da yai min fyade, ya dawo yan so na”
“Wooo What....!”
Ya furta da karfi muryarsa na amayar da mamakin da ke cikinsa.
“Waye? A ina ya ganki?”
“Labari mai tsawo ba zai yiyu a yanzu ba”
“Waye shi kin san shi ne?”
Na girgiza kai.
“Ban san shi ba, sunansa Abraham, dan sanda ne, yana aiki a unguwar gwaza, kuma shi ba musulmi ba ne”
Na daga kaina sama ina shanye kuka.
“Abraham.....”
Ya maimaita sunan sannan ya jinjina kansa.
“Shiga ciki za ku yi magana da Suwaiba”
Na gyada kai alamar gamsuwa sannan na saka hannuna na share hawayena sannan na juya na nufi gidanmu. Ko da na shiga na samu Suwaiba zaune falon mama tana ta rutsar kuka kamar ba ita ba, tana ganina ta soma bani hakuri tana fadin na yafe mata, a iya sanina Abdallah baya duka balle nace dukanta yai ya cilasta mata zuwa ta ba ni hakuri sai dai idan wani abun ya fada mata ko kuma cilastata yai.
7/21/21, 10:47 PM - Buhainat: I think you'd like this story: "GOBE NA (My Tomorrow)" by KhadeejaCandy on Wattpad https://www.wattpad.com/story/247701926?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=story_info&wp_page=story_details_button&wp_uname=KhadeejaCandy&wp_originator=ZkyWKvWuHXhIRzZDEluZ%2BuUXayIbDBikXAQA%2BM4xeAsJY%2Fh9rtovTCoQphCdFYUPM4K1nHTquOLcFfifZUhwZ0RRyERddTi4AY1OYORg8gUhN9fNU%2FLr6t3SMGO9O8M2
*GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
4️⃣5️⃣
ABDALLAH POV.
Zuciyarsa cike take da tunanin abunda Halima ta fada masa, ba sau daya ba ya sha jin sunan Abraham a gurin Abdulhamid, sai dai da kamar wuya ya iya fada mta kai tsaye idan har shi din ne? Mi zai saka ya tonawa kansa asiri? Mi mai zai saka yayi mata fyaden tun farko? Miyasa yai shigar yan fashi? Sai dai ya yarda Halima ba zata masa karya ba, tun da ita din bata san Abraham ba, kuma bata san cewa shi din ba musulmi ne ba, idan har ba shi ya fada mata ba.
Yana tsaye jikin motar Suwaiba ta fito daga cikin gidansu Halimatu ta nufo i da yake da hijabinta har kasa, be tsaya jiran ta karaso ba ya bude side dinsa ya zauna yai ma motar key tana shiga ya tashi motar.
Ta yi zaton hanyar gida zai nufa sai ta ga ya dauki hanyar family house dinsu.
“Doc baka hakura ba?”
Ta tambaya cikin kuka, ko kallon inda take be yi ba har ya shiga titin unguwarsu.
“Na ba ka hakuri kace ita zan bawa hakuri ita ma na bata, amman be isa ya saka ka yafe min dan abunda nai ba”
Sai a lokacin ya kalleta.
“Dan abunda kika yi? Da ne ma? Kin san irin kuncin da Halima take fuskata kike neman kara mata wani? Ko ba u so a tsakanina da ita ai ita din yar'uwata ce kuma kin sani, ko dan yan'uwantakan da ke tsakaninmu be isa ya saka ki raga mata ba ko da ma ace ita ce ta nemi fada da ke? Ko karuwata ce ai ya cancanci ki kyaleta saboda mutuncina, amman wai dan shashanci da aurena akanki ki shiga public place kamar nn kina magana any how, idan auren zan yi kin isa ki hana ni ne ko fadan ki sai ya saka na fasa?”
Tun da ya fara fadan take kuka har ya faka bakin kofar gidansu.
“Da gaske sakina din za ka yi?”
“Ko dai ban sake ki ba, dole na samawa su Inteesar wata uwar mai tarbiya da sanin ya kamata”
Da sauri ta hade hannayenta.
“Dan Allah kai hakuri, ka sake ni idan sakin zai saka ka huce haushi daga baya sai ka maida ni amman karka kara aure dan Allah, wallahi na bari ba zan sake ba”
“Dan Allah ina rokon alfarma”
“Na san kai ma oganka ne, amman kuna da kyakkyawar fahimta wata kila za ka iya yi masa magana ya ji, dan Allah ka saka ba ki ya saki matar da ya saka a ka kulle”
“Ya sake ta ai, tun dazun mijinta ya tafi da ita”
“Da gaske? Amman cewa yai ba zai barta ta tafi ba”
“Gaskiya tun dazun aka wuce da ita”
Dan murmushi nai na juya ina kallon office din. Shi kuma ya juya fice ya bar a gurin tsaye n rasa abunda zan yi murna ko kuka ko mamaki?
Kasa komai nai a cikin office din sai kawai nai zaune ina ta kallon office din, misalin daya da mintuna wata ta shigo da abinci ta ba aje min, takeway ne na jalof da naman kaza a ciki. Nikam ban ci ba duk kuwa da kasancewar ni kadai ce a dakin sai na saka abina a jaka.
Biyu na yi na shiga bandakin da ke office din nai alwala na fito nai sallah sannan na dauki wayata na kira gida na fadawa Hafiza ta fadawa Mama an canja min aiki dan haka yau sai 5pm zan dawo.
Har karfe uku ban duba email din ba ban kuma tura komai ba, har sai da Yunus din ya sake dawowa ya nuna min yadda ake da kuma wandanda ya kamata a turawa Ahmad din.
Karfe biyar na yi na dauki jakata na fito daga office din, ko da na fito Rilwal da Blessed basa gurin sun gama aikinsu sun tafi.
A lokacin da na isa gida na labartawa Mama da dukan yan gidan abunda ya faru tsakanina da Ahmd da kuma abunda Suwaiba tai, a nan Hafiza take fadar wai Suwaiba ta kirata kwanan baya tana tambayar inda nake aiki ita kuma ta fada mata ba ta yi tunanin wani abun ba ashe dan ta samu zuwa ta ci min mutunci ne.
Su namra na bawa abincin office din, suna ta murna sun ga har da nama a cikin gurin rabon abun har ya so zame musu fada sai da Husna ta shiga tsakani.
Bayan na huta na ci abincin da aka girka gida, na watsa ruwa na sake shiryawa cikin wasu tufafin na nufi bankin da ke kusa da mu, kudin gasar da na ci nake son cirowa na samma kowa wani abu a ciki sannan nai sauran lalurorin da suke gabana. 200,000 na ciro na saka a jaka ta cikin tsoro domin a lokacin an fara kiran sallah sai nake ganin kamar akwai wasu a biye da ni duk kuwa da ba ni kadai na ciri kudi a atm din ba.
Ina yin gaba kadan sai wata farar mota mai bakin gilashi ta faka a gabana, na san ba zai wuce Abraham ba amman hakan be saka ni jin tsoro ba har sai da ya bude motar ya fito.
“Ki daina cirar kudi a atm idan yamma yayi, wani zai iya sa miki ido wasu ma ba diban kudin suka je yi ba kallon masu cire kudin suka je yi”
Ban ce masa komai ba nai gaba kamar zan wuce sai ya saka ya cin min.
“Kin gani jin labarin ki ya kara min kaunarki, kuma ya kara kafafa min guiwar aurenki, ni kadai zan rayu dake ba wata kyama ba wani tunani, ina da kudi zan sakar miki su ki jidadin rayuwarki”
“Ba kudi ne jindadin rayuwa ba, da su ne da masu kudin ba su shiga kunci ba, ni farinciki nake nema da kwanciyar hankali”
“Na sani shiyasa zan baki ai”
“Baka isa ka bani farinciki ba, baka isa ka keta min haddi da aurena ba har nai ciki yanzu kuma ka biyo ni kace zaka aureni, addininmu dabam al'adarmu dabam, baka san zafin da nake ji a raina ba, baka san yadda mace take ji idan an keta haddinta ba, saboda kai namiji ne, mace tana jin matukar bakinciki ko hannunta a rike balle a keta haddinta, kasan saboda me? Saboda martabarta kimarta mutuncinta jindadinta farincikinta yana a nan ne, to kai ka zubar min da duka wannan ka saka uwar mijina da mijin da ya sake ni suna min kallon karuwa wacce ta zubar da mutuncinta tai fasikanci da wani namijin har ta samu ciki, wannan tabon ba zai taba gogewa ba, idan kuma ka zo ne saboda ka kashe ni da bakincikin kallonka da nake kana da dama”
Na karasa cikin kuka.
“Idan nisanta kaina da ke zai saka ki farinciki, i will do that, amman bana da niyar saka ki bakinciki, sai dai sama miki farinciki ada bakincikin fyaden da nai miki kawai yake damuna, amman a yanzu har da rayuwar kuncin da kike ciki, kina da zuciya mai kyau kuma kina da hakuri”
Bayan ya fadi haka ya bude motarsa ya shiga yai mata key ya bar ni a gurin tsaye. Sai da na daina hango motarsa sannan tari napep na shiga. Ko da na isa gida har an gama magariba, bayan na sallame mai napep na lura da motar Abdallah, na yi zaton yana cikin gidan ne sai ji nai ya kirani, ina juyowa na hango shi ya fito hanyar masallacin unguwar sai ya nufi gurin motarsa ya tsaya, hakan yasa nima na karasa kusa da shi na tsaya.
“Ki yi hakuri da abunda Suwaiba tai miki, ban san yadda akai taje gurin ba kuma ban fada mata cewar kina kawo min abinci ba, kin san zuciya kowa da irin tasa ba tai tunani ba a lokacin da ta aikata abunda ta aikata dazun kuma ban jidadi ba”
“Tana da gaskiya Abdallah, tana tsoron wata ta karbe nata miji mai karamci da sanin ya kamata, mai kula, mai tausayi, mai taka tsantsan akan komai, kai kadai ka yarda da ni Abdallah baka taba yarda cewar na aikata laifi ba, kai kadai ka yarda cewar ban aikata zina, kai ne kadai ka yarda fyade ka min har na samu ciki, amman Hajiyarka da Abdulhamid ba su yarda da ni ba, kai na zarga a lokacin da aka min fyaden kuma na fada maka, amman gujeni ba baka kyamace ni ba, baka fasa so na ba, baka kasa taimaka min ba, so na be taba sa ka nemi aikata alfasha da ni ba, baka taba kyamar yayana ba, Wallahi ina son ka Abdallah ina son ka har kasan raina”
Na karasa cikin kuka mai tsanani. Har ga Allah ban taba jin son wani da namijin a raina kamar yadda nake jin Abdallah a raina ba, sai bayan komai ya lalace na gano shine mutumen da ya dace da ni.
“Ke dai ba kya gajiya da kuka, shiga ciki Suwaiba tana jiranki”
“Ina son na fada maka wani abu, mutumen da yai min fyade, ya dawo yan so na”
“Wooo What....!”
Ya furta da karfi muryarsa na amayar da mamakin da ke cikinsa.
“Waye? A ina ya ganki?”
“Labari mai tsawo ba zai yiyu a yanzu ba”
“Waye shi kin san shi ne?”
Na girgiza kai.
“Ban san shi ba, sunansa Abraham, dan sanda ne, yana aiki a unguwar gwaza, kuma shi ba musulmi ba ne”
Na daga kaina sama ina shanye kuka.
“Abraham.....”
Ya maimaita sunan sannan ya jinjina kansa.
“Shiga ciki za ku yi magana da Suwaiba”
Na gyada kai alamar gamsuwa sannan na saka hannuna na share hawayena sannan na juya na nufi gidanmu. Ko da na shiga na samu Suwaiba zaune falon mama tana ta rutsar kuka kamar ba ita ba, tana ganina ta soma bani hakuri tana fadin na yafe mata, a iya sanina Abdallah baya duka balle nace dukanta yai ya cilasta mata zuwa ta ba ni hakuri sai dai idan wani abun ya fada mata ko kuma cilastata yai.
7/21/21, 10:47 PM - Buhainat: I think you'd like this story: "GOBE NA (My Tomorrow)" by KhadeejaCandy on Wattpad https://www.wattpad.com/story/247701926?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=story_info&wp_page=story_details_button&wp_uname=KhadeejaCandy&wp_originator=ZkyWKvWuHXhIRzZDEluZ%2BuUXayIbDBikXAQA%2BM4xeAsJY%2Fh9rtovTCoQphCdFYUPM4K1nHTquOLcFfifZUhwZ0RRyERddTi4AY1OYORg8gUhN9fNU%2FLr6t3SMGO9O8M2
*GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
4️⃣5️⃣
ABDALLAH POV.
Zuciyarsa cike take da tunanin abunda Halima ta fada masa, ba sau daya ba ya sha jin sunan Abraham a gurin Abdulhamid, sai dai da kamar wuya ya iya fada mta kai tsaye idan har shi din ne? Mi zai saka ya tonawa kansa asiri? Mi mai zai saka yayi mata fyaden tun farko? Miyasa yai shigar yan fashi? Sai dai ya yarda Halima ba zata masa karya ba, tun da ita din bata san Abraham ba, kuma bata san cewa shi din ba musulmi ne ba, idan har ba shi ya fada mata ba.
Yana tsaye jikin motar Suwaiba ta fito daga cikin gidansu Halimatu ta nufo i da yake da hijabinta har kasa, be tsaya jiran ta karaso ba ya bude side dinsa ya zauna yai ma motar key tana shiga ya tashi motar.
Ta yi zaton hanyar gida zai nufa sai ta ga ya dauki hanyar family house dinsu.
“Doc baka hakura ba?”
Ta tambaya cikin kuka, ko kallon inda take be yi ba har ya shiga titin unguwarsu.
“Na ba ka hakuri kace ita zan bawa hakuri ita ma na bata, amman be isa ya saka ka yafe min dan abunda nai ba”
Sai a lokacin ya kalleta.
“Dan abunda kika yi? Da ne ma? Kin san irin kuncin da Halima take fuskata kike neman kara mata wani? Ko ba u so a tsakanina da ita ai ita din yar'uwata ce kuma kin sani, ko dan yan'uwantakan da ke tsakaninmu be isa ya saka ki raga mata ba ko da ma ace ita ce ta nemi fada da ke? Ko karuwata ce ai ya cancanci ki kyaleta saboda mutuncina, amman wai dan shashanci da aurena akanki ki shiga public place kamar nn kina magana any how, idan auren zan yi kin isa ki hana ni ne ko fadan ki sai ya saka na fasa?”
Tun da ya fara fadan take kuka har ya faka bakin kofar gidansu.
“Da gaske sakina din za ka yi?”
“Ko dai ban sake ki ba, dole na samawa su Inteesar wata uwar mai tarbiya da sanin ya kamata”
Da sauri ta hade hannayenta.
“Dan Allah kai hakuri, ka sake ni idan sakin zai saka ka huce haushi daga baya sai ka maida ni amman karka kara aure dan Allah, wallahi na bari ba zan sake ba”