Sashe 46
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan mun gama cin abincin dare ya fada min cewar na shirya gobe za mu je asibiti, be fada min dalilin zuwan ba ni kuma ban cire tsammanin wani ko wata za mu je gani ba, ashe abunda ban sani ba gurin gwaji zai kai ni gwaji zai kai ni, mamaki ya cika ni, har na kasa boye damuwata da kuka a lokacin, sai dai ban ce masa komai ba duk kuwa da kasancewar a yanzu na kara katsewa da lamarinsa. Mijina be yarda da ni ba kenan.
“Zanje office na dawo kamin a gama, saboda akwai layi sosai”
Kai kawai na iya gyada masa na bishi da kallo har na daina hangoshi. Miyasa ba zai fada min naje nai gwajin ba? Mi yasa ba zai fada inda za mu je ba tun jiya? Idan ma aka samu ina dauke da hiv ko wata cutar Abdulhamid rabuwa zai yi da mi kenan? Lallai na sake sarewa da lamarin maza!
Ina zaune a gurin ina bin layi hawaye na min zuba har aka kawo kaina, duk wanda ya gan ni a cikin wannan yanayin zai yi tunanin ko ina tsoron kar ace ina dauke da cutar ne. Bayan an dibi jinin nawa na fito na baro asibitin ba tare da tsayawa sauraren komai ba, ba fargaba nake kar ace ina dauke da cutar ba, na kasa raba dayan biyu a tsakanin neman Abdulhamid ya sake ni ko kuma na cigaba da hakurin zama da shi? Da kafa nake tafiya ina ta kallon ababen hawa da mutanen da ke kai kawo ba dan bana da kudin napep ba sai dan ina jin kamar tafiyar kasa zata sama min sassauci, ban san inda zanje ba tafiyar kawai nake duniyata na juya min. Wayata na ji tana ringing alamar kira ban tsaya komai ba na saka hannuna a jaka na fiddo wayar ba tare da na duba sunan mai kiran ba nai picking.
“Kin fito daga asibitin ne?”
Muryar mai kiran ta karantar da ni ko waye ne.
“Na fito ina bakin titi”
“Bakin titi gurin me?”
“Ban sani ba....”
Na amsa ina jin kuka kamar zai kubuce min.
“Daidai ina kike tsaye?”
Waigawa nai na duba hagu da damana sannan na soma masa kwantanci.
“Ina kusa da Exclusive City”
“Okay shiga ciki ki zauna ga ni nan zuwa”
Kai na gyada masa kamar ance yana kallona sannan sauke wayar na share hawayen da suk zubo min na nufi Exclusive City din, babba guri ne na manyan mutane yan kasaita, gurina da masoya suka fi zuwa saboda tsarinsa da kuma abubuwan kawa da aka tanadar a gurin ga abinci kala kala, haka na ke jin ana yawa fada duk da ban taba zuwa ba sai yau.
Duk sai na ji dabam abun ka da wanda be saba ba, duk kuwa da kasancewar gurin kowa be kula da kowa ba, akwai guraren zama da yawa amman sai na ji na tsawwala kamar ba zan iya zama a gurin ba.
“Akwai wanda kike jira ne?”
Daya daga cikin ma'aikatan gurin ne yai min tambayar yana sanye da rigar aikinsa.
“Aa ina son na zauna a gurin da babu mutane sosai”
“Okay ga vip 1 can ga kuma vip 2 can, za ki iya zama a daya daga ciki”
Ya fada yana nuna min vip 1 da ke kasa da kuma 2 din da ke sama, zuciyata ta fi natsuwa da 2 din ganin shi a sama yake kuma bana iya hango komai daga inda tsaye hakan na nufi na cikin ne zai iya hango na waje, tsabanin na waje da ba zai iya hango wainar da ake toya a cikin ba. Kai tsaye na nufi hanyar da zata kai ni VIP 2 din, ina shiga na samu gurin fiye da yadda nake tsammaninsa domin tsakanin wani teburin da wani a akwa doguwar tazara ga kamshi da iska mai dadi na kadawa, komai na gurin ja ne gwanin sha'awa sai wani dan sauti da ke tashi mai dadi ta taba zuciya mai kuma daidai da kowane irin yanayi.
Ko wane tebur kujera uku ce zagaye da shi amman ban da tebur daya mai kujera biyu masu fuskantar juna. Zuciyata ta fi natsuwa da shi fiye da sauran hakan yasa na nufi gurin na ja kujera daya na zauna. Wata irin natsuwa ta sauko min ba natsuwa irin ta masu kwanciyar hankali ba, natsuwa da samun damar yin kuka issasshe ta samu damar tausayawa, ta samu damar yin tunani da kuma nemawa kai mafita....!
7/21/21, 10:44 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
2️⃣5️⃣
“Abun nan fa ya wuce iya abunda kike tunani, Wallahi mutanen nan ba za du yi karya ba, kuma ga zahiri kina gani, abubuwa sai kara kwabewa suke”
Aminu ne yake wannan maganar yana shafa kansa cikin tsananin damuwa, hannunsa na dama rike da takardar transfer.
“Iko sai Allah, ni wani abun yana bani mamaki Wallahi, taya za ka biye maganar bokaye? Tun farkon fari ma mi ya kai ka gurin ya saka tsinbo? Da har za su fada maka karya da gaskiya ka yarda”
“Hajiya ai dubiya yanzu babu wanda yake zaune, ba maza ba mata ba kowa kuma yadda lamurran nan suka fara lalacewa ai dole na saka a bincika min, ba ni kadai ba ko Alfa da ya kai ni sai da abun ya daure mata kai”
“Allah kadai ya san gaskiyar wannan lamarin wata kila ma gurin malaminta ka fada, ko kuma shi alfan yana goyon bayanta ne, shiyasa suka hada kai ai maka haka”
“Babu wani zancen goyon baya Hajiya fa a zahiri kike ganin komai sai lalacewa yake”
“Kai fa baka iya tashin hankali ba, kai yanzu dan Allah Aminu har ka kawo maganar dawowa da Halimatu a gidanka? Mace da bata kaunar uwarka bata son yan'uwanka? Ka duba ja ga har kazafi tai wa Sadi fa? Wallahi har a bada ba zan taba son Halimatu ba”
“Hajiya abunda ba ki sani ba, ko wane dan'adam yana da good side of him kuma bad side, Wallahi Hajiya ba dan ina son dawowo da Halimatu ba, acire zancen arziki, Hajiya Halimatu ta fi Murja hakurin zama da ni, Halima ko bata son abu bata nuna, sannan ko fada nai mata ko na ci zarafinta sai dai tai kuka ta ba ni hakuri, and tana kokarin ganin ta gujewa bachin raina, zan iya tafiya inda nake so nai iya adadin kwanakin da nake so na dawo bata ce min komai, amman ban isa nai ma Murja haka ba Wallahi Hajiya, idan na dawo tara na dare Wallahi sai Murja ta yi min fada, amman a lokacin da Halima take nan zai iya kai wa 1 na dare a waje kuma ba zata ce min komai ba, Murja ta bi ta saka min ido akan komai nawa, ba ni d sukunin daukar waya na latsa a cikin gidana idonta na kai”
Hajiya ta saki baki.
“Ban gane idan kai dare tai maka fada ba? Uwarka ce ita? Ita ta aje ka ko kai ka aje ta da zata maka fada? Ita ba mata ba ce da ba zaka mata magana ba”
“Hajiya ba za ki gane ba ne, idan ranta ya bace, jikina har rawa yake Wallahi”
“To acan gurin malaman da kaje ba su fada maka komai akanta ba?”
“Me za su fada min? Ni yanzu ba ta nata nake ba, ta Halimatu na ke domin sun fada min matukar ban mayar da ita ba, ba zan taba ganin komai daidai ba, kuma ga alama nan kina ganin bayan rage min mukami da akai yanzu an min transfer zuwa enugu, duka duka yaushe ne rabuwar mu? Idan aka kara dadewa kila ma bara zan koma, tun da sun ce ita ke da kashin arzikin duk abunda na samu saboda ina tare da ita ne, ni da farko ma na dauka ko sammu ne kai mi shiyasa ma har na biye ta Alfa ya kai ni gurin ashe ba asiri ba ne rabuwar da mu kai ce, Hajiya ki duba fa ki ga abun hawa ma neman gagara ta yake, motata na mata gyara uku abunda ban taba ba, yanzu na siye sabuwa ita ma engine dinta ya tsaya, sabuwar mota fa Hajiya Motar miliyan biyar ace engine dinta ya tsaya”
“Wai kana nufin ba da motar ka zo ba?”
“Wallahi Alfa ne ya sauke ni bakin gate, tun jiya motar ta tsaya tana can gurin ma su gyara”
“To abun nan fa d daure kai ni na fi zargin sammu gaskiya, asiri ne akai maka, ko ita ai zata iya maka asirin na ka lalace tun da ta ga ka sake ta, ko kuma abokan aiki ko makota”
“Hajiya Malami hudu msgana daya suke, babu wanda yace asiri ne, ni dai ki taimaka min ta dawo dan Allah”
“To ai ban ga ta inda zan iya taimaka maka ba, matar nan fa ma aure tai gidan wani take”
Dafe kansa yai.
“Kai Hajiya, ko wane da idan yana cikin matsala gurin uwarsa yake zuwa ta sama masa mafita, amman ke sai kokarin kin yarda kike da ni”
“Ba yarda ne ban yi da kai ba, nawa binciken zan yi akai”
“To ki kara bincika mu ji idan za a samu results daya, ni yanzu yarana nake son na fara dawowa da su hannuna, na san ina dauko yaran nan hankali zai dawo kaina dan bata hada su da kowa ba”
“Tana son su za tai aure ta bar su?”
Cewar Hajiya tana tabe baki.
“Wannan ai na dabam ne, idan naja yaran a jikina na nuna musu su janyo uwarsu ai dole hankalinta ya dawo nan, Wallahi shegen son ya'ya ne da ita Allah kadai ya san yadda akai ma tai aure ta bar su”
“Kudi ta bi, shi wanda ta auran ba ance dan uwanta ba ne kuma mahaifinsu ya bar musu dukiya, ai kudi babu abunda basa sakawa, ni ganin na ke komai kai ba zata bar wacan mijin ta dawo maka ba”
“Zata dawo ai kin dan yadda take so na, kuma daman first love shine so ai, kuma ni na san Halima na so sosai Wallahi, zata dawo da gudu ma”
“Uhm... ”
Mikewa yai tsaye.
“Motarki na nan Hajiya?”
“Zanje office na dawo kamin a gama, saboda akwai layi sosai”
Kai kawai na iya gyada masa na bishi da kallo har na daina hangoshi. Miyasa ba zai fada min naje nai gwajin ba? Mi yasa ba zai fada inda za mu je ba tun jiya? Idan ma aka samu ina dauke da hiv ko wata cutar Abdulhamid rabuwa zai yi da mi kenan? Lallai na sake sarewa da lamarin maza!
Ina zaune a gurin ina bin layi hawaye na min zuba har aka kawo kaina, duk wanda ya gan ni a cikin wannan yanayin zai yi tunanin ko ina tsoron kar ace ina dauke da cutar ne. Bayan an dibi jinin nawa na fito na baro asibitin ba tare da tsayawa sauraren komai ba, ba fargaba nake kar ace ina dauke da cutar ba, na kasa raba dayan biyu a tsakanin neman Abdulhamid ya sake ni ko kuma na cigaba da hakurin zama da shi? Da kafa nake tafiya ina ta kallon ababen hawa da mutanen da ke kai kawo ba dan bana da kudin napep ba sai dan ina jin kamar tafiyar kasa zata sama min sassauci, ban san inda zanje ba tafiyar kawai nake duniyata na juya min. Wayata na ji tana ringing alamar kira ban tsaya komai ba na saka hannuna a jaka na fiddo wayar ba tare da na duba sunan mai kiran ba nai picking.
“Kin fito daga asibitin ne?”
Muryar mai kiran ta karantar da ni ko waye ne.
“Na fito ina bakin titi”
“Bakin titi gurin me?”
“Ban sani ba....”
Na amsa ina jin kuka kamar zai kubuce min.
“Daidai ina kike tsaye?”
Waigawa nai na duba hagu da damana sannan na soma masa kwantanci.
“Ina kusa da Exclusive City”
“Okay shiga ciki ki zauna ga ni nan zuwa”
Kai na gyada masa kamar ance yana kallona sannan sauke wayar na share hawayen da suk zubo min na nufi Exclusive City din, babba guri ne na manyan mutane yan kasaita, gurina da masoya suka fi zuwa saboda tsarinsa da kuma abubuwan kawa da aka tanadar a gurin ga abinci kala kala, haka na ke jin ana yawa fada duk da ban taba zuwa ba sai yau.
Duk sai na ji dabam abun ka da wanda be saba ba, duk kuwa da kasancewar gurin kowa be kula da kowa ba, akwai guraren zama da yawa amman sai na ji na tsawwala kamar ba zan iya zama a gurin ba.
“Akwai wanda kike jira ne?”
Daya daga cikin ma'aikatan gurin ne yai min tambayar yana sanye da rigar aikinsa.
“Aa ina son na zauna a gurin da babu mutane sosai”
“Okay ga vip 1 can ga kuma vip 2 can, za ki iya zama a daya daga ciki”
Ya fada yana nuna min vip 1 da ke kasa da kuma 2 din da ke sama, zuciyata ta fi natsuwa da 2 din ganin shi a sama yake kuma bana iya hango komai daga inda tsaye hakan na nufi na cikin ne zai iya hango na waje, tsabanin na waje da ba zai iya hango wainar da ake toya a cikin ba. Kai tsaye na nufi hanyar da zata kai ni VIP 2 din, ina shiga na samu gurin fiye da yadda nake tsammaninsa domin tsakanin wani teburin da wani a akwa doguwar tazara ga kamshi da iska mai dadi na kadawa, komai na gurin ja ne gwanin sha'awa sai wani dan sauti da ke tashi mai dadi ta taba zuciya mai kuma daidai da kowane irin yanayi.
Ko wane tebur kujera uku ce zagaye da shi amman ban da tebur daya mai kujera biyu masu fuskantar juna. Zuciyata ta fi natsuwa da shi fiye da sauran hakan yasa na nufi gurin na ja kujera daya na zauna. Wata irin natsuwa ta sauko min ba natsuwa irin ta masu kwanciyar hankali ba, natsuwa da samun damar yin kuka issasshe ta samu damar tausayawa, ta samu damar yin tunani da kuma nemawa kai mafita....!
7/21/21, 10:44 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
2️⃣5️⃣
“Abun nan fa ya wuce iya abunda kike tunani, Wallahi mutanen nan ba za du yi karya ba, kuma ga zahiri kina gani, abubuwa sai kara kwabewa suke”
Aminu ne yake wannan maganar yana shafa kansa cikin tsananin damuwa, hannunsa na dama rike da takardar transfer.
“Iko sai Allah, ni wani abun yana bani mamaki Wallahi, taya za ka biye maganar bokaye? Tun farkon fari ma mi ya kai ka gurin ya saka tsinbo? Da har za su fada maka karya da gaskiya ka yarda”
“Hajiya ai dubiya yanzu babu wanda yake zaune, ba maza ba mata ba kowa kuma yadda lamurran nan suka fara lalacewa ai dole na saka a bincika min, ba ni kadai ba ko Alfa da ya kai ni sai da abun ya daure mata kai”
“Allah kadai ya san gaskiyar wannan lamarin wata kila ma gurin malaminta ka fada, ko kuma shi alfan yana goyon bayanta ne, shiyasa suka hada kai ai maka haka”
“Babu wani zancen goyon baya Hajiya fa a zahiri kike ganin komai sai lalacewa yake”
“Kai fa baka iya tashin hankali ba, kai yanzu dan Allah Aminu har ka kawo maganar dawowa da Halimatu a gidanka? Mace da bata kaunar uwarka bata son yan'uwanka? Ka duba ja ga har kazafi tai wa Sadi fa? Wallahi har a bada ba zan taba son Halimatu ba”
“Hajiya abunda ba ki sani ba, ko wane dan'adam yana da good side of him kuma bad side, Wallahi Hajiya ba dan ina son dawowo da Halimatu ba, acire zancen arziki, Hajiya Halimatu ta fi Murja hakurin zama da ni, Halima ko bata son abu bata nuna, sannan ko fada nai mata ko na ci zarafinta sai dai tai kuka ta ba ni hakuri, and tana kokarin ganin ta gujewa bachin raina, zan iya tafiya inda nake so nai iya adadin kwanakin da nake so na dawo bata ce min komai, amman ban isa nai ma Murja haka ba Wallahi Hajiya, idan na dawo tara na dare Wallahi sai Murja ta yi min fada, amman a lokacin da Halima take nan zai iya kai wa 1 na dare a waje kuma ba zata ce min komai ba, Murja ta bi ta saka min ido akan komai nawa, ba ni d sukunin daukar waya na latsa a cikin gidana idonta na kai”
Hajiya ta saki baki.
“Ban gane idan kai dare tai maka fada ba? Uwarka ce ita? Ita ta aje ka ko kai ka aje ta da zata maka fada? Ita ba mata ba ce da ba zaka mata magana ba”
“Hajiya ba za ki gane ba ne, idan ranta ya bace, jikina har rawa yake Wallahi”
“To acan gurin malaman da kaje ba su fada maka komai akanta ba?”
“Me za su fada min? Ni yanzu ba ta nata nake ba, ta Halimatu na ke domin sun fada min matukar ban mayar da ita ba, ba zan taba ganin komai daidai ba, kuma ga alama nan kina ganin bayan rage min mukami da akai yanzu an min transfer zuwa enugu, duka duka yaushe ne rabuwar mu? Idan aka kara dadewa kila ma bara zan koma, tun da sun ce ita ke da kashin arzikin duk abunda na samu saboda ina tare da ita ne, ni da farko ma na dauka ko sammu ne kai mi shiyasa ma har na biye ta Alfa ya kai ni gurin ashe ba asiri ba ne rabuwar da mu kai ce, Hajiya ki duba fa ki ga abun hawa ma neman gagara ta yake, motata na mata gyara uku abunda ban taba ba, yanzu na siye sabuwa ita ma engine dinta ya tsaya, sabuwar mota fa Hajiya Motar miliyan biyar ace engine dinta ya tsaya”
“Wai kana nufin ba da motar ka zo ba?”
“Wallahi Alfa ne ya sauke ni bakin gate, tun jiya motar ta tsaya tana can gurin ma su gyara”
“To abun nan fa d daure kai ni na fi zargin sammu gaskiya, asiri ne akai maka, ko ita ai zata iya maka asirin na ka lalace tun da ta ga ka sake ta, ko kuma abokan aiki ko makota”
“Hajiya Malami hudu msgana daya suke, babu wanda yace asiri ne, ni dai ki taimaka min ta dawo dan Allah”
“To ai ban ga ta inda zan iya taimaka maka ba, matar nan fa ma aure tai gidan wani take”
Dafe kansa yai.
“Kai Hajiya, ko wane da idan yana cikin matsala gurin uwarsa yake zuwa ta sama masa mafita, amman ke sai kokarin kin yarda kike da ni”
“Ba yarda ne ban yi da kai ba, nawa binciken zan yi akai”
“To ki kara bincika mu ji idan za a samu results daya, ni yanzu yarana nake son na fara dawowa da su hannuna, na san ina dauko yaran nan hankali zai dawo kaina dan bata hada su da kowa ba”
“Tana son su za tai aure ta bar su?”
Cewar Hajiya tana tabe baki.
“Wannan ai na dabam ne, idan naja yaran a jikina na nuna musu su janyo uwarsu ai dole hankalinta ya dawo nan, Wallahi shegen son ya'ya ne da ita Allah kadai ya san yadda akai ma tai aure ta bar su”
“Kudi ta bi, shi wanda ta auran ba ance dan uwanta ba ne kuma mahaifinsu ya bar musu dukiya, ai kudi babu abunda basa sakawa, ni ganin na ke komai kai ba zata bar wacan mijin ta dawo maka ba”
“Zata dawo ai kin dan yadda take so na, kuma daman first love shine so ai, kuma ni na san Halima na so sosai Wallahi, zata dawo da gudu ma”
“Uhm... ”
Mikewa yai tsaye.
“Motarki na nan Hajiya?”