← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 127 OF 136

Sashe 127

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ta nuna min wata bakar mota wacce Ahmad da Hajiya suka shiga, a tare muka nufi motar sai ga Amal ta fito daga wacan motar da gudu tana fadin wacce na shiga zata shiga. Ina kokarin yi mata fada Ahmad ya bude front seat ya ce ta zo, a tare da shi ta zauna gidan gaba, ni da Hajiya da Siyama kuma muka zauna a baya, ina ta jin kunya sai dai na lura Hajiya bata kula wannan ba sai ma kokarin fira take da ni idan an kai wani gurin tace min ga kaza nan.
Sai da muka isa sakkwato muka huta a wata hotel sannan muka wuce airport, ko da muka isa ya rage sauran minti talatin jirgin ya tashi zuwa Abuja, a nan mukai duk abunda ya kamata sannan mukai sallama da su, Siyama har da hawaye ta rumgume dan'uwanta tana masa addu'ar samun lafiya sannan ta rungume Hajiya nima ta rumgume ni.

“Matar yaya ki kula min da yayana kin ji”

“In-Sha-Allah”

Daga haka mu kai sallama da su tare da yarana sannan muka shiga cikin jirgin ina ta jin kewar gida, kujerar da ke kusa da window ce tawa sannan ta Ahmad sai kuma ta Hajiya a baya kuma ta wani ce da nai zaton direba ne domin shi ya tuko mu duk kuwa da shigarsa bata nuna hakan ba. A lokacin da jirgin zai tashi duk muka saka belt sai jin dagawarsa nai hakan kuma ba karamin tsoro ya saka min ba abunka da wanda be taba shiga ba. Ina ta addu'a domin gani nake na yi kusa da mutuwa tun da jirgin ya daga sama.
Ba zan iya sanin awanin da muka dauka ba kamin mu isa Abuja wata kila ma yan mintuna ne tun da ance jirgi sauri ne da shi, sai dai naji Hajiya na fadin mun yi sauri.
Sallah akwai na san mun yi a wani gida da nake kyautata zaton na yan'uwansu Ahmad ne, ko awa daya ba mu yi ba a gidan muka koma airport din abinci ma sai a can muka ci, gaskiya garin Abuja na da kyau mayan gidaje ta ko'ina ga tituna gwanin burgewa ga yanayin garin da sanyi ba kamar Sokoto ko Zamfara ba.
Manyan shuke shukensu ma abun kallo ne, airport din ma gwanin burge wa kowa ka gani tsab da shi sai hada hada ake ba ruwan kowa da kowa.
Wani jirgin muka shiga ya daga da mu zuwa kasar nasara....

Na sha bachi kam sosai a cikin jirgin a duk lokacin da zan farka sai na gan ni a kafadar Ahmad, can kuma ya tashe ni ya bani tea a wani karamin kofi da biscuit shi ma ba wani mai yawa ba, bayan na gama sha wata mace mai sanye da uniform ta zo ta karba. Mun dade sosai muna tafiya kamin mu isa, a iya sanina mun baro Nigerian da yamma lis amman da muka sauka nan sai na ga safiya ce fal, ga wani uban sanyi mai ratsa kashi. Cikin airport din Ahmad ya fiddo rigar sanyi ya saka min a saman abayar da ke jikina ya bani safa na saka na a hannuna a kafa ma ya bani na saka sannan na cire talkamina ya bani wasu talkamin masu rufe na saka shi ma ya saka kamar yadda Hajiya ma ta saka sannan muka nufi gurin tex. Kusan tun da muka bar airport din sai na ce ban hadu da bakin mutum ba har muka isa hotel din da aka kama mana bana aikin komai sai kalle kalle, ashe a Abuja ance min baki ga komai ba yanzu ne kallo yake.
Komai na su a cikin tsari yake gwanin ban sha'awa ga bin doka da oda, tun da muka sauka cikin jirgin Ahmad ke rike da hannuna har muka isa dakinmu da aka bare mana.
Ina zaunawa bachi yace sallamu alaiku, sai jin nai yana tashina.

“Lims ta so mu yi wanka sai ki yi bachin mu kuma za mu karasa asibitin”

“No nima zan bi ku”

“A a Hajiya tace na barki ki huta”

“Da gaske”

“Ai ba zan miki karya ba”

“Yaushe tace ban ji ba kuma ai tare muka shigo nan”

“A waya ta kira ni”

Ya nuna min wayarsa. Yana kokarin rika hannuna.

“Taso muje mu yi wanka mu yi sallah jirana take”

“To ka shiga ka fara yi sai....”

“A a nan ai babu wanda zai sa mana ido ki saki jikinki”

“Aa wallahi ba zan iya ba a yanzu”

Na fada ina girgiza masa kai, sai ya dafa kaina.

“Why da rantsuwa? Wata rana ke zaki bukaci haka ma”

A gabana na cire tufafin jikinsa sai da na kawarda fuskata ya daura tawul ya wuce bandakin ba tare da jin komai ba, ni kam gaba duk naji wani iri ji nake kamar wacce bata mu'amala da wani ba haka na ji, gaba daya komai sai na koma kin sabo musamman Ahmad da na lura lamarinsa azimun ne.

_________________

Na so na karasa pages din kamin sallah amman Allah be nufa ba, dan haka zamu tafi hutu sai bayan Sallah idan mai kowa mai komai ya amince mana In-Sha-Allah.
7/25/21, 4:10 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy

6️⃣2️⃣

Sai da ya fito daga wankan sannan na shaga, da sabulu kawai nai wankan domin babu soso a ciki sabulun ma ba irin na mu na Nigeria ba ne, bayan na gama na daura karamij tawul din har na nufo kofa na fito sai kuma wata zuciyar tace min kara dai na maida tufafim jikina kar na fita da wannan guntun tawul ai da kunya.
  Ina kokarin daukar kayan na saka sai jin nai an yaye labulen bandakin daman ba kofa ba ce bandakin na glass ne sai lalulen da aka saka dan kare wanda yake wankan.

“Ba ki gama ba ne”

Ya fada yana kallona tun daga saman kaina har kasan kafafuwana. Tsaye nai da kayan ka kasa sakawa na kasa ajewa na kasa fitowa wata irin kunya mai tsanani ta rufe ni. Sai da ya hade yawu sannan yai murmushi ya juya yana fadin.

“Fito ki saka tufafin ki, ni ba wani abu zan miki ba”

Kallon jikina nai tawul din karami ne sosai ta yadda idan na duka za a iya ganina idan kuma ban rike shi da kyau ba zai iya subuce min ya fadi. A haka na daure na fito ganin babu wata mafita na nufi gurin akwaitina da zimmar na fito da doguwar riga na saka, sai jin mutum nai a bayana ya dora hannayensa saman kafadata yana sharce min ruwan da ke kai bakinsa saitin kunnena ya rada min.

“Ki daina jin kunyata, ni mijinki ne kuma zaki wahalar da kanki ne kawai, ni kaina ina da kunyar amman akan halila gaskiya babu wannan ina sakewa nai yadda nake so, ni da ke abu daya ne a yanzu”

Ya karasa tare da tsosa kunnena, wani yarrrr na ji rabon da na ji irin haka har na manta, kamar wacce aka daurewa baki haka na zama da kansa yaja hannuna zuwa gaban akwatinsa ya bude ya dauko wani mai mai kamshi ya zuba a hannunsa ya fara shafa min kamar nai magana sai kuma a kasa, haka ya ji ko'ina na jikina ya shafa min man har a cikin yatsun kafata, sannan ya fara kokarin kwantar da ni saman gadon a nan kam Allah ya bani ikon magana

“Ban yi sallah ba”

Bakin da nai magana da shi ya kurawa ido gaba daya idanuwansa sun canja kana kallonsa kasan natsuwarsa ta dade da barin jikinsa, can kuma ya kalli cikin idona sai kuma ya sake kallon bakina tare da kai hannunsa ya taba lisp din a hankali sannan ya sake ni ya juya ya nufi bandaki, ni kuma na mike tsaye daidai ina gyara tawul din dake kokarim subucewa gaba daya, kamar an koroshi haka ya dawo da gudu ya rika ni ya fara kissing din bakina yana wani irin haki yana shafani kamar wanda aka ce za a raba da ransa idan be sumbance ni ba.
Ban san iya lokacin da mu ka dauka a haka ba, tun muna tsaye har tsayin ya gagara muka kwanta saman gadon, wanda hakan ya bashi damar kai hannunsa a kirjina yai wasa da shi yadda ransa yake so. Sai da aka soma kwankwasa kofar sannan ya daga ni da sauri ya nufi kofar sai dai be bude ba sai ya tsaya daga jikin kofar.

“Waye?”

Ya fada yana cizon lisp dinsa tare da aje numfashi a hankali.

“Kai fa nake jira tun dazun”

“Hajiya gani nan zuwa yanzu please I'm sorry”

Ya fada yana maida numfashi sai da ya tabbatar ta tafi sannan sake nufo ni yana murmushi.

“Na manta Hajiya na jirana idan na fita zance ke kika tsayar da ni a nan”

Bance masa komai ba nai kasa da idona, wannan karon kafafuwansa biyu ya raba ya kai bakinsa gurin hancina sai da ya tsotse shi tasss sannan ya dagani ya fara kokarin cire tufafin jikinsa. Juyaawa nai na bashi baya tare da yan Bedsheet din na rufe jikina, ina jin sautin dariyarsa da kuma maganganun da yake fada na rashin kunya har ya shige bandanki, nima dan murmushin nai ina lumshe ido, ni kaina a yau wani shauki ya ziyarce ni wanda na manta rabon da na ji irinsa, wata irin natsuwa da annashuwa suka sauko min, na kasa daina murmushi har ya gama wankan ya fito, ya sake shiryawa cikin wasu riga da wandon ya fesa turare sannan ya kwanto bayana yai kissing din gefen wuyana yasa hannunsa ya kama hannuna yatsunsa cikin nawa.

“Ki yi bachi ki more”

Juyowa nai da sauri da zimmar nai masa magana sai bakina ya gogi nasa numfashina ya gauraya da nasa, babu abunda yake kallo sai bakin nawa.

“Talk”

Ya fada bakinsa na gugar nawa, a dole nima a haka nai masa magana bakina da nasa na gogar juna.

“Ina son naje nima ai”
Chapter 127 · 0% Book details