← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 136

Sashe 14

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Ke Zakiya iskanci ya tsaya a kanki, karki sake saka min baki a magana ke kanwar mijina ce ba yarsa ba, idan baki da tarbiya Wallahi zan gyara miki zama”

Ta nuna kanta

“Ni din? Ai kece marar tarbiya mai son hada yan'uwa bawan Allah yana can yana nema muku abunda za ku ci kina nan kina tada mishi hankali da yan'uwasa, ko da ya kira har kuka yake yace yana gurin aikin Kaduna amman kin daga masa hankali da maganar fyade”

“Karya dan uwanki yake miki, ba aiki yaje yi ba hutu ya samu ya dauki karuwarsa suka je can gurin hutu, abunda yake ne yaja akai wa Namra kuma aka rasa wanda zai mata sai dan'uwansa”

Hajiya ta nuna ni da yatsanta.

“Ke marar kunya, fitsararki ta tsaya kanki karki ce zaki min iskanci, ni danaba mazina ce bane, daman can baki da aiki sai kawo kararsa kullum cikin kawo kararsa kike baki taba gode abunda yake miki ba, ke da kike aiki ba ace miki mazinaciya ba sai shi? Tirrr Wallahi mugun abun ki ya biki, kuma Wallahi ki hada kayanki ki bar gidanan ko ke kadai ce mace a duniya ya gama aurenki, ki koma can cikin agolayen gidanku,kuma Yaya sai an kaiwa Sadi shi zai rikasu sai dai ki mutu, wannan zumuncin baki isa ki raba shi ba”

“Zan bar gidan nan Hajiya, amman idan Aminu ya damka min takardar sakina, ba zanje gidanmu na zauna da igiyar auren danki a kaina ba, kuma Wallahi ko ina za'aje sai na je sai na kwatowa yata hakkinta, ban san yayanki haka suke ba Hajiya da ban auri Aminu ba da Sadi be ganni ya ci zarafin yata ba, hakuri na ya kare indai aurena da Aminu na kare ko da kuwa hakan na nufin karshen rayuwata ne, tirr da ɗa irin na ki dan da za a cewa an yi ma yarsa fyade ya karyata ba tare da bincikar komai ba, ke kuma ki sako kafa ki zo ci mun mutunci ko? Kin zo ki shigarwa yayanki to Namra ma ƴa ce idan Aminu be san darajar ta da kimarta ba ni na sani kuma ba zan bar wannan maganar ba, kotu zata kwatar mana hakkinmu”

Tun da na fara maganar babu wanda ya sake cewa uffan ba kanensa kadai ba har Hajiya tsaye tana kallona, ni kaina na san na yi mata abunda ban taba ba, ko kusanyar magana bana iyawa da ita balle kuma har nai sa'insa da ita. A yadda nakr jin kaina a yau ko marina tai zan iya ramawa, domin ina jin babu wata sauran alaka tsakanina da dangin Aminu yanzu. Har Laweeza ta bude baki zatai magana sai Hajiya ta hana ta ta hanyar daga mata hannu sannan ta saka su gaba suka fice daga falon.
Faduwa nai zaune a gurin ina wani irin fuci kamar zakayan.

“Momy ni ce naja fada ko?”

Namra ta tambaya tana kallona tare da fashewa da kuka. Kallonta kawai nai sai na kasa cewa komai na mike tsaye tare da maganin da nake bata na nufi dakina, ina shiga na fada saman gadon a ruf da ciki, wani irin soya nake jin zuciyata na min bana jin kuma ba kuma za a kawo zancen dariya ko farinciki a tare da ni a yanzu ba, gaba daya bana jindadin komai ciki kuwa har da rayuwata. Ina yi awa daya a gurin sannan na mike tsaye na nufi bandaki amai nai bayan na gama na wanke bakina na fito ina shafa cikin da ke jikina, abunda be isa shigowa duniya ba na ke tausayawa wani abu na hade mai nauyi sannan na fito na nufo falo. Wani abun mamaki sai an samu Namra tana ta kuka har da shisshika kamar ranta zai fita, haka ne na nuna alamar ta ci kuka ta kenan sosai har ta gaji. Adnan da Aiman kuma suna zaune a guri daya kusa da ita sun rakube kasa kamar wasu marayu, Amal ce kawai ke ta sha'aninta da wayata da ke hannunta.

“Adnan kuje ku kwanta kunsan gobe akwai scul”

“To Momy”

Suka tashi a tare suka nufi dakinsu a natse kamar ba su ba, yaran da sai na yi da gaske suke zuwa su kwanta ko kuma su yi bachi a duk inda ransu ya so sai na dauke su na kai dakinsu. Kusa da Namra na zauna ya dago ta idonta har yayi ja tsababen kuka.

“Yar Kirki mi akai miki?”

Bata ce min komai ba sai na kwantar da kanta jikina ina ta shafa kanta a hankali. Amal na gani ta rugo a guje tana kuka, daman haka take bata kaunar wani ya taba min jiki ko ya kwanta a jikina sai dai ita kadai. Dagata nai na ajeta a gefena na rumgume ta sannan na karbi wayata. Ganin sako a saman wayar yasa na shiga messages box sunan Abban Namra ne a saman kamar yadda nai saving number. Wani irin fargaba da tsoron bude sakon ne ya kamani a lokacin. Saurin sauke Namra da Amal dake jikina nai na mike tsaye na nufi gaban windows falon rike da wayar ba tare da na bude sakon ba. Na hade yawu ya fi a kirga numfashi na ma har gargada yake zuciyata na raya min saki na Aminu yai. Cikin karfin hali na kai hannu na bude sakon.

_Ni Aminu Idrees na saki mata ta Halimatu Ibrahim saki daya a yau 4 ga watan 3, ya zama saki uku kenan babu gwara a tsakaninmu_

Ina gama karantawa na ji kamar ba a duniyar nan nake ba, ba dan bana bukatar sakin ba, sai dan saki abu ne mai kirma wanda ko baka kaunar mutum idan aka sake ka dole ne sai ka ji wani abun marar dadi ya ratsaka.

_Karki kara minti daya a cikin gidana! Karki yarda na dawo gobe na same ki a cikin gidana, kuma karki daukar min yara_

Shine sako na biyu bayan na farkon, ban san ta inda hawaye suka taru a idona har suka zubo min ba, sai jika screen din wayata suke.

“Zaki iya wannan Halimatu, wasu uwa da uba suka rasa balle ke da igiyar aure ce kawai kike rasa kuma auren mutumen da be san darajarki ba, akan yaranki ne right? Zaki iya yin komai akan yaranki, wannan be isa ya karya miki guiwa ba, be kamata ma hawaye ya ziyarci idonki ba saboda kin rabu da mugun mutum right?”

Ni kadai nake magana da kaina kamar wata tabbabiya da sauri na share hawayena, na nufi Namra dake kallona.

“Tashi muje gida”

Na fada ina daukar Amal, dakin su Adnan na shiga har sun fara bachi na taso su na saka Hijab dina na dauki jakata domin bana jin iya tsayawa daukar komai a yanzu, waje muka fito gaba daya na rufe kofar falon sannan na saka yarana gaba muka fita gate din.
Misalin tara da rabi muka isa unguwarmu wato family house dinmu, tun a waje na san Abdallah na cikin gidan sakamakon ganin motarsa da nai a waje, bayan an sallame mai Napep di na ji kamar ba zan iya shiga cikin gidan ba saboda Abdallah. Sai da na sauke ajiyar zuciya sannan na saka kafata a cikin gidan, babu kwalla ko kadan a tare da ni a lokacin da na shiga cikin gidan sai dai ina shiga falon nai arba da Mama da kanena biyu da kuma Abdallah sai na ji kuka ya zo min marar misaltuwa.

“Lafiya dai Halimatu”

Mama ta tambaya tana kallona da yara hankalinta a tashe.

“Mama Aminu ya sake ni.....”

Na fada ina fashewa da kuka, kanwata Salma dake kwance kan kujera ta yi saurin tashi zaune tana zaro ido, Mama kuma ta dafe kai ita da Ummi.

“Wow..... ”

Shine abunda Abdallah ya fada yana mika dukan kallonsa a gareni fuskarsa da murmushi kamar ya manta a inda yake.

________________

Saki mace mai ƴaƴa huɗu saboda son zuciya 💔😪
Anya akwai imani a zuciyar Aminu kuwa?
A matsayinki na mace ya kike auna abun nan ya kike ji a ranki?😪

Abdallah me yake yi ma murmushi? 🙄
Idan tawayensa Abdulhamid yaji ya zai yi 🤔
Anya Aminu zai barwa Halimatu yaranta kuwa?
7/20/21, 8:29 AM - Buhainat: https://chat.whatsapp.com/Kd8IIfbBTC824Lw3DOeKra

*GOBE NA...*
_My Tomorrow_

By Khadeeja Candy

9️⃣

“Wannan kaddararen aure yau Allah ya kawo karshensa, ni ban ga abun kuka ba ma balle wata damuwa”

Shine abunda ya fito daga bakin Abdallah, Mama kam kasa cewa komai tai har lokacin tana dafe da kanta nima na kasa daina hawaye zuciyata tana min wani mugun zafi.

“Ummi rikata ki shiga da ita daki mana”

Cewar Abdallah yana kallona kamar ya taso da kansa din ya rikani. Salma ta taso ta zo ta rika daga tsayen da nake muka nufin dakin Mama tana rike da ni kamar yadda Abdallah ya bukata, muna shiga dakin na zauna bakin gado sai ta zauna kusa da ni tana kallona idonta taf da hawaye.

“Ki yi hakuri Anty Halima haka Allah ya so, ki dauka wannan ma yana rubuce a cikin abunda Allah ya rubuto zai same ki”

Na gyada mata kai ina ta kokarin taushe kukan da ke cina, Amal ce ta shigo ta zauna saman kafafuwana ya lafe kamar zatai kuka sai kace wacce ta san abunda ke faruwa. Salma kuma ta tashi ta fita ta barni a dakin daga ni sai Amal a nan na samu damar yin kukana iya yadda raina yake son, ina cikin kukan Mama ta shigo ta zauna bakin gado na yi zaton zata fara tambayar abunda ya faru ne ko kum ta tausaya min ko ta karfafa min kuiwa akan abunda ya faru, amman sai na ji wani abu dabam na fitowa daga bakin.

“Ai ga irin ta nan kin kashe aure tun ba a aje ko'ina ba kin fara kuka, ina amfanin wannan abun? Kin saka kanki da yayanki a cikin matsala bayan kuma kin san saki daya ya rage ba wani gyara a tsakaninku? Halima rayuwa zatai yi? Yanzu duk maganar da muka miki muka ce ki rufe abun nan sai da kika tona shi?”
Chapter 14 · 0% Book details