← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 64 OF 136

Sashe 64

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Da zaka ji labarin matar nan da ka tausaya mata, kaddara ce ta fada mata kuma mahaifiyarta tai min rantsuwa....”

Saurin saukowa yai daga saman kujerar yana hade wani bakin abu daya tsaya masa a makoshi.

“Hajiya dan Allah? Bana son na ji duk wani abu da ya shafe ta, ba ina kokarin kai kararta ba ne saboda na danne mata hakki no hakki yata nake kokarin kwatowa?”

“Wace hujja kake da ita wacce ta nuna maka cewar matar nan ita ce ta kashe Baby? Haba Gwarzo ya kake neman zautuwa akan mutuwar da ba yau ta saba bakuntarka ba?”

Sakin baki yai da mamaki yana kallon Hajiya miyasa tai saurin canja har take kokarin hana shi bayan ita ma a da tana goyon bayan karar?
Siyama ce ta tashi zaune ta tana kallon Hajiya da mamaki.

“Hajiya be kamata a kyale wannan maganar ba, taya zata kashe Baby kuma a barta?”

Hajiya ta daka mata matsawa.

“Kar na sake jin bakinki ba ki san komai akan rayuwa ba, kuma idan manya suna magana karki sake tsoma bakinki”

“Amman gaskiya ta fada Hajiya indai suna da gaskiya kotu zata ba su gaskiyarsu mu kuma ta ba mu rashin gaskiyar”

Kallonsa Hajiya tai da kyau

“Mutuwar nan ta dauke mahaifinka ta dauke matarka, yanzu kuma ta dauke yarka, wata rana ni zata dauke kuma ta dauke kanwarka kamin ta dauke ka, wata rana zata zo da zaka rasa wanda zai hana ka aikata ba daidai ba balle ya fada maka kuskurenka....”

“Bana tunanin idan wannan ranar ta zo zan iya rayuwa Hajiya, na rasa babana na rayu na rasa matata yes na rayu yanzu kuma na rasa yata still zan rayu amman bana tunanin idan na rasa ki zan rayu, ku kadai kuka rage min a yanzu daga ke sai Siyama ku kadai nake da ku a yanzu, Allah ya min kyautar mata ya karbe, ya ba ni ya ya karbe, mahaifina ma ya karbi abunsa, ba ni da kowa a yanzu daga ke sai yar'uwata sai dangi”

Ya fada hawaye na sauko masa, sannan ya taso daga inda yake zaune ya nufa inda take ya rumgumeta.

“Na bar maganar nan har bada Hajiya, Wallahi na barta”

Hajiya ta lumshe idonuwanta dake cike da hawaye zuciyarta cike da tausayin danta.

“We're three mu kadai muka rage, babu Baby babu Daddy”

Cewar Siyama tana fashewa da kuka tare da rumgume Hajiya.

“Allah ya musu albarka”

Hajiya ta fada da muryar kuka, hakan yasa Gwarzo tashi ya bar falon yana share hawaye wasu na sauko masa.

HALIMATU POV.

Na ga abubuwa daya a cikin dogon bachi na, abubuwa mabanbanta, masu rikitarwa wadanda ba zan iya fassawaba, tabbas bachi da na dade ina yi a yau yana daure da mafarka kalakala. Ina ji a jikina kamar ban taba bachi mai nauyi irin wannan ba, domin ba jikina kadai ya mutu ba har fatar idona ji nake kamar ba zan iya budewa ba, numfashin ma idan ya fita daker ya ke dawowa, a duk lokacin daya dawo sai na ji wani bari da ban gama tantancewa daga ina yake fitowa ba, sai dai na sa tabbas ba na muhallina ba ne. A zuciyarta nake ta amboton mahallincina hakan ba karamin taimaka min yai har na samu karfin buden idon ba, sai kuma nai saurin maidawa na rufe sakamakon hasken da na ji yai min yawa idon har wani yaji na ji suna min. Cikin karfin hali na kai hannuna na murza idon sannan na sake budewa ina karewa dakin kallo sai a yanzu nake gane ko warin asibiti ne nake ji, amman miya kawo ni asibiti? Shi nake kokarin tunawa, a take kaina ya tsara na nemi duka tunani na rasa sai na sake rufe idon ina jin bakina da daci. Tuna abunda ya faru yasa ni saurin bude idon a nan abun neman ya samu hawaye suka fara aikinsu, unkurin tashi nai zaune amman na kasa saboda rashin kuzari. Hakan na cilasta min cigaba da karewa dakin kallo, ina haka aka turo kofar dakin wani ya leko ni sai kuma ya rufe dakin, da alama wani yake nema domin haka wasu suke idan suna neman wani sai su rika bibiyar daki suna lekawa. Har na lumshe idona sai kuma na sake jin an bude kofar a karo na biyu sai dai wannan karon na ji alamar shigowa duk kuwa da kasancewar idon nawa a rufe suke. Wani irin fitinannane kamshi turare na ji ya maye gurbin warin asibitin da nake ji hakan yasa ni saurin bude idon karaf nai arba da wani kyakkyawan farin mutum wanda ba zan iya kiransa da saurayin ba ba kuma zan ce masa mai aure ba tunda ban san gaibu ba, yana da manyan idanuwa ga dogon hanci, bakar rigar dake jikinsa ta haska fuskarsa gwanin daukar hankali. Matsowa yake ta yi kusa da ni yana kallon fuska kamar mai son tantance wani abu, van yarda a zahiri nake kallonsa ba har sai da na runtse ido na sake budewa, sai a yanzu na fahimci mutumen dazun ne da ya leko ni ya sake shigowa.

“Sannu.... ”

Ya furta min yana cigaba da kallona.

“Yauwa”

Na amsa daker, sai ya kalli kofa ya sake kallona.

“Ya jikin?”

“Al-hamdulillah kai likita ne?”

Jimm yai kamin ya bani amsa, hakan yasa ni tsaye na kare masa kallo da kyau, kusan a kuskure nai arba da sarkar cross din dake wuyansa wacce nake kyautata zaton ta zinari ce, kamar yadda hannunsa yake dauke da agogo da awarwaro na zinari haka ma zoben hannunsa, ba rigar jikinsa kadai ba har jean da ke jikinsa kana kallonsa kasan mai tsada ne.

“Yes ni Doctor ne how are you feeling now?”

Yana fadar hakan ya nufi gurin files dina ya bude yana dubawa sai dai babu alamar natsuwa a tare da shi in each seconds sai ya kalli kofa kamar mai tsoron shigowar wani. Ba zan iya karyata cewar shi din ba likita ba ne domin ban san a wace asibitin nakr ba, ba kuma zan iya gasgata cewar shi din likita ne ba domin ban ga alamun hakan a shigarsa da natsuwarsa ba, ko da yake likitoci ma sun fi saka kananan kaya.

“Ina mijinki?”

Ya tambaya yana kai hannunsa ya taba jikina.

“Miya faru?”

“Akwai maganar da nake son yi da shi”

Ya fada babu alamar wasa a tare da shi.

“Idan wani abun ne ka fada min likita ba ni da aure a yanzu zaman kaina ke”

Shiru yai yana kallon na dan wani lokaci kamin ya kai duka hannayensa ya rika ni ya tashe ni zaune, sai dai har lokacin ba shi da natsuwa.

“Haihuwarki nawa?”

“Hudu na samu miscarriage daya”

“When last kika samu miscarriage?”

“Ba a dade ba be wuce wata biyu zuwa uku ba”

“Mi kikai aka kawo ki asibiti mi yasa kike kuka?”

Hannu na kai na taba fuskata sai na ji sanyin hawayen dazun da ba su bushe ba.

“Wata yarinya ta fada rijiya kuma ta mutu shine abun ya firgita ni”

“Shiyasa kika samu kanki unconscious?”

Kallon rashin fahimta nai masa.

“Miyasa kake ta min wadannan tambayoyin?”

“Sun shafi lafiyarki ne, na duba files dinki na ga komai after that kina fama da cutar damuwa, kin sha maganinki yau?”

“Ban san an kawo ni asibitin ba sai yau”

Saurin tashi yai tsaye sai ya kai hannunsa a karo na uku ya taba fuska, sai kuma ya saka hannunsa aljihu ya ciro wayar da ban taba irinta ba ya miko min.

“Saka min Number ki a nan zan, akwai bayanin da zan miki akan ciwonki yanzu sauri nake yi”

Tsakanin wayar da fuskarsa sai idanuwa suka kasa tsayawa kallon abu daya, fuskarsa ko kuma wayar ko tambayar da ta cika min zuciya? Mi zai saka likita ya tambayi number wayata? Wane irin bayani ne da ba zai iya yi min ba?

“Wane irin likita ne kai? Wane bayani ne da ba zaka iya yi min ba? Ni ban gane ba? Waye kai? Ka bar ni na ji da abunda yake damuna dan Allah”

“I'm sorry”

Ya fada sannan ya nufi kofar fita kamin ya fice ya sake waigo ya kalleni.

“i'm sorry”

Sannan ya fice, ni kuma na lumshe idona ina maida numfashi a hankali, tsakanin fitar Mutumen da ban san wanene da sake turo kofar dakin a shigo be wuce minti biyar da yan dakiku ba. Da sauri na sake bude idon a zato na shine ya sake dawowa sai ni arba da Abdallah ido cikin ido wani irin faduwar gaba na ji wanda ban taba jin irinsa ba, sai na ji yayi min wani irin kwarjini kimarsa ta cika ido, hakan yasa ni kawarda kaina daga barin kallonsa har ya karaso kusa da ni, yawo ya rika min da hannunsa a fuskata kamin ya kai hannunsa ya taba ni.

“Halimatu....”

“Na'am”

Na amsa ba tare da na kalleshi ba, ina iya jiyo sautin fitar iskar bakinsa kamin ya kai hannunsa ya daga idona.

“Sannu yaushe kika tashi?”

“Ban dade sosai ba”

“Okay”

Da kanshi ya shiga ba ni kulawa kamin ya fita ya hado min tea ya dawo. Ya mika min tea na saka hannu na karba idonaa na kaina, yana ta kallona kamar be taba ganina ba, har na gama shan tea na aje kofin be dauke idonsa daga gareni ba. Dagowa nai na kalleshi a zatona zai kawarda idonsa ne amman kamar jiran yake mu hada sai ya cigaba da kallona ido cikin ido, hakan yasa sai duk na ji na tsargu.

“Yan gidan mu basa nan?”

Sai ya gyada min kai still idonshi na kaina.

“Kwananki tara a nan sai yau kika farka”

Kwana tara? Kenan ba bachi nayi ba kamar yadda nake tunani suma nai? Na tambayi kaina kamin na sake kallonsa na ce.

“Da gaske Baby Namra ta rasu?”

Nan ma kan ya gyada min yana cigaba da yi min kallon da ban san na minene ba, shigowar wani likitan ne yasa shi saurin mikewa tsaye ya saka hannayensa aljihu yana yi Doc maraba.

“Ya jikin nata?”

“Da sauki.... ”
Chapter 64 · 0% Book details