← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 65 OF 136

Sashe 65

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haka Abdallah yai ta ba ni kulawa fiye da yadda na cancanta, sai dai hakan ba karamin taba ni yai ba, miyasa Abdallah zai yi ta bani kulawa bayan na zabi auren dan'uwansa sama da shi? Bayan na yi masa zargin shi yai fyade? Anya na cancanci girmamawa da kulawa daga gareshi?

Duka yan gidansu yan'uwa na kusa da kawaye na sun zo ganina ciki kuwa har da mahaifiyar Aminu, ban da mahaifiyata, ko baba da bashi da wadacacciyar lafiya sai da ya zo ganina amman ban ga mahaifiyata ba, idan na tambaya sai ace min tana gida tana miko min gaisuwa hankalina be kwanta ba sai da nai waya da ita muka gaisa sai dai a yanayin da na jita kamar ba lafiya ba. Aisha da Hafiza ne suka labarta min yadda Mama da Baba sukai da mahaifin Baby Namra da kuma zirga zirgar gaisuwar da suka rika zuwa yi.
Kwana na biyu asibitin aka ba ni takardar sallama, a ranar da aka sallame ni a ranar Aminu ya kawo min ziyara, ba karamin mamaki ya kamani ba da nai arba da fuskarsa, domin a yanzu bayan Mahaifin Baby Namra babu wanda na tsana kamar shi, su biyun nan bana kaunarsu a rayuwata. Be zo min hannu biyu ba yayi min siyayya mai yawa, bayan mun gaisa be sake ce min komai ba kamar mai kunyata sai wani sunsun da kai yake baya son kallona. Nima ta bangarena ban da kallon tsana babu abunda nake masa, ko ya jikin da ya ce min kasa amsawa nai sai Husna ce ta amsa masa shi kuma ya rike hannun Adnan yana ta wasa da shi gwanin kunya. Muna haka Abdallah ya shigo wani tsaya yai cak ya kalleni ya kalli Aminu.

“Waye wannan?”

“Mahaifinsu Namra ne?”

Aisha ta amsa masa.

“Daman Namra tana da uba? Miya kawo shi nan? Naga dai ba Namra ce bata da lafiya ba mi ka zo yi?”

Dagowa Aminu yai ya kalleshi.

“Na zo duba jikinta?”

“Sai yanzu kake damuwa da jikinta? Lokacin da take gidanka ka kula da ita ne? Dan Allah mana tashi ka fice ko na saka a wulakantaka yanzu nan”

“Akwai alaka a tsakanin mu ba ka isa ka raba wannan ba, so ko ka so ko ka ki dole ne alaka ta cigaba da tafiya har a bada saboda akwai yaya a tsakaninmu”

Aminu ya fada yana mikewa tsaye

“Yayan da baka damu da su ba? Yaran da kanenka ya lalata yarka ka kasa yin komai? Malam zo ka wuce”

A fusace Aminu ya fice daga dakin, aiko Abdallah kamar jira yake sai yai kaina da masifa kamar zai cinye ni.

“Tsakanin ke da shi ban san waya fi wani hauka ba, taya mutumen daya aureki ya raba ki da danginki ya kuma can ya wulakanta ki ya ci zafinki ke da yar ki  yanzu zai zo dubaki har ki saurareshi? Wace irin mahaukaciya ce ke? Ko sonshi kike ne? Son shi kike?”

Yana ta maimaita min tambayar son sa na ke yafi a kirga be yi shiru ba har sai da na amsa masa a fusace hawaye na sauko min zuciyarta cike da wani irin bacin rai da bakinciki marar misaltuwa.

“Eh son shi nake shikenan?”

Yawo yake da idonsa a fuskata kamin ya gyada min kai.

“Yes shikenan....!”

Ya fice ya bar a ni a dakin ni da Aisha ban san lokacin dana fashe da kuka ba.

ABDULHAMID POV.

A natse ya shigo ya falon ya zauna bayan sun gaisa da Hajiyarsa sai shiru ya biyo baya alamar akwai damuwa a tare da shi, sai dai Hajiya bata lura da hakan sai aikin motsa furarta take.

“Hajiya mi yasa baki taba fada min cewar Abdallah yana son Halimatu ba?”

Da sauri Hajiya ta juyo ta kalleshi.

“Wace irin magana ce wannan? Taya Hussein zai so matarka? Wacce ka rabu da ita”

“Wallahi Hajiya zan iya dafa miki al'qurane cewar Abdallah yana son Halimatu, sai dai abunda ban gane ba kamin na aure ta yake son ta ko kuma bayan na aureta? Ko kuma bayan rabuwarmu?”

Hajiya ta aje kofin furar tana dan murmushi tace.

“Ba haka ba ne Husaini yana tausayinta ne kuma.... ”

“Abunda yake mata ya wuce tausayi Hajiya, ni ba mahaukaci ba ne na fahimci komai yanzu, kuma na san ke ma kin sani”

“Ni ban san komai ba kuma Husaini ba son Halimatu yake ba, hasalima duk wani taimako ita ce take neman yai mata”

Hajiya na rufe baki Abdallah na shigowa dakin fuska babu annuri ya kwaso fushinsa na asibiti ya shigo gidanta da shi. Har ya zauna be cewa kowa uffan ba, kamar ya san zancen a ake, sai dai a badini kalaman Halimatu ne suka taba masa zuciya. Hajiya ta watsa mata wata uwar harara kamin ta rufe shi da fada.

“Daga ina kake?”

“Asibiti”

Ya fada yana dan sakin fuskarsa shi sai yanzu ma ya ankara da ya shigo babu sallama kuma be gaishe da Hajiya ba.

“Abunda kake yi wa Halimatu yayi yawa Husaini gashi nan har dan'uwanka ya fara zarginka.... ”

Abdulhamid yai saurin tarar numfashinnta.

“Ba zargi nake ba Hajiya zahiri na gani, kawai abunda na masa ganewa, shin kamin na aureta ne yake sonta ko kuma bayan na aureta ne?”

Abdallah ya kalli Abdulhamid with confused.

“Saboda kawai ina taimakonta sai ya zama ina sonta?”

A take Abdulhamid ya daka matsa tsawa abunda be taba ba.

“Sonta kake Abdallah, ni ba mahaukaci ba ne abunda kake mata ya wuce taimako, kuma abun kunya ne ace na saki mata ka koma kana bibiyarta”

Tabe baki Abdallah yai.

“Daga kai har Aminu ba ku dace da zama mata kamar Halimatu ba gaba daya ba ku da hali ba ku da tunani... Kuma ba ku da tausayi... ”

“Eh sai kai gwani, je kai yi campaign ta aure ka”

Abdallah ya mike tsaye a fusace.

“Wai miye damuwarka da taimakon da nake yi ma mata ne? Ka riga ka ji baka bukatar zama da ita ka sake ta, to miye damuwarka da ni ko ita? Baka san cewa ina taimakon Halimatu tun kamin ka aureta ba?”

Abdulhamid ma ta mike tsaye.

“That's mean kana sonta tun kamin na aureta kenan? Miyasa ka bari na aureta bayan ka san kana sonta?”

“Wai minene matsalar ka Abdulhamid? Abdulhamid?”

“Kai ne matsala Abdallah? Taya taya taya zan saki mata twins brother naya rika bibiyarta?”

Abdulhamid ya fada cikin daga murya.

“Haram nai ko kuma taimakon da nake mata ne ba dace ba?”

“Ana barin halak ko dan kunya, kuma ko dan gudun zagin mutane, kuma ni cin fuska ne a gareni kuma abun kunya a gareka”

“Bana gudun zagin mutane, kuma wata halak din take baruwa Abdulhamid, wata halak din...!”

“Husaini......! ”

Tsawar da Hajiya dakawa Abdallah ne yasa Abdulhamid ficewa daga falon a fusace.

“Enough is enough, so ba hauka ba ne kana ta wahala akan yarinyar da ta kasa daga kai ta kalli soyayyarta a idonka, da gangan ta take soyayyarka ta auri dan'uwaka, ba ka da hankali ne kai? Yanzu hakan da ran dan'uwanka ya bace ya maka dadi kenan? Baka da magana sai ta Halimatu baka da time sai na Halimatu, baku taba fada da junanku ba sai akan yarinyar, to ya isa haka an kai karshe”

Ta karasa hawaye na sauko mata, Abdallah dai be ce komai ba all what he try to do ya saukar da fushinsa ya samu natsuwa.

“Daga yau sai yau, ban yafe ka sake shiga safgar Halimatu ba, ban yafe ka sake taimakonta da komai ba”

A rikice ya girgiza mata kai da sauri sai ta daga masa hannu.

“Fita ka ba ni guri”

Hannunsa ya saka ya dafe kansa kamin ya juya da sauri ya fice daga gidan gaba daya....
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy

3️⃣4️⃣

“Kai ma wani irin ka zama ne Aminu? Kamar ba kai ba? Har ka tsaya wani katon banza ya ci maka mutunci akan matarka ka kasa ramawa sai yanzu zaka zo nan kana wani huce haushi kana fada min? Haka yarinyar ta saka gaba wai ba zaka maida yaranka a gidanka ba kuma ka saka mata ido ya biye mata sai kace ba kai kake aurenta duk ka bi ka zama wani irin mutun”

Uffan be ce ba har Hajiya ta gama yi masa fadan, shi kansa a yanzu ya san ba kamar da ba ne, duk wani kuzari da kazarkazar irin nasa yanzu babu shi a tare da shi, tun da ya auri murja komai nasa ya sauya ga tsoronta da yake kamar mutuwarsa, abubuwa sai fada masa suke.

“To idan ba zaka iya zuwa kai wa matar taka fada ba, ni zanje da kaina nai mata fadan kuma dole na yayanka su zauna a gidanka kamin uwarsu ta dawo, dan yara ba za su zauna suna ta gararanba a gari ba ba kamar marasa gata”

Da sauri ya dago kansa jin Hajiya tace zata je tai wa Murja fada.

“A'a Hajiya zan sake mata magana zan lalaba har ta yarda”

“Har da yarda? Ka lallabata? Uwarka ce ita? To ba zan lamunta ba, ba zan dauka ba, ko tana so ko bata so dole ne yara su dawo gidan ubansu, da har zance zan rika maka su amman yanzu na fasa ko zaku mutu sai sun zauna a gidan nan”

Cikin rashin jindadin ya kalli Hajiya.

“Hajiya komai dai a bi a hankali kin san ba ko wace mace ke son rikon yaran wata ba, kuma kin ga bata haihu ba so duk wani responsibility na yara bata san shi ba”

“Idan suka zauna gidan ka daukar musu mai kula da su, yaran ma ai da wayonsu kuma ba fata muke a wani dade ba mahaifiyarsu zata dawo, duk yadda za ayi sai ta dawo duk inda zan fita na shiga sai na yi amman Halimatu sai ta dawo maka, ko dan arzikinka ya dawo”

“Shine kawai abunda nake fata yanzu ni har abunda nake ganin yafi a bar yaran a hannunta idan zata dawo sai ta dawo tare da su gaba daya, sai na kama mata wani gidan ita da yara su zauna”
Chapter 65 · 0% Book details