← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 136

Sashe 60

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Hajiya ta ya zan cire abunda ba ni na sakawa kaina shi ba? Da ina da iko da dama da ban bar zuciyata ta kamu da son Halimatu ba tun farko”

“Dan Allah na hada ka da girman Allah ka bar yarinyar nan, ka daina shiga zabgarta ka manta da ita a rayuwarka”

“Idan umarni ne zan bi, idan kuma shawara to zan amsa miki da cewar Wallahi ba zan iya ba Hajiya, Soyayyar Halimatu a zuciyata kaddara ce, Hajiya na san Halimatu tun kamin tai aure, amman Allah be dora min kaunarta sai da tai aure ta haifi yara biyu, da igiyar aurenta na kamu da sonta Hajiya, shim ba ki yi mamaki ba? A yanzu na tabbatar ba son ne kawai a kaddarar da ke tsakanina da ita ba, har da taimakon rayuwarta da tsaya mata a wasu abubuwa, kamar yadda Allah yake bawa wani bawa abinci a karkashin wani bawa, ko yai maka kyauta da hannun wani bawan”

Taso yai ya baro kujerarsa ya zauna kasa yana kallon mahaifiyarsa da duba irin na yaro mai neman dauki a gurin mahaifiyarsa.

“Dan Allah karki hana ni yi mata ko wane irin taimako Hajiya, yarinyar tana cikin damuwa tana bukatar mutane a kusa da ita”

“Halima ba yarinya ba ce, ka daina mata kallon yarinya, duk mace da zata haifi yara hudu ta san me take”

Hajiya ta fada tana kallon wani gurin fuskarta a hade.

“Yarinya ce Hajiya haihuwar da taima ta sauri ce, har yanzu Halimatu bata haura 26 ba, tana da rauni da yasa Hajiya, damuwa ta mata yawa yanzu har rasa tunaninta take, damuwarta kawai take iya karantowa idan tai losing memory ta”

“Ba damuwa bace matsalar Hassan ya fada ai, tana shaye-shaye kuma duk mai shaye-shaye dole ya hadu da irin wannan matsalar gasu nan muna gani sai haukacewa suke, ni ina mamakin wace irin damuwa ce da ba za abar wa Allah ba, damuwar me ma? Idan bayan cin amanar da tai Hassan ya sake ta... ”

Bata karasa Abdallah ya tafi numfashinta.

“Hajiya da gaske kin yarda Halimatu ta aikata abunda Abdulhamid yake zargi? Na rasa gane dalilin tsanar Halima da kike a yanzu, mace da za tai aure ba ta dace ba, ayi ma yarta fyade mijinta ya saketa saboda haka, ta dawo ta bar yayanta da aikinta ta auri d'anki da bashi da lafiya wata kaddarar ta fada mata a keta mata haddi da aurenta, kuma d'anki yai mata sakamako da saki a lokacin da take bukatarsa ki kasa ganin tausayinta? Wallahi na tabbatar da Abbah yana da da Abdulhamid be isa ya saki Halimatu ba, domin yana yawan fada yayansa ba su isasu taba masa yan'uwa ba, yan'uwan ma Baba Dahiru mutunen da be a shi da amini irinsa, duk inda Abbah ya saka kafa kafarsa tana nan, ina tuna lokacin da Abbah yake mana wasiya da son zumunci da taimakon masara shi, musamman Baba Dahiru, babu irin neman arzikin da ba su yi tare da Abbah ba, amman shi Allah be bashi ba, daga karshe ya koma ciwon kafafuwa ya tare a gida, sannan Allah be ba shi yaya maza ba sai a lokacin da tsufa ya kama shi balle su taimake shi, matan kuma babu wata mai tsiyayar sana'ar da zata iya taimaka masa sai Halimatu da take aiki kamin ta rasa aikin nata, yanzu macen da ta taso a irin wannan rayuwar bata baki tausayi ba?”

Tsawa Hajiya ta daka masa.

“Bata ba ni ba...! Bana kaunar yarinyar nan Husaini, ita kadai tasan bakin nufin da ke zuciyarta shiyasa take haduwa da abubuwa, da gangan ta taki soyayyarka ta auri dan'uwaka, ta barka kana ta wakenta, shi kuma yana can zuciya cike da kuncinta, ai ko dan hallacin da kake mata be kamata tai maka haka ba, ta san kana son ta kuma yar ta yarda ta auri dan'uwanka bayab kuma ta san ba da zuciya daya zata zauna da shi ba, ko da ma zaman ya yiyu da wane ido zata kalleka? Ina da tabbacin Halimatu taja Hassan a jikinta ne ta nuna masa zata aureshi saboda ta musguna maka, ashe ba kai kadai tai niyar ciwa mutunci ba duka ku biyun ne, ina da tabbacin Hassan ba zai taba yafe maka ba idan har ya gano ka taba sonta kuma ka bari ya aureta, taya zan so yarinyar Husaini ka fada min, ku yan biyu ne a mahaifa daya kuka rayu, ciki daya kuka fito a rana daya ta sani kuma ta aikata wannan abun? Ba yanzu ba, gaba na ke hange tsabanin da mahaifinku yake gudun kar ku samu kuna daf da rusgawa a wannan ramen matukar baka cire kanka daga dramar wannan matar ba”

Ya girgiza mata kai.

“A'a Hajiya, kaddarar ce a haka, ina da tabbacin da ni ta aura da ta samu jindadin da ta rasa har ma da doriya, amman wahala da bakinciki be kare mata ba shiyasa ta auri Abdulhamid sai waenan abubuwa suka faru da ita”

Wannan karon kallon tsoro Hajiya tai masa.

“Na bonu wannan wane irin abu ne Husaini? Wani irin so kake mata haka?”

Hajiya na masa tambayar ya lumshe ido ya dora kansa saman kafarta ta dama yana sauke ajiyar zuciya.

‘Wani irin so ne, wanda hannu be isa ya rubuta ba, ba ki ba zai iya furtawa ba, zuciya ta cika da kaunar Halimatu, rai na ta aikin begenta ta mamaye illahirin jiki da tausayinta, babu gurbin ganin laifinta, balle kiyayya ta samu muhalli...’

A zuciyarsa yake wannan maganar a fili kuma sai ya bude idon ya dago kansa ya kalli Hajiya ya ce.

“Tausayinta kawai na ke”

“Ka fara bani tsoro, duk yadda na ke tunanin abun nan ya wuce nan, sai dai ina gargadinka kar ka kuskura ka bar dan'uwanka ya san cewar wata alaka ta taba shiga tsakaninku”

Shiru yai na few minutes.

“Hajiya kin san miyasa na zo yanzu? So nake ki saka Abdulhamid ya maida aurensa da Halimatu”

Kallonsa Hajiya ta tsaya yi kamin ta mike tsaye.

“ Ada dai ina maka kallon mai hankali da tunani, to yanzu na gano baka da shi, Halimatu ta dauke ta tafi da shi, ai zamanta a gidan dan'uwanka ma hatsari gareku sai yanzu na gano, kuma Al-hamdulillah da ya saketa Allah ya hada kowa da rabonsa”

“Wallahi Hajiya tana bukatar Abdulhamid a kusa da ita, dazun ma da ya rasa tunaninta maganarsa take min, hannunwanta ta nuna min ce min take na kalla na ga yadda Abdulhamid ya rabu da ita, ya kasa yadda da ita ya kasa riketa....”

Tabe baki Hajiya tai.

“Wani makircin sai mata, kai miya kai ka gurinta?”

Be boye mata komai ba, ciki har da marin da Ahmad yai mata.

“To Allah ya kyauta yai mafita”

Shine abunda Hajiya ta fada ta shige dakinta, ta kasa samun muhallin da zata sake kaunar Halimatu a ranta, ada kam tana kaunarta sosai amman ban da yanzu da take ganin kamar Halimatu na son tarwatsa mata kan yaya ne. Sai 10 ya bar gidan bayan ya yanke shawarar tunkarar Abdulhamid kai tsaye da maganar.

AHMAD POV.

Ya kasa barin kowa yai jinyar yarsa ciki kuwa har da mahaifiyarsa, zuciyarsa ta cika da rauni har yake ganin idan ya daga kusa da Baby Namra zai iya rasata, mutuwar mahafiyarta yake tunawa and think he's not ready to bear the pain.
After yayi losing mahaifiyarta ace yanzu ita ma ya rasa ta? The pain was almost more than he could bear.
Tun da aka shigo da ita ICU bata motsa ba, yana ganin numfashinta yana tafiya yasan yarsa tana da rai, amman ba shi da tabbacin za ta tashi.

Iskar bakinsa ya busar yana neman ta inda iska zai shiga hancinsa ya huda zuciyarsa ya zauna ko ya samu sassauci. Be taba jin ya tsani wata hallita ba kamar yadda ruhinsa ya cika da tsanar Halimatu. Abubuwa mabanbanta zuciya take raya masa, wata kila wulakanta masa Y'a akai har ta kai ta je waje ta fada rijiya, wata kila ma tsawa tai mata shiyasa ta ji haushi ta fada rijiya, ko kuma ta koreta daga gidan ita kuma taje gurin rijiyar, what if yarta ce ta jefata? Ya mai akai ta fada rijiya?

“Ki yi addu'a kawai yata ta rayu, ya rabb pls save me”

Ya furta yana maida numfashi da karfi, sannan ya kalli tafin hannunsa, wanda tun a lokacin da ya mare Halimatu hannunsa yai sanyi har yanzu, maybe because be taba marin mace ba sai yanzu kusan shi a rayuwarsa ma be taba dukan kowa ba sai ita. Ji yake ya zama wani irin mugun mutum idan ya tuna ta, yadda zai sarrafa rayuwarta idan yarsa ta mutu kawai yake tunani, kamin ya kai hannun nasa ya rike hannun yarsa..........
Runtse ido yai be bude ba sai da Hajiya ta shigo tare da likitan da suka fita dazun.

“Gwarzo ya kamata kaje gida ka huta fa, 12 ta yi”

“Hajiya ina son na maida ita Abuja a akwai wata asibiti a can wata kila za ta fi samun kula fiye da nan”

Likitan ya matsa kusa da Namra da sauri ya taba ta, babu alamun numfashi a tare da ita, a take hankalinsa ya tashi ya fara bata taimakon gaggawa amman mai kira yayi kira wanda ya bada aro ya karbi kayansa, fita yai ya shigo da wasu likiton abunda ya kara tadawa Ahmad hankalin kenan, ta yadda ya ga fuskar ko wannensu da yadda suka ja zanen asibitin suka rufe ita sai ya zuba hannayensa aljihu ya daga kansa sama ya rumtse ido.

“Na yi imani da kai Allah, kai kake kashewa ka raya, La'ilaha illallahu..... ”

Ya furta yana jin kamar babu komai a zuciyarsa, duk kuwa da ya kasa gasgata yarsa ta tafi ta bar shi da gaske. hajiya kam fashewa tai da kuka tana ta salati har ta kasa tsayi sai da aka fito da ita daga dakin.
Dafa shi da Doc Nura yai ne yasa shi bude ido ya kalleshi.

“I'm sorry Gwarzo take heart”

“Da gaske ta rasu?”

Ya gyada masa kai sai ya runtse ido, ya bude yana murmushi.

“Subhanallah”

Ya juya ya kalli gawar Baby Namra, sannan ya sake kallon Doc Nura.
Chapter 60 · 0% Book details