← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 136

Sashe 67

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mai nepep din ya fada yana fito mana da kayan mu, da na daga kaina sai na hango wata kafirar bakar mota mai bakin gilashi wacce ban taba ganin irinta a fili ba sai a fina finai, mai motar kamar ni yake jiran na dago na kalleshi sai ya sauke gilashin motar a hankali, me zan gani? Mutumen nan ne wanda na taba gani a lokacin da na farka a asibiti kafirin nan, wani irin faduwa gabana yai a take na nemi natsuwata na rasa.

“Hasbiyallahu wani'imal wakeel”

Na furta ina cigaba da kallonsa kamar yadda shi ma yake kallona fuskarsa ba yabo ba fallasa.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”

Na sake furtawa daga Aisha har Husna kallona suke kamin su kalleshi sai yai sauri daga gilashin motar yai ribas ya juya inda ya fito.

“Kin san shi ne?”

Mai Napep din ya tambaya.

“No”

“To Allah ya sawwake yanzu mutane abun tsoro ne, garkuwa ake da mutane ta ko'ina”

Na dan tabe baki.

“Allah na tuba to ni idan an yi garkuwa da ni me za a tsinta?”

“Ai ba shi mutane suke dubawa ba, kuma ai akwai matsafa masu dauke mutane, sai dai kuma idan sonki yake”

Na sake duban mai napep din da kyau kamin nai murmushi na girgiza masa kai.

“Ni kan yanzu ai na girmi so”

“Ta ina? Ga ki kyakkyawa da jini a jika? ”

Daga ni har shi har kannen da muke tare dariya mukai, Maganarsa sai ta tuna min da wata maganar marar dadi da Aminu ya taba fada min.

“Look at you duk kin yi wani muni kin tsufa..... ”

Ajiyar zuciya na sauke na dauki wasu kayan na shiga da su cikin gida ni da Husna Aisha kuma ta tsaya sallamar mai napep din sarkin bargwanci.

Na jidadin ganin Mama da nai duk kuwa da kasancewar na ganta jikin nata sai a hankali amman hakan be hanani jindadin ganin farincikina ba, ba ita kadai ba kowa a gidan ya jidadin dawowata musamman ma yarana wadanda suka rika tsalle kamar na shekara bana gidan, Amal ta zo jikina ta zauna tana ta zuba min shagwaba.

ABDALLAH POV.

Luma biyu yai ya ji kamar ba zai iya cin abinci ba sai ya aje spoon din ya kurba ruwan dake gabansa.

“Lafiya kake yau?”

Ya dago a hankali ya kalli Suwaiba sai ya amsa mata a hankali tare da tashi ya bar mata dinning.

“Bana jin dadi ne”

Da kallo ta bishi ta tabe baki.

“Ai shine daidai da kai na san da ba haka nai maka ba ba zaka fita safgar wannan shegiyar Halimatun ba, amman yanzu da Abdulhamid ya san gaskiya ai dole ka kama kanka dan na san zai taka maka burki da wuri, tun da ku maza ba kunya ce da ku ba yanzu nan sai kace zaka aureta, idan anyi magana kace tausayinta kake to sannu sahabi.... ”

Ta cigaba da cin abincinta ranta fes duk kuwa da kasancewar bata san makasudin bacin ran mijin nata ba, sai dai ta san baya rasa nasaba da abunda ta fadawa Abdulhamid domin a yadda ta ga ransa ya bace ta san ba zai bar maganar ba!

Dakinsa ya shiga ya kwanta ya rasa abunda ke masa dadi, a duk lokacin da ya tuna maganar Hajiya ta gatangar da ta gina tsakanina da Halimatu sai yaji wani abu ya tokare masa zuciya, be tabbatar yana sonta da gaske ba sai a yanzu da yake jin kamar Hajiya na kokarin rabashi da ruhinsa ne. Ya rasa dalilin Hajiya na kin masa uzuri ya rasa dalilin hajiya na tsanar Halimatu tun daga lokacin da ta auri Abdulhamid, yes yasan tayi kuskure na auren Abdulhamid bayan kuma ta san yana sonta, amman ai itama mutun ce kamar kowa ko? Zata iya daidai zata iya akasin haka, then miyasa Hajiya ba zata kalli wannan tai mata uzuri ba? Ko da yake yanzu ba laifi Hajiya ba ne laifin Abdulhamid na yi mata maganar da nuna bacin ransa. Bayan kuma ba shi da wata hujja a yanzu domin da yana sonta kuma ta damu da ita da be sake ta da be juna mata baya ba. Hannunsa ya kai ya dafa zuciyarsa yana kara fadawa wani kogin tunanin.

Wai yanzu duk wani abu da yake yi ma Halimatu janye zai yi? Ba zai sake mata komai ba kenan? Babu wata alaka da zata sake shiga tsakaninsu? Ya tambaya kansa yana jin wani irin shauki da son ganin fuskarta.

______________________

Anya Abdullahi zai iya jurewa?
Da gaske Aljanun murja ne suka taso?
Waye yake bibiyar Halimatu kuma a yanzu?
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy

3️⃣5️⃣

Kasa cewa komai yai  ya tsaya a gurin kamar an dasashi, Sadi kan sai gumi yake hadawa abun ka da marar gaskiya, Murja kuma na can dakinta tana aikin ihu kamar da gaske Aljanun ne suka ziyarce ta har da wani yare take shi ba yarbanci ba, ba kuma iyamuranci ba.

“A kaita asibiti, no gurin malamai”

Fadi ya fada wiki wiki da ido, sai Aminu yai masa murmushi tare da gyada masa kai alamar gamsuwa.

“Za a kaita”

Ya amsa masa sannan ya nufi dakinsa jikinsa babu kwari, saman gadonsa ya zauna sai ya rasa abunda zai fara tunani, korarsa da akai a gurin aiki ko kuma tararda dan'uwansa tare da matarsa? Kwantawa yai saman gadon yana ta kallon silin.

“Aminu ka ji tsoro Allah abunda kake mana baka kyautawa, ka rika tunawa kana da yara kana da mata, ace magidanci kamar idan ya bar gida ba zai dawo ba sai karfe daya ko biyu na dare...?”

“Ke Halima a nan gidana ne ina da yancin shigowa a lokacin da nake so na fita na lokacin da na ke so, ba ki isa ki saka min doka a gidana ba”

“Ba doka nake son saka maka ba, abunda kake yi nake kokarin nuna maka illarsa, duk abunda kai wa matar wani sai an yi ma taka, kuma duk abunda kai wa yar wani sai an yi wa yarka....”

“Idan iskancin kike so ni ban hana ki yi ba, ga ki ga guri har kya fada min wani wai sai an yi ma yar wani matar wani dan baki da hankali”

“Allah ya tsare ni, ban aikata zina ina budurwa ba ba zan aikata da aurena ba, ga hakkin yayana ga na iyayena ga na mijina ga na ubangijina? Wallahi ba zan iya ba”

Ya fada tana share hawayenta sannan ta tashi ta bar masa dakin. Tuna wannan yasa shi share hawayensa ya rumgume hannayensa a kirjinsa. A yau na mallakawa murja komai, ita ke saka masa duk dokar da tai mata, be isa ya kai 9 a waje ba, be isa ya dawo gidan ba tare da saninta ba, amman hakan be hana ta cin amanarsa ba. Abunda be taba mafarki ba, domin a lokacin da zai aureta sai da yai bincike mai karfi aka tabbatar masa da tarbiyarta sannan ya aureta, sannan ya yaba da shigarta da hankalinta shiyasa ya aureta ashe be tsira daga abunda yake gudu ba, kuma ta rasa wanda zata aikata da shi sai dan'uwansa uwa daya uba daya! Wani irin abu yaji ya tsaya masa a kirji ya danne masa numfashi har sai da yai saurin kifewa a saman gadon ya runtse ido sannan ya samu  sassauci.

“Allah yasa ka gane kuskuren da kake aikatawa da wuri, ko dan yaranka..... ”

Maganar Halimatu ta sake dawo masa.

“Na gane Halimatu na gane......”

Ya fada yana fashewa da kuka wasu hawaye masu zafi suna sauko masa. Kamar an tsikare shi sai ya zabura tai saurin tashi zaune. So da gaske Halimatu take da fada masa cewar Sadi yai ma Namra fyade? Sadi ya daka masa wuka har sau biyu kenan? Yayi saurin tashi zaune, ji yai babu wanda yake bukatar gani a yanzu kamar Halimatu da yayanta.

Tashi yai ya fice daga gidan gaba daya, a bakin gate ya samu abun hawa ya fada masa unguwar su Halimatu, kamin su isa duk sai ya tsawalla kamar wanda ya shekara ba ga yaranba. Sai kuma yai rashin sa'a ya tarar bata gidan wai ta tafi dauko yaran daga School. Kai tsaye Scul din ya wuce a can ya sameta ta tana kokarin taron napep tana rike da hannun yaranta. Sai a lokacin yake jin rashin kyautawa ta ya zai barta ita kadai tana daukar responsibility ba yaransa bayan yana raye? Gaba daya sai jikinsa yai sanyi, karasa yai kusa da su, kallo daya tai masa ta dauke kai sai ya koma gaba Namra ya risina ya kai hannu ya shafa fuskarta yana murmushi.

“Daddy ina wuni?”

Kasa amsawa yai sai ya rumgume ta hawaye na sauko masa. Tun yana yi a hankali har ta kai mutane na kallonsa.

“Miye haka? A cikin jama'a muke fa, ka sake ta gida zamu je”

Sakinta yai ya dago kai yana kallon Halimatu wacce ke watsa masa wata uwar harara, kamin ya kai hannu ya shafa kan duka yayansa sannan ya mike tsaye ya share hawayensa, ita kuma taja yaranta sukai gaba, yana tsaye a bakin titin yana kallonsu har suka samu Napep suka shiga suka bar shi a gurin. Shi ma achaba ya hau ya dauki hanyar family house dinsu.
Ko da be fada ba kana ganinsa kasan yana cikin tsakanin damuwa, kamar yadda mahaifiyarsa ta karanta a fuskarsa. Gashi ya shigo mata har dakin bachinta babu sallama balle gaisuwa.

“Aminu lafiya kake?”

A lokacin daya dago kansa sai hawaye ta gani a fuskarsa.

“GOBENA Hajiya tunani nake yadda zata kara kasancewa....”

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, miya faru kuma?”

“Hajiya yanzu na gane, ba dan na rabu da Halimatu na rabu da arzikina ba, saboda na cutar da ita ne, hakkinta ba zai bar ni ba, samun irinta a duniyar nan sai an tona, kullum nasiha take min bata tana nuna min gazawarta, da gangan Hajiya da gangan nake kauracewa Halimatu sai nai wata uku hudu ban neme ta ba kuma a haka take hakuri da ni......”
Chapter 67 · 0% Book details