← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 136

Sashe 11

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Wane Halimatu zata zaba? Aurenta da Aminu wanda shine rufin asirinta da na yarta kamar yadda Mahaifiyarta ta fada?
Ko kuwa kwato hakkin yarta wacce aka lalatawa rayuwa aka maida babban mace?

#Abdallah
#Abdulhamid
#Aminu
#Halimatu
#ZawarcinHalimatu
#Gobena
#Freepage
#Twinbrother

*If you want to subscribe pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*
7/20/21, 8:29 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_

By Khadeeja Candy

7️⃣

Hawayena na share na tashi na shiga dakina nai alwala na soma gabatar da sallah azahar, ina Sallah shiedan na ta kawo min wasu abubuwan da be kamata nai tunaninsu a lokacin da nake a gaban Ubangijina ba, sai dai na yi nasarar fadawa Allah bukatata kuma na kai masa kuka. A lokacin da na sallame sai addu'a ta subuce bakina saboda tunanin da ya taru yai min yawa. Ida har na hakura na bar rayuwar Namra ta tafi a haka ni tawa rayuwar zata inganta kuwa? Taya zata inganta bayan yata zata kasance cikin kunci? Kyale Baba Sadi zai canja mishi hali ne daga abun yake? No sai dai ya kara masa kwarin guiwar yin hakan saboda an kyaleshi, hakan kuma ba zai saka Aminu sauya halinsa ba, miye ma amfanin zama da mutumen da ke mu'alama da wasu matan a waje, wanda har ya zama silar lalacewar ta wa yar? Shin yin shiru zai amfanin wani abu ne? Jin bugun kofar falo ne ya dawo a ni daga duniyar tunanin da na tafi. Tashi nai sanye da hijab da nai sallah na nufi kofar falon, ina budewa na ga Abdallah tsaye rike da hannun Adnan dayan hannunsa kuma rike da leda fara irin babbar nan ta pharmacy, Aiman kuma na gefensa, sam na manta da zancen dauko su daga makaranta sai yanzu.

“Be kamata ace har yanzu kina barin kanen mijinki yana zuwa dauko yaranki daga makaranta ba, domin idan be samu mace ba mazan zai iya lalata su tun da duniyar ta canja ba maza ba mata”

Shine abunda ya fada min kai tsaye, ni kuma na kwara bude kofar falon.

“Adnan ku shigo ciki”

Da sauri suka shiga falon ni kuma na fito na tsaya bakin kofar falon na janyo kofar na rufe.

“Kin yi kuka da yawa Halima ga fuskarki nan ya nuna, kina tunanin kuka zan canja komai ne? Kina tunanin kukam zai saka Kanen mijinki nadamar abunda yai? Ko kuma mijinki zai fasa neman matan da yake ne yana gallaza miki? Haka zaki saka ranki a kunci kina ta damuwa?”

Kasa nai da kaina ina jin wasu hawayen suna kokarin cika min ido.

“Na je gida na kai miki yaran na yi tsammani kina gida, sai suka ce kin zo kin tafi, tun da na ji haka na san cewar sun karya miki kuiwa ko? Su baki shawarar rufe sirrin saboda kar wani yaji, Kanen mijinki ya ci bulus kenan? Bayan ya ci amanar dan'uwansa, rayuwar aure ba rayuwar kunci ce ba Halima, saboda kina neman lahirarki ko kuma kina son kyautata rayuwarki be kamata kullum ki yi zama da kunci kina tauye kanki ba, musulunci ma be yarda da irin wannan auren ba, yaushe rabon da ko kusantarki mijinki yai?”

Hawaye ya fara sauko min, tabbas Abdallah yana da gaskiya akan dauki wata daya biyu wani lokacin har uku kamin Aminu ya zo min da bukatarsa.

“Ba sai kin fada min ba na sani, namiji mai neman matar sosai kamar yadda Aminu yake baya iya kula matar gida, duk abunda zaki yi ba zaki burgeshi ba saboda idonsa sun bude akan wasu matan na waje kuma ya yarda sun fi ki komai, so baki da wata daraja da kima a idonsa, yana yawan fadar baya son mace mai irin siffarki halittarki bata burge shi, kuma kin tara masa yayana yana da kananan shekarunsa a lokacin da yake bukatar hutu ke kuma kika son hana shi jindadin rayuwa, shiyasa yake gallaza miki”

Dagowa nai na kalleshia fusace na ce

“Kana ta fadin karya da gaskiya akan mijinki, tsayawa a ina saurarenka ba shi yake nufin na yarda da kai ba, baka san komai akan mijina ba babu ruwanka da rayuwarsa”

“Kwarai na san komai akansa, da yawa daga abokansa ina hulda da su kuma kin sani mazinata basa da sirri, har jinjirin cikin da kike dauke da shi na sani Halima, babu wanda be san irin zaman da Aminu yake da ke ba a cikin abokansa, saboda mijinki ba shi da sirri, ban san taya akai ma kika auri Aminu ba Halima sam ba mijin daya dace ki aura ba ne”

“Baka isa ka shigo har cikin gidana ka ce zaka fada min wata maganar banza akan mijina ba, ka fice”

Cikin wani irin tsawa na nuna masa gate raina na bace, daman ya saba a duk lokacin da muka hadu da shi sai ya fada min wata maganar marar dadi akan Aminu. Murmushi yai ya tabe baki ya miko min ledar hannunsa.

“Maganin Namra ne, karki sake mata abunda zai tsoratata saboda kwakwalwarta a tsorace take a yanzu ya riga ya gama tsoratata so tsoron yana tare da ita har sai ta samu sakewa na wani lokacin kamin ta koma Normal, ki rika gasa mata da ruwan zafi. And idan kin ga dama ki dauketa ki kai ta riko gidan Kenan mijinki sai na yarda kin fi ganin kimar mijinki fiye da yarki, duk abunda kike idan saboda goben ki kike to goben ta fara lalacewa a yanzu tun da har zaki iya barin hakkin yarki akan aurenki......!”

Yana fada min haka ya juya a fusace ya sauka daga dan gudun stairs din dake gurin ya nufi motarsa ya shiga yai ribas da karfi alamun da ke nuna ransa ya bace sosai kenan. Bude kofar falon nai na shigo ya maida kofar na rufe na jingina jikin kofar ina fashewa da kuka mai karfi. Na rasa abunda zan yi maganar mahaifiyata zan bi ko kuwa abunda nake ganin yafi?

“Momy mi kike kuka?”

Adnan ya tambaya daga shi har Aiman kallona suke.

“Ba kuka na ke ba”

“Gashi nan hawaye yana miki zuba”

“Kaina ke ciwo”

Na fada ina kirkiro murmushi tare da share hawayen. Hannu na mika musu sai duka suka zo na zaunar da su kusa da ni na shafa kansu sannan na daga kaina na kalli Namra da ke bachi saman cushion. Yayana na daya daga cikin babban kyautar da Allah kan yi ma bawa, wasu nema suke yi saboda Allah be basu ba, da ana siya da kudi da sun siya ko nawa ne, wasu kuma Allah ya basu mazan be basu matan ba, suna ta son mata ba su samu ba, wasu kuma matan Allah ya basu be basu maza ba, amman ni Allah ya hada min duka biyu ya bani maza biyu mata biyu a cikin shekara 11, sai dai ya bani su a inda ni kadai nake masa godiya da kyautar da ya ba ni, ni kadai na ke kallonsu na jidadi, mahaifinsu kan ganin yake na tara masa tsufa, har yana guduna saboda su saboda haihuwarsu ta canja min halitta na tashi daga buduwar zuwa mace mai yaya hudu da ciki na biyar, cikin da yake cewar na zubar baya bukatarsa.

“Allah ya raya ku ya sakawa rayuwarka albarka ya tsare min ku”

Na fada ina kara shafa kansu, sannan na mike tsaye na nufi kitchen na kunna gas na hada musu tea na gama musu da sauran biredin safe da yai saura na mika musu, ni kuma na shiga dora girkin rana duk kuwa da ina jin cewar ba zan iya ci ba amman dole na dora saboda yarana. Komai saboda su ne, zaman da nake da Aminu saboda su ne, idan na fita na barsu ban san wace irin rayuwa za su shiga ba, ban san wace macen ce zata raine su ba, fatar shiriyar da nake masa ko bana aurensa ina masa ita saboda na riga na haihu da shi. Ina cikin wanki shimkafa na ji yara suna murna.

“Oyoyo Anty Hafiza”

Kanwata ce wacce muke uba daya da ita, sai dai Allah ya hada jininmu kamar yan daki daya, bata boye min komai ni ma bana boye mata damuwata.

“Yar aljanna... Da aka fada miki kuma sai kika ji kika dawo gida har kina girki, Allah mai ikon, da ya tashi sai yai mu uba daya amman hali kowa da na shi”

Juyowa nai na kalleta da idona da suke kumbure, sai na ga hawaye na mata zuba mayafinta ma a hannu yake tare da jakarta.

“Da ace ko wace mace zatai irin zaman auren da kike da mijinki, da maza sun huta da korafin matansu, kuma da ko wane yaro mai uwa da uba a raye be girma ya ga uwayensa a rabe ba, kina da hakuri Halima fiye da kima, sai dai hakurin idan yai yawa yana cutarwa, abun ya wuce kanki a yanzu rayuwar yaranki ake neman lalatawa, be kamata ki yi hakuri a nan gurin ba”

Sai da na hade yawun bakina sannan na ce.

“Inna ta fada miki abunda ya faru?”

Sai ta matso kusa da ni tana kallon irin kallon nan na tsantsar tausayi.
Chapter 11 · 0% Book details