Sashe 133
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Iyakar kokarin da nai na danne dariya ta ne domin har ga Allah ya bani dariya matuka, daga ganin amai sai ya sa rai da ciki, ko da yake idan ance ina da cikin ba mamaki tunda mahaifa a bude take kamar yadda Aminu ya fada wai ina ta haihuwa zan tsufar da shi, yau kuma gashi Allah ya kawo ni inda ake kaunar yaya ake son haihuwa.
Ganin abun nasa ba mai karewa ba ne yasa na nufi gurin da nake aje tsintsiya na dauka na dawo gurin da zimmar gyara gurin sai ya kai hannu ya rike hannuna.
“That's my condition idan mace tana da ciki bata aikin komai sai cikin ya tsufa”
Kallon mamaki nai masa.
“Wani irin ciki dan Allah what if malaria ce?”
Dan murmushi yai murmushin dake nuna alamar be jidadin kalmar ba, ya karbe tsintsiyar ya aje ya matsa kusa da ni ya rike hannayensa yana min kyakkyawan murmushinsa cikin sanyi murya yace.
“Kin fatar ciki ne mana, da ko ya ko kuma duka biyun Allah ya hada ban ki ba, ina son haihuwa lims ina son yaya, yaya rahama ne sanyin idaniya ne i need my own family too, Hajiya ma tana son na haihu Siyama ni kaina ina son naga yayana na ciki, ko yayana nawa zaki haifa min ina so ni dai fatana su zama masu albarka kuma masu tausayinmu”
Sai kuma ya zaunar da ni ya kara jimke hannuna yana kallona cikin idona da idanuwansa da suka koma kalar tausayi.
“Ba zan iya fada miki yadda na ji a lokacin dana rasa Baby, idan har wannan aman da kikai ya tabbata ciki ne zan fi kowa farinciki Lims, and idan kika duba rayuwar nan bata da wani tsayo wata kila zamu dade wata kila ba zamu dade ba akalla ya kamata ace kamin mu bar duniya mu yi sadakatul jariya, sannan mu haifi yayan da zasu rika mana addu'a bakya fatar ki ga jinina za su yi kyau idan sun biyo ki look at your nose”
Ya fada yana jan hancina yana murmushi, nima hancin nasa naja.
“Ko kuma idan sun biyoka ba, Allah ya bamu masu albarka”
Kiss ya mannna min a goshi ya tashi yana fadin.
“Shiga ciki ki gyara jikinki zanje nai sallah na dawo sai na gyara gurin”
Ba musu na tashi na nufi hanyar dakin, bina yai da kallo sai da shiga sannan na ji ya bude kofar falon na fita. Da na shiga bandakin sai na tsaya haban madubi ina kallon kaina.
“Ba dai wani cikin ba ne? Ke dai Mahaifarki a bude take da anyi abu kadan sai ciki, da gangan dai kike yi so kike ki tara min yaya na rasa yadda zan yi nai saurin tsufa, ki hana ni jindadin rayuwa, yaushe kika haye Aiman da har za a ce kin dauki wani cikin? Mtchssss”
Abun dariya wai abunda Aminu yai min a lokacin dana samun cikin Amal ne ya rika dawo min, lallai na yarda bayan wuya sai dadi kuma komai yai farko dole ne yai karshe gashi a yau na aurin wanda jiran haihuwar ma yake ba kyama ba.
Tufafina gaba daya na cire tufafi na sake wanka nai alwala na fito daure tawul a kirjina sai na same shi gefen gadona a zauna yana ta kallon kofar bandakin kamar mai jiran fitowata.
Gaban madubi naje na tsaya sai ya mike tsaye ya tsaya a bayana yana kallona ta cikin madubi wani irin kallon ne da a zan iya fadar ma'anarsa ba.
“Da sannu ina ta maye gurbin abubuwan da na rasa”
Na yi murmushi sai ya rumgume ta baya yana sumbantar kafadata dayan hannunsa kuma a kaina yana shafa kananan tsorayen da ke kaina. Juyowa nai ina kallonsa, sai ya sa hannunsa ya lakaci kumatuna.
“Ya akai?”
Kasa ce masa komai nai sai kallonsa nake ina murmushi a raina ina ayyana irin kyau da Allah ya hore masa ga sura da cikar zati irin na da'namiji.
“Kin yi sallah?”
Ya tambaya yana had goshina da nashi, hakan yasa nai saurin sakinsa na nufi wardrobe na dauko wasu tufafin na saka ya shimfida min pray mat na saka Hijabi, har na yi sallah na gama banda kallona babu abunda Ahmad yake.
“Zan samo wacce zata rika dan share share da mopping girki kuma sai na karbo gurin Hajiya”
“Zan iya komai bama bukatar mai aiki, salon wata ta zo ta karbe min kai”
Na fada da iyakar gaskiyata. Ya dan wara ido ya dawo kusa da ni ya zauna.
“Kina tunani akwai wacce zata kwace place dinki? No one i mean no one”
“To idan kuma tai creating nata place din fa”
“Ai ba dadin zama za ta ji ba, kin riga kin karbe Hajiya Siyama ni da duk Family na”
“Ni dai ban yarda ba”
“Dole ma ki yarda wannan ka'idata ce indai macce nada ciki zan barta ta ji da dawainiyar cikin ne kawai sai na dauke mata na gida amman banda kaina”
Ya fada da murmushin.
“To yanzu shikenan sai ka cewa Hajiya ina da ciki Fisabilillahi sati daya da kawo ni?”
“A a ba fada mata zan yi ba, sai sai tace ba mu da hakuri mun yi ciki tun a waje, abun ai da kunya, amman kuma idan kika yi wata 8 kika haihuwa ganewa za yi fa?”
Magana yake da ni yana zaro ido kamar mai magana da wata karamar yarinya har da bude baki. Ni ban sansan lokacin da na fashe da dariyar ba na buge masa bakin sai ya rumgume ni yana kissing dina.
Kamar wasa, abu ya zama na gaske ko kofina Ahmad baya barin na dauke, idan ya bar ni na yi wani aikin sai idan baya nan, wata tsohuwa aka dauko tana mana aiki wanke wanke da shara sai mopping da karbo mana abincin gurin Hajiya, ban san abunda ya fadawa Hajiyarsa ba kullum sai ta kawo min abincin rana da dare wani lokacin kuma idan bana sha'awar abincin sai ya siyo min. Sai dai tun wacan aman da nai ban sake yin wani ba, kuma a kullum sai Ahmad ya tambaye ni me kike ji me kike so ina ke maki ciwo idan kin ji wani abu ki fada, haka yake kula da ni kamar wacce mai cikin fari, idan ya fita kuma ya ga wani abun kwadayi sai ya siyo min wai be sani ba ko ina so.
Be barni naje gida ba sai da nai wata uku da kuwa da irin kewar da nayi da ganin su Inna da Mama, suna Namra kam ko wane weekend sai ya dauko su sun zo mana hutu. Kowa fadi yake na canja wai fuskata ta kara cika fari na ya fito kamar ba ni ba, ni kaina na san na canja domin ina jin nauyin jikina a yanzu sabanin da. A gidan na wuni sai dare yaje da kansa ya dauko ni bayan ya shiga ya gaisa da su Mama yai musu alheri sannan muka kamo hanya.
“Zaki ci tsire?”
Yana tambaya na hade yawu dan na hango mai tsiren yana gasawa gefen hanya. Sai ya faka motarsa ya fita ya siyo min ya dawo.
“Sauran ice cream”
“A a ba ki san sanyi yana effecting abunda ke ciki ba? Na lura da ke kullun sai kin sha ruwan sanyi fa sai ma na cire makulin fridge din nan ai”
“Ai kadan nake sha”
Be ce min komai ba ya faka gefen titi ya sake fita ya siyo min ice cream sannan ya dawo motar a lokacin ni kam har na yi nisa da fara cin tsiren.
Ko da muka isa gida na cinye rabi sai dai ba ni kadai ba har da shi dake tukin miko min bakinsa yake na saka masa. A part dinsa yai bakin motar ya zagayo ya bude min kamar yadda ya saba na fito rike da kedar sai ya rufe motar sannan ya karba ledar hannuna.
“Jira ni a nan na fito Hajiya na da bako zaki je ki gaishe shi”
A gurin na tsaya har ya shiga ciki ya fito, sannan ya bude motarsa ya dauko tissue ya gyara min bakina kamar wata karamar yarinya ya jefar sannan ya rika hannuna muka nufi part din Hajiya. Sai muna daf da shiga sannan ya saki hannun nawa ya bude min kofar falon na shiga bakin kumshe da sallama Hajiya ce kadai a falon sai mai aikinta sam ban lura da su Kabir ba da wata mai zaman mahaifiyarsa wace suka tafi waje tare da ita da matarsa da wasu mutanen da suke tare da su ba sai da naje zan zauna. Aiko ba shiri na gwalo ido baki saki ina kallonshi shi ko sai dariya yake min.
“Kabir.....?”
“Na'am..... ”
Kara zaro ido nai jin muryarsa ce da gaske kuma gashi har ya amsa min ga shigarsa tsaftsaf cikin kamala, aiko na nufi cikin wani irin mamaki da bazata sai jin nai an rike ni an dawo da ni baya.
“Ke”
Sai na juyo na kalli Ahmad baki saki farinciki har cikin raina.
“Ba ka fada min ya dawo ba”
“Ba gashi kin gani ba”
Ya fada yana kokarin zama har lokacin be saki hannuna ba, aiko dan murya ban san lokacin dana rumgume Ahmad din ba sam na ma manta da zancen wata Hajiya tana gurin, har ga Allah ya jidadin samun lafiyar Kabir hakan ya wanke raina fes. Godiya suka rika yi ma Ahmad da Hajiya kamin su shiga yi mana addu'a kala kala suna saka mana albarka.
“Ka yi sa'ar mata Halima tana da kirki tana da mutunci kuma ta san kanta”
Kabir ya fadawa Ahmad yana kallona, a nan Ahmad ya wani dauke kai yana murmushin yake kamin ya kalleni murya kasa kasa yace.
“Tashi kije part din mu ki jira ni”
“Wayyo ina son na ga lafiyarsu”
Ganin abun nasa ba mai karewa ba ne yasa na nufi gurin da nake aje tsintsiya na dauka na dawo gurin da zimmar gyara gurin sai ya kai hannu ya rike hannuna.
“That's my condition idan mace tana da ciki bata aikin komai sai cikin ya tsufa”
Kallon mamaki nai masa.
“Wani irin ciki dan Allah what if malaria ce?”
Dan murmushi yai murmushin dake nuna alamar be jidadin kalmar ba, ya karbe tsintsiyar ya aje ya matsa kusa da ni ya rike hannayensa yana min kyakkyawan murmushinsa cikin sanyi murya yace.
“Kin fatar ciki ne mana, da ko ya ko kuma duka biyun Allah ya hada ban ki ba, ina son haihuwa lims ina son yaya, yaya rahama ne sanyin idaniya ne i need my own family too, Hajiya ma tana son na haihu Siyama ni kaina ina son naga yayana na ciki, ko yayana nawa zaki haifa min ina so ni dai fatana su zama masu albarka kuma masu tausayinmu”
Sai kuma ya zaunar da ni ya kara jimke hannuna yana kallona cikin idona da idanuwansa da suka koma kalar tausayi.
“Ba zan iya fada miki yadda na ji a lokacin dana rasa Baby, idan har wannan aman da kikai ya tabbata ciki ne zan fi kowa farinciki Lims, and idan kika duba rayuwar nan bata da wani tsayo wata kila zamu dade wata kila ba zamu dade ba akalla ya kamata ace kamin mu bar duniya mu yi sadakatul jariya, sannan mu haifi yayan da zasu rika mana addu'a bakya fatar ki ga jinina za su yi kyau idan sun biyo ki look at your nose”
Ya fada yana jan hancina yana murmushi, nima hancin nasa naja.
“Ko kuma idan sun biyoka ba, Allah ya bamu masu albarka”
Kiss ya mannna min a goshi ya tashi yana fadin.
“Shiga ciki ki gyara jikinki zanje nai sallah na dawo sai na gyara gurin”
Ba musu na tashi na nufi hanyar dakin, bina yai da kallo sai da shiga sannan na ji ya bude kofar falon na fita. Da na shiga bandakin sai na tsaya haban madubi ina kallon kaina.
“Ba dai wani cikin ba ne? Ke dai Mahaifarki a bude take da anyi abu kadan sai ciki, da gangan dai kike yi so kike ki tara min yaya na rasa yadda zan yi nai saurin tsufa, ki hana ni jindadin rayuwa, yaushe kika haye Aiman da har za a ce kin dauki wani cikin? Mtchssss”
Abun dariya wai abunda Aminu yai min a lokacin dana samun cikin Amal ne ya rika dawo min, lallai na yarda bayan wuya sai dadi kuma komai yai farko dole ne yai karshe gashi a yau na aurin wanda jiran haihuwar ma yake ba kyama ba.
Tufafina gaba daya na cire tufafi na sake wanka nai alwala na fito daure tawul a kirjina sai na same shi gefen gadona a zauna yana ta kallon kofar bandakin kamar mai jiran fitowata.
Gaban madubi naje na tsaya sai ya mike tsaye ya tsaya a bayana yana kallona ta cikin madubi wani irin kallon ne da a zan iya fadar ma'anarsa ba.
“Da sannu ina ta maye gurbin abubuwan da na rasa”
Na yi murmushi sai ya rumgume ta baya yana sumbantar kafadata dayan hannunsa kuma a kaina yana shafa kananan tsorayen da ke kaina. Juyowa nai ina kallonsa, sai ya sa hannunsa ya lakaci kumatuna.
“Ya akai?”
Kasa ce masa komai nai sai kallonsa nake ina murmushi a raina ina ayyana irin kyau da Allah ya hore masa ga sura da cikar zati irin na da'namiji.
“Kin yi sallah?”
Ya tambaya yana had goshina da nashi, hakan yasa nai saurin sakinsa na nufi wardrobe na dauko wasu tufafin na saka ya shimfida min pray mat na saka Hijabi, har na yi sallah na gama banda kallona babu abunda Ahmad yake.
“Zan samo wacce zata rika dan share share da mopping girki kuma sai na karbo gurin Hajiya”
“Zan iya komai bama bukatar mai aiki, salon wata ta zo ta karbe min kai”
Na fada da iyakar gaskiyata. Ya dan wara ido ya dawo kusa da ni ya zauna.
“Kina tunani akwai wacce zata kwace place dinki? No one i mean no one”
“To idan kuma tai creating nata place din fa”
“Ai ba dadin zama za ta ji ba, kin riga kin karbe Hajiya Siyama ni da duk Family na”
“Ni dai ban yarda ba”
“Dole ma ki yarda wannan ka'idata ce indai macce nada ciki zan barta ta ji da dawainiyar cikin ne kawai sai na dauke mata na gida amman banda kaina”
Ya fada da murmushin.
“To yanzu shikenan sai ka cewa Hajiya ina da ciki Fisabilillahi sati daya da kawo ni?”
“A a ba fada mata zan yi ba, sai sai tace ba mu da hakuri mun yi ciki tun a waje, abun ai da kunya, amman kuma idan kika yi wata 8 kika haihuwa ganewa za yi fa?”
Magana yake da ni yana zaro ido kamar mai magana da wata karamar yarinya har da bude baki. Ni ban sansan lokacin da na fashe da dariyar ba na buge masa bakin sai ya rumgume ni yana kissing dina.
Kamar wasa, abu ya zama na gaske ko kofina Ahmad baya barin na dauke, idan ya bar ni na yi wani aikin sai idan baya nan, wata tsohuwa aka dauko tana mana aiki wanke wanke da shara sai mopping da karbo mana abincin gurin Hajiya, ban san abunda ya fadawa Hajiyarsa ba kullum sai ta kawo min abincin rana da dare wani lokacin kuma idan bana sha'awar abincin sai ya siyo min. Sai dai tun wacan aman da nai ban sake yin wani ba, kuma a kullum sai Ahmad ya tambaye ni me kike ji me kike so ina ke maki ciwo idan kin ji wani abu ki fada, haka yake kula da ni kamar wacce mai cikin fari, idan ya fita kuma ya ga wani abun kwadayi sai ya siyo min wai be sani ba ko ina so.
Be barni naje gida ba sai da nai wata uku da kuwa da irin kewar da nayi da ganin su Inna da Mama, suna Namra kam ko wane weekend sai ya dauko su sun zo mana hutu. Kowa fadi yake na canja wai fuskata ta kara cika fari na ya fito kamar ba ni ba, ni kaina na san na canja domin ina jin nauyin jikina a yanzu sabanin da. A gidan na wuni sai dare yaje da kansa ya dauko ni bayan ya shiga ya gaisa da su Mama yai musu alheri sannan muka kamo hanya.
“Zaki ci tsire?”
Yana tambaya na hade yawu dan na hango mai tsiren yana gasawa gefen hanya. Sai ya faka motarsa ya fita ya siyo min ya dawo.
“Sauran ice cream”
“A a ba ki san sanyi yana effecting abunda ke ciki ba? Na lura da ke kullun sai kin sha ruwan sanyi fa sai ma na cire makulin fridge din nan ai”
“Ai kadan nake sha”
Be ce min komai ba ya faka gefen titi ya sake fita ya siyo min ice cream sannan ya dawo motar a lokacin ni kam har na yi nisa da fara cin tsiren.
Ko da muka isa gida na cinye rabi sai dai ba ni kadai ba har da shi dake tukin miko min bakinsa yake na saka masa. A part dinsa yai bakin motar ya zagayo ya bude min kamar yadda ya saba na fito rike da kedar sai ya rufe motar sannan ya karba ledar hannuna.
“Jira ni a nan na fito Hajiya na da bako zaki je ki gaishe shi”
A gurin na tsaya har ya shiga ciki ya fito, sannan ya bude motarsa ya dauko tissue ya gyara min bakina kamar wata karamar yarinya ya jefar sannan ya rika hannuna muka nufi part din Hajiya. Sai muna daf da shiga sannan ya saki hannun nawa ya bude min kofar falon na shiga bakin kumshe da sallama Hajiya ce kadai a falon sai mai aikinta sam ban lura da su Kabir ba da wata mai zaman mahaifiyarsa wace suka tafi waje tare da ita da matarsa da wasu mutanen da suke tare da su ba sai da naje zan zauna. Aiko ba shiri na gwalo ido baki saki ina kallonshi shi ko sai dariya yake min.
“Kabir.....?”
“Na'am..... ”
Kara zaro ido nai jin muryarsa ce da gaske kuma gashi har ya amsa min ga shigarsa tsaftsaf cikin kamala, aiko na nufi cikin wani irin mamaki da bazata sai jin nai an rike ni an dawo da ni baya.
“Ke”
Sai na juyo na kalli Ahmad baki saki farinciki har cikin raina.
“Ba ka fada min ya dawo ba”
“Ba gashi kin gani ba”
Ya fada yana kokarin zama har lokacin be saki hannuna ba, aiko dan murya ban san lokacin dana rumgume Ahmad din ba sam na ma manta da zancen wata Hajiya tana gurin, har ga Allah ya jidadin samun lafiyar Kabir hakan ya wanke raina fes. Godiya suka rika yi ma Ahmad da Hajiya kamin su shiga yi mana addu'a kala kala suna saka mana albarka.
“Ka yi sa'ar mata Halima tana da kirki tana da mutunci kuma ta san kanta”
Kabir ya fadawa Ahmad yana kallona, a nan Ahmad ya wani dauke kai yana murmushin yake kamin ya kalleni murya kasa kasa yace.
“Tashi kije part din mu ki jira ni”
“Wayyo ina son na ga lafiyarsu”