Sashe 122
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwantar da kaina nai kafadarsa ta hagu ina jin wani sabon kukan na son fito min. A hankali na fara jin yana motsi da na kalleshi sai na ga ya rufe ido yana cizon baki, a take hankali yai mugun tashi cikin sauri na mike tsaye ina tunanin abunda zan yi, dayan hannunsa yasa ya rike hannunsa na dama yana wani irin nishi yana ambaton Allah.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Shine abunda na furta ina fashewa da kuka, a yanayin yadda nake ganin fuskarsa da kuma yadda ya rike hannun ya isa ya sanar min da irin azabar da yake ji, wacce nake jin kamar ace akwai abunda zan iya a dauke masa ciwo gaba daya, da sauri na fito daga dakin da zimmar zuwa dakin da Doc Nura yake domin na san asibiti tun da ba yau na fara shigowa ba, a kujerar dake kusa da dakin na yi arba da Siyama zaune tana latsa wayarta tana ganina ta mike tsaye.
“Ciwon ya tashi kenan?”
Ban ko kula ta ba na nufi hanyar da zata sadani da dakin likita ina kuka, kamin na karasa mutumen da ke gadin kofar office din ya tare ni.
“Likita nake nema ciwon Ahmad ya tashi”
“Baya office dinsa tun dazun ya fita”
Juyawa nai da gudu na koma dakin sai na samu likitan da wasu likitoci biyu suna tsaye a kansa, Siyama kuma tana gefe tsaye tana kuka, belt din suka kwance suka sake saka masa wani sannan sukai masa allura.
“Dan Allah ku je waje..... ”
Ni da ita muka fito daga dakin muka tsaya a waje, ita kuka ni hawaye.
“Ki yi hakuri zai samu lafiya in Allah ya yarda”
Na fada ina dafata domin a yadda ita take kuka dole ne ni tasa ni na hade nawa kukan na zama jaruma na lallashe ta.
“Ina fatar hakan, baya son muna zuwa kusa da shi saboda kar mu ga halin da yake ciki, tsoro na ke ji ina jin kamar.... kamar.... Yaya mutuwa zai yi.....”
Na yi saurin rufe mata baki.
“Haba dai cuta ai ba mutuwa ba ce, zai samu sauki In-Sha-Allah”
A lokacin ne wani kukan ya zo min, tana da gaskiya ni da ita za mu iya rasa shi, saboda haka suka rasa yarsa, idan har ya kasance ni ce sila fa? What if ya kamu da wannan ciwon ne saboda ya aure ni? Ban raba dayan biyu ba Doc Nura ya fito daga dakin, ya nufo inda nake tsaye ni da Siyama yai mana maganar da zata kwantar mana da hankali cewar Ahmad zai samu sauki. Sai da ya wuce zuwa wani gurin sannan Siyama ta bude dakin ta shiga, ni kuma na bi bayan likita na cika kafa kamin ya shige na cin masa.
“Doc dan Allah ina son magana da kai”
Juyowa yai ya kalleni.
“Ina jin”
“Dan Allah miye abunda yake damun Ahmad?”
Shiru yai kamar mai nazari.
“Hajiya bata fada miki ba?”
“Ta fada min tace ba a san ko minene ba amman ina son kara ji daga bakinka”
Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya ce.
“Gaskiya ne, an yi duk wani hoto daya kamata amman ba a ga komai ba, kuma shi yace yana jin ciwo yana masa yawo a hannun”
“Amman tun yaushe abun ya fara?”
“Yace min ranar assabar da dare, ya fito daga gurin abokinsa da dare, wai be iya kai kansa gida ba sai da ya kira direbansu ya kawo shi, na tambaye shi ko ya ci wani abu ne ko kuma hannun ya bugu da wani abu? Yace min a a yanzu jibi za a fita da shi, asibitin da za a kai shi tana da kyau tana daya daga cikin asibitoci masu kyau da iya aiki a duniya, ina sa ran ko minene za su gano In-Sha-Allah ki kwantar da hankalinki”
Na gyada masa kai sannan na juyo na fara tafiya kamar kazar da kwai ya fashewa, babu komai a zuciyata sai tausayin Ahmad da kuma zargin kaina domin a wannan assabar din guri ya fito, ban san ko ya biya ta wani gurin ba, amman tabbas na san ranar ce abun ya same shi. Jinginawa nai jikin wani gini ina hawaye, wayata tai ringing da na duba sai na ga number Hafiza, share hawayen nai na dauki kiran.
“Hello”
“Halima kina ina?”
“Dan Allah kina kusa da Mama?”
“Eh ita tace a kira ki ai ta duba bata gan ki ba”
“Bata wayar”
Ina jin sallamar ta a kunnena sai na fashe da kuka.
“Mama na fita na zo nan asibiti Ahmad ba shi da lafiya”
“Subhanallahi miya same shi?”
“Hannun shi ke ciwo, kuma likitan yace ba a gano matsalar shi ba an yi hoto ba aga komai ba, Mama tun ranar assabar din daya bar gurin be sake lafiya ba har yau”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, kina asibitin ne?”
“Eh Mama tsoro nake ji”
Na fada ina kuka domin har ga Allah tsoron nake ji.
“Ikon Allah abu kamar na iska? Ki kwantar da hankalinki za ku zo yanzu In-Sha-Allah”
“To”
Na kashe wayar ina share hawayena, sannan na nufi dakin da yake na tura na shiga, ban samu Siyama a dakin ba shi kadai na samu a zaune kamar dazun, a take hawaye suka fara wanke min fuska amman shi murmushi yake min wanda zai kwantar min da hankali, karasa nai kusa da shi na saka hananyena duka biyu na rika fuskarsa ina ta kallonsa har ga Allah ban tana jin son sa da tausayinsa a raina ba irin yau.
“Tun ranar da ka bar gurina baka sake lafiya ba, ba a gano dalilin ciwon nan naka ba, Ahmad ba zan daina zargin kaina ba, idan wannan ciwon be barka ba zan yafewa kaina ba, na dade ina jin tsoro bana son mutane suna samu matsala saboda ni, kuma ina ji a jikina cewar ni ce sila....”
“Shiiiiiiiiiiiiiiiiii”
Ya dora hannunsa saman bakina.
“Ke baki dogara da Allah ba ne? Kin gani saboda gudun hakan yasa nace kar a fada miki, zaki saka damuwa a ranki har ciwonki ya taso, sannan za ki so ki fara magana marar kyau har ki sa a fara zargin wani abu, musamman ma Hajiya ta ko Siyama, dan Allah Lims ki bar wannan a matsayin sirrin mu, bana son wani yace zai ga laifinki ko ya tsane ki a yanzu, kina bukatar farinciki ko bana raye, and I'm sure idan ba ki samu a gurina ba Hajiya da Siyama za su ba ki, saboda sun san ina son matata sosai...”
Ya karasa yana sumbatar hannuna. Ban san lokacin da na fashe da kuka ba, na rumgume shi ina jin kamar akwai abunda Ahmad ya boye min, har ga Allah ba zan daina zargin kaina a kan ciwon Ahmad ba domin a lokacin da be aure ni ba abun ba haka yake ba, why sai yanzu? Ko dai ni din ba alheri ba ce a gurin jama'a? Sanadina ya rasa yarsa, yanzu kuma ace ya zama mijina kuma ta kamu da ciwo? Ina kokarin tsayar da kukana zancen Siyama da na Doc Nura ya fado min a rai, cewar a daren assabar din data gabata abun ya same shi and a wannan assabar din yana tare da ni ai kuma daga ita ne be dawo ba, hakan na nufin a ranar ne ya kasa kai kansa gida? Kuma a wannan ranar he hold my hand wata kila daga nan abun ya same shi.
“Abu kamar na iska”
Maganar Mama ta dawo min, no wait a daren ma ai ya gaisa da Abdallah, kuma Abdallah zai iya masa wani kofi, indai har ransa ya bace, i can remember ni ma ya taba min a lokacin da ya bukaci na shiga motarsa na ki sai an rasa mai napep din da zai dauke ni, and i lokacin da na auri Abdulhamid ma ya taba min na kasa girki, ya taba min wayata tsage ba tare da ta fadi ba, and yayi ma Abdulhamid ma, tabbas zai iya yi ma Ahmad inda har za a duba ace ba a ga komai ba tabbas Abdallah ne.
Shine abunda zuciyata ta raya min kai tsaye, domin a wannan ranar Ahmad ya rike hannuna har gaban Abdallah kuma na san hakan ba dadi zai masa ba, secondly the way da ya ba Ahmad hannu su gaisa ba dan Allah bane, how Abdallah zai yi wani murna ya aure ni? Wanin ma wanda ya bukaci na daina aiki a kamfaninsa saboda baya son taraiya mu...
Ban san lokacin da na mike tsaye da sauri ba hankalina yai mugun tashi.
“What...?”
“Ya kamata naje gida ba su san na zo nan ba gashi yamma ta yi”
Kallona yai from head to toe.
“Ji veil din da kika fito da shi Lims, nasa doguwar riga ce amman ina bukatar ki rika rufe min jikina”
“Zan saka next time, zan dawo anjima kadan...”
Na fada ina nufar kofa da sauri sai ya kira ni.
“Hey Lims are you okay?”
“I'm fine”
Na fada ina kokarin kwantar da hankali.
“Okay come here and kiss me”
Dawowa nai na yi kissing dinsa sai ya rumgume ni da dayan hannun nasa.
“I love you”
Ya rada min sannan na sake shi na mike tsaye na dauki purse dita na fice daga dakin. A phone list dina na shiga na nemo numbersa da ke kan gmail nawa na danna masa kira da sabon line na, ringing rai sai da ta kusa katsewa sannan ya daga da muryar da ke nuna be san mai magana.
“Abdallah kana ina?”
Yana jin muryarta ya gane ni ce mai magana.
“Halima.....”
Yayi shiru sai kuma ya amsa.
“Ina gida”
“Wane gidan?”
“Gurin Hajiya”
Kashe wayar nai na nufi hanyar fita daga ward din ina ta sauri kar na hadu da su Mama.
*Where are are the classy ladies 🤔 mata yan kwalissa ga awwaba scent tazo maku da hadadun turarukan wuta humra body oil turaren jiki na tsuguno da kayan gyaran jiki kaman dilka scrub organic soap 🧼 da sauransu akan farashi daidai aljihu say no karnin da warin damshi na lokacin damina zaaiya samunmu a wannan lqmbobin 09137294470 08034236800*
7/21/21, 11:11 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
6️⃣0️⃣
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Shine abunda na furta ina fashewa da kuka, a yanayin yadda nake ganin fuskarsa da kuma yadda ya rike hannun ya isa ya sanar min da irin azabar da yake ji, wacce nake jin kamar ace akwai abunda zan iya a dauke masa ciwo gaba daya, da sauri na fito daga dakin da zimmar zuwa dakin da Doc Nura yake domin na san asibiti tun da ba yau na fara shigowa ba, a kujerar dake kusa da dakin na yi arba da Siyama zaune tana latsa wayarta tana ganina ta mike tsaye.
“Ciwon ya tashi kenan?”
Ban ko kula ta ba na nufi hanyar da zata sadani da dakin likita ina kuka, kamin na karasa mutumen da ke gadin kofar office din ya tare ni.
“Likita nake nema ciwon Ahmad ya tashi”
“Baya office dinsa tun dazun ya fita”
Juyawa nai da gudu na koma dakin sai na samu likitan da wasu likitoci biyu suna tsaye a kansa, Siyama kuma tana gefe tsaye tana kuka, belt din suka kwance suka sake saka masa wani sannan sukai masa allura.
“Dan Allah ku je waje..... ”
Ni da ita muka fito daga dakin muka tsaya a waje, ita kuka ni hawaye.
“Ki yi hakuri zai samu lafiya in Allah ya yarda”
Na fada ina dafata domin a yadda ita take kuka dole ne ni tasa ni na hade nawa kukan na zama jaruma na lallashe ta.
“Ina fatar hakan, baya son muna zuwa kusa da shi saboda kar mu ga halin da yake ciki, tsoro na ke ji ina jin kamar.... kamar.... Yaya mutuwa zai yi.....”
Na yi saurin rufe mata baki.
“Haba dai cuta ai ba mutuwa ba ce, zai samu sauki In-Sha-Allah”
A lokacin ne wani kukan ya zo min, tana da gaskiya ni da ita za mu iya rasa shi, saboda haka suka rasa yarsa, idan har ya kasance ni ce sila fa? What if ya kamu da wannan ciwon ne saboda ya aure ni? Ban raba dayan biyu ba Doc Nura ya fito daga dakin, ya nufo inda nake tsaye ni da Siyama yai mana maganar da zata kwantar mana da hankali cewar Ahmad zai samu sauki. Sai da ya wuce zuwa wani gurin sannan Siyama ta bude dakin ta shiga, ni kuma na bi bayan likita na cika kafa kamin ya shige na cin masa.
“Doc dan Allah ina son magana da kai”
Juyowa yai ya kalleni.
“Ina jin”
“Dan Allah miye abunda yake damun Ahmad?”
Shiru yai kamar mai nazari.
“Hajiya bata fada miki ba?”
“Ta fada min tace ba a san ko minene ba amman ina son kara ji daga bakinka”
Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya ce.
“Gaskiya ne, an yi duk wani hoto daya kamata amman ba a ga komai ba, kuma shi yace yana jin ciwo yana masa yawo a hannun”
“Amman tun yaushe abun ya fara?”
“Yace min ranar assabar da dare, ya fito daga gurin abokinsa da dare, wai be iya kai kansa gida ba sai da ya kira direbansu ya kawo shi, na tambaye shi ko ya ci wani abu ne ko kuma hannun ya bugu da wani abu? Yace min a a yanzu jibi za a fita da shi, asibitin da za a kai shi tana da kyau tana daya daga cikin asibitoci masu kyau da iya aiki a duniya, ina sa ran ko minene za su gano In-Sha-Allah ki kwantar da hankalinki”
Na gyada masa kai sannan na juyo na fara tafiya kamar kazar da kwai ya fashewa, babu komai a zuciyata sai tausayin Ahmad da kuma zargin kaina domin a wannan assabar din guri ya fito, ban san ko ya biya ta wani gurin ba, amman tabbas na san ranar ce abun ya same shi. Jinginawa nai jikin wani gini ina hawaye, wayata tai ringing da na duba sai na ga number Hafiza, share hawayen nai na dauki kiran.
“Hello”
“Halima kina ina?”
“Dan Allah kina kusa da Mama?”
“Eh ita tace a kira ki ai ta duba bata gan ki ba”
“Bata wayar”
Ina jin sallamar ta a kunnena sai na fashe da kuka.
“Mama na fita na zo nan asibiti Ahmad ba shi da lafiya”
“Subhanallahi miya same shi?”
“Hannun shi ke ciwo, kuma likitan yace ba a gano matsalar shi ba an yi hoto ba aga komai ba, Mama tun ranar assabar din daya bar gurin be sake lafiya ba har yau”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, kina asibitin ne?”
“Eh Mama tsoro nake ji”
Na fada ina kuka domin har ga Allah tsoron nake ji.
“Ikon Allah abu kamar na iska? Ki kwantar da hankalinki za ku zo yanzu In-Sha-Allah”
“To”
Na kashe wayar ina share hawayena, sannan na nufi dakin da yake na tura na shiga, ban samu Siyama a dakin ba shi kadai na samu a zaune kamar dazun, a take hawaye suka fara wanke min fuska amman shi murmushi yake min wanda zai kwantar min da hankali, karasa nai kusa da shi na saka hananyena duka biyu na rika fuskarsa ina ta kallonsa har ga Allah ban tana jin son sa da tausayinsa a raina ba irin yau.
“Tun ranar da ka bar gurina baka sake lafiya ba, ba a gano dalilin ciwon nan naka ba, Ahmad ba zan daina zargin kaina ba, idan wannan ciwon be barka ba zan yafewa kaina ba, na dade ina jin tsoro bana son mutane suna samu matsala saboda ni, kuma ina ji a jikina cewar ni ce sila....”
“Shiiiiiiiiiiiiiiiiii”
Ya dora hannunsa saman bakina.
“Ke baki dogara da Allah ba ne? Kin gani saboda gudun hakan yasa nace kar a fada miki, zaki saka damuwa a ranki har ciwonki ya taso, sannan za ki so ki fara magana marar kyau har ki sa a fara zargin wani abu, musamman ma Hajiya ta ko Siyama, dan Allah Lims ki bar wannan a matsayin sirrin mu, bana son wani yace zai ga laifinki ko ya tsane ki a yanzu, kina bukatar farinciki ko bana raye, and I'm sure idan ba ki samu a gurina ba Hajiya da Siyama za su ba ki, saboda sun san ina son matata sosai...”
Ya karasa yana sumbatar hannuna. Ban san lokacin da na fashe da kuka ba, na rumgume shi ina jin kamar akwai abunda Ahmad ya boye min, har ga Allah ba zan daina zargin kaina a kan ciwon Ahmad ba domin a lokacin da be aure ni ba abun ba haka yake ba, why sai yanzu? Ko dai ni din ba alheri ba ce a gurin jama'a? Sanadina ya rasa yarsa, yanzu kuma ace ya zama mijina kuma ta kamu da ciwo? Ina kokarin tsayar da kukana zancen Siyama da na Doc Nura ya fado min a rai, cewar a daren assabar din data gabata abun ya same shi and a wannan assabar din yana tare da ni ai kuma daga ita ne be dawo ba, hakan na nufin a ranar ne ya kasa kai kansa gida? Kuma a wannan ranar he hold my hand wata kila daga nan abun ya same shi.
“Abu kamar na iska”
Maganar Mama ta dawo min, no wait a daren ma ai ya gaisa da Abdallah, kuma Abdallah zai iya masa wani kofi, indai har ransa ya bace, i can remember ni ma ya taba min a lokacin da ya bukaci na shiga motarsa na ki sai an rasa mai napep din da zai dauke ni, and i lokacin da na auri Abdulhamid ma ya taba min na kasa girki, ya taba min wayata tsage ba tare da ta fadi ba, and yayi ma Abdulhamid ma, tabbas zai iya yi ma Ahmad inda har za a duba ace ba a ga komai ba tabbas Abdallah ne.
Shine abunda zuciyata ta raya min kai tsaye, domin a wannan ranar Ahmad ya rike hannuna har gaban Abdallah kuma na san hakan ba dadi zai masa ba, secondly the way da ya ba Ahmad hannu su gaisa ba dan Allah bane, how Abdallah zai yi wani murna ya aure ni? Wanin ma wanda ya bukaci na daina aiki a kamfaninsa saboda baya son taraiya mu...
Ban san lokacin da na mike tsaye da sauri ba hankalina yai mugun tashi.
“What...?”
“Ya kamata naje gida ba su san na zo nan ba gashi yamma ta yi”
Kallona yai from head to toe.
“Ji veil din da kika fito da shi Lims, nasa doguwar riga ce amman ina bukatar ki rika rufe min jikina”
“Zan saka next time, zan dawo anjima kadan...”
Na fada ina nufar kofa da sauri sai ya kira ni.
“Hey Lims are you okay?”
“I'm fine”
Na fada ina kokarin kwantar da hankali.
“Okay come here and kiss me”
Dawowa nai na yi kissing dinsa sai ya rumgume ni da dayan hannun nasa.
“I love you”
Ya rada min sannan na sake shi na mike tsaye na dauki purse dita na fice daga dakin. A phone list dina na shiga na nemo numbersa da ke kan gmail nawa na danna masa kira da sabon line na, ringing rai sai da ta kusa katsewa sannan ya daga da muryar da ke nuna be san mai magana.
“Abdallah kana ina?”
Yana jin muryarta ya gane ni ce mai magana.
“Halima.....”
Yayi shiru sai kuma ya amsa.
“Ina gida”
“Wane gidan?”
“Gurin Hajiya”
Kashe wayar nai na nufi hanyar fita daga ward din ina ta sauri kar na hadu da su Mama.
*Where are are the classy ladies 🤔 mata yan kwalissa ga awwaba scent tazo maku da hadadun turarukan wuta humra body oil turaren jiki na tsuguno da kayan gyaran jiki kaman dilka scrub organic soap 🧼 da sauransu akan farashi daidai aljihu say no karnin da warin damshi na lokacin damina zaaiya samunmu a wannan lqmbobin 09137294470 08034236800*
7/21/21, 11:11 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
6️⃣0️⃣