Sashe 27
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*** *** ***
A satin suka fara zuwa makaranta, daga uniform har Littafai da school bus da ke zuwa daukarsu da komai Abdallah yai, aikina kawai wanke musu uniform shi ma ba kullum ba domi kanena ne suke wankewa su goge musu, bangaren abinci na samu sauki sosai domin a makarantar ake ba su na safe da kuma na karfe sha biyu daya da rabi kuma a kawo su gida. Tun daga lokacin ban sake saka Abdallah a ido ba da na kira wayarsa nai masa godiya ma kin dauka yai.
Wata rana muna cikin fira da Abdulhamid na ke masa zancen yarana akan tafiyar da zan yi na bar su a gidan.
“Amman za su rika zuwa suna ganina a gidanka”
Na fada ina karantar yanayinsa.
“Haka ne”
Ya fada yana hade yawu, ni kuma na ji wani iri, be karfafa min guiwa ba kuma ba ce zai hana su zuwa ba, a ranar har muka karkare ba mu tattauna wani abun arziki ba. Misalin goma na dare na shigo gida, dakinmu na wuce kai tsaye sai na samu dukansu sun kwanta a saman katifa sun yi bachi har Amal da bata bachi da wuri. Ido na kura musu ina ta kallonsu kamin na zauna na kai hannuna na safa su, ina ta jin su kamar wasu marayu zan auri wanda baya farinciki da zuwansu a gidansa ga mahaifinsu har yau be leko ko ya turo a duba lafiyarsu ba, gaba daya ma sai na ji kamar na fasa auren kuma babu dama. Shinfida nai musu na kwantar da su a inda nasaba kwantar da su Amal kuma na rumgumeta mu kai bachi rumgume da juna. Tun daga lokacin wata irin shakuwa da kauna ta kara shiga tsakanina da yayana ba ma kamar Amal da take karama, har ta kai ko laifinsu bana son a gani dana ji kukan daya daga cikinsu sai na ji babu dadi. Ban sanarda kowa zancen auren ba sai ana sauran sati biyu ciki kuwa har da aminiyata Hajara, a ranar da ta sallamo gidanmu ta nuna min bachin ranta sosai har take labarta min wai mijinta ya fara gina gida mai part biyu saboda ni da ita.
“Hajara ba ki da hankali”
“Babu wani rashin hankali Halimatu, abokiyar zama tana da dadi ko da dan yau da gobe, kuma ko Abban Afra be aure ki ba zai karo aure saboda akwai son karin auren a ransa, ba ki san kudirinmu ba, ba ki san iya abunda muka shirya akanki ba”
“Wai ba ki ma kishin mijinki?”
“Wallahi ban taba jin kishi akan ki auren mijina ba, na san waye mijina za sama miki rayuwa mai kyau irin wacce kika rasa a gidan Aminu, kuma zai rike yaran nan da muhimmanci ko ba komai ai hakan zai bawa Aminu haushi tunda abokinsa ne”
“Wallahi ni ba zan iya ba Hajara, taya zan yi kishi da yar'uwata?”
“Ba zaman kishi za mu yi ba, zaman yan'uwa za mu yi”
Duk yadda tai ta kokarin convince dina na yarda da ita sai na kasa, ni kallon marar tunani ma na koma yi mata, a ranar dai mun sha fira sai da yamma ta tafi. Washe gari sai ga kawata Sa'adatu na yi mamakin ganinta ba ni kadai ba har da kanwata Hafiza domin ni dai na san ban fada mata cewar zan yi aure ba, rabona da ita ma tun a lokacin da ta fada min cewar za tai tafiya tafiyar da Hafiza ke labarta min cewar da Aminu tai yi ta. A al'adar ko ma na kira shi da dabi'a bana iya cin fuskarka mutum a kusa da shi kamar yadda na ke saurin yarda da mutane, komai mutum yai min zan shanye na mai da komai ba komai ba. Haka muka zauna muka sha fira da ita daman a gidan babu wanda ya san akwai wata alaka tsakaninta da Aminu daga ni sai Hafiza, hakan yasa Inna da Mama suka sakar mata fuska kamar yadda suka basa tun ina budurwa.
Sosai ta nuna min rashin jindadin mutuwar aurena da Aminu da kuma tambayar wai da su Namra zanje gidan sabon mijin nawa ko a'a.
“Ya ce na je da su, ni kuma na ga kara dai na bar su a gida tun da sun fara sabawa da nan din”
“Eh kuma kin yi tunani, tun da na ji ance saurayi ne wanda za ki aura”
Na kalleta da mamaki.
“A ina kika ji?”
“Hmmm Halimatu kenan, ai abun duniya baya boyuwa ballantana ma kin san wannan babban sakamako ne Allah yai miki Allah yasa dai kyakkyawa ne kamar yadda kike kyakkyawa kin san ke fa matar manya ce”
Murmushi nai tare da canja mata fuska, hakan yasa ta hade duk wani zancen da ke kunce a bakinta tai min sallama ta wuce har da mikawa su Amal 2k ni dai ko rakiya ban mata ba.
Duk yadda kawaye da yan'uwa suke ba ni kayan gyara da tsima jiki kin sha nai sanin mijin da zan aura, dan haka ba zan sha abun da zai zo ya dame ni ba ko ya zame min matsala. Sai dai bana nunawa kowa sanin cewar babu wanda yasan da matsalar Abdulhamid sai ni. Daga ni har shi ba mu tsara yin wani event ba, dama ni ba budurwa ce shi ne dai ya kamata yai hakn kuma be yi ba, wata kila saboda shi ma din kansa ya san be cika cikakakken ango ba ko kuma dan baya da son hayaniya ne oho.
Ranar da aka daura aurena da Abdulhamid sai na kasa farinciki kamar wacce akai ma auren dole, wata kila saboda na san irin mijin da na aura ko saboda zan tafi na bar yayana ko kuwa saboda dan'uwan Abdallah na aura wanda ya saka ce min komai akan hakan har yanzu. Duk wata murna ta iya fuska ce da hakora amman bata kai zuci ba, gaba daya ma neman son Abdulhamid nai da ke zuciyata na rasa, da na tuna cewar baya son yarana sai ji kamar bana bukatar zama shi, duk kuwa da kasancewar be fito kai tsaye ya fada min ba amman alamu ya nuna haka. A wunin ranar da akai wunin biki Amal na biye da ni duk inda zanje, ba Amal kadai ba har da Namra Aiman da Adnan ne kawai ke ta sha'aninsu su kan fito basu kula ba, Amal har wani sabon kuka ta tsira ba tare da am mata komai ba. Tun da magariba kanena Zayyanu ya karbe ta ya fita da ita da Namra saboda ya dauke musu hankali kar su ga tafiyata.
Inna da Mama sun min huduba kamar yadda su kai min a farkon daren da za a kai ni gidan Aminu, sai abun ya dawo min sabo ina ta hawaye kamar bakuwar aure. Baba ma ya min tasa bayan wacce yake ywan min tun daga lokacin da aka saka ranar auren. Ban san abunda ya hana jin bana son tarewa a ranar ba sai naji kamar ace sai nan da kwana biyu zan tare. Motoci da Abdulhamid ya turo na daukar amarya motoci ne amsu kyau da tsada, ba mota daya ko biyu aka kawo ba, motoci da yawa aka kawo na daukar amarya da kawayenta ni kaina abun har mamaki ya ba ni sai ka ce wata budurwa, ko da yake a gurinsa auren fari ne dole abokai da yan'uwa su yi masa kara.
“Hafiza ga yayanki dan Allah ki kula min da su, na san kowa yana kula da su yadda ya dace amman zan kara tunatar da ke ne saboda na san halin yara da cin rai, ta bangaren makarantar su a kula min da su dan Allah”
Haka na fadawa Hafiza kanwata wacce muka fi shakuwa, ina jin wani abu ba dadi kamar ina bar mata wasiya. Dafa ni tai tana karfafa min kuiwa.
“Karki damu Yaya Halimatu za'a kula da su In-Sha-Allah, Allah dai ya baku zama lafiya da hakuri, idan kika cire komai a ranki sai ki ga kin saba kamar can baya”
“Na gode Hafiza”
Misalin tara da yan mintuna aka kai ni gidan Abdulhamid da ke can bayan science, har muka isa kafata ta taka cikin katon gidan mai kyau ban daina jin kewar yayana a raina ba, ba ma kamar Amal sarkin takuwa yau ko a jikin wa zata kwana oho...
AMINU POV.........✍️
___________________________
To fa Halimatu za a fara sabuwar rayuwa, Allah bada zaman lafiya.
Anya dai ta kyautawa Abdallah kuwa? 🙄😏
7/20/21, 8:30 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
1️⃣6️⃣
Milk shadda ce a jikinsa sai farar hula, fuskarsa na ta sheki kamar shi ne angon ga wani kamshin tutare da yake mai sanarda zuwansa tun kamin ya iso. Abu biyu ne babu a tare da shi walwala da sai kuma yar ramar da yai kadan. Da sallama ya shigo falon Hajiyarsa sannan ya zauna da bismillah, kamin ya mika mata gaisuwa daga inda yake zaune. Sai ta amsa masa tana ta kallon yanayinsa yanayin da ya sauya masa tun sati biyu da suka gabata.
“Hajiya ta sai yanzu ake karyawa?”
Ya fada yana kallon kofin tea da ke hannunta.
“Aa yau da dumamen tuwo na karya sai yanzu na ke shan tea”
Be sake cewa komai ba ya maida hankalinsa a gurin tv da ke kunne.
“Ba kaje aiki ba yau ko kuma ba a aikin ne yau?”
“Zan je yanzu, Suwaiba na kai gidan Abdulhamid, daman ta matsa min tun kwanaki baya tana son zuwa na hana ta sai yau dai na kai ta”
Har lokacin da yake maganar be kalli gefenta ba. Yana shirin mikewa tsaye ta ce.
“Jiya Mal Dalhatu ya zo nan”
Da sauri Abdallah ya juyo ya kalleta jin ta ambaci mahaifin Halimatu.
“Mi ya kawo shi?”
“Yace yana ta son ya zo yai mana godiya be samu dama sai yau saboda yanayin jikinsa”
Dan murmushi yai ya kawardar fuskarsa.
“Baba Karami akwai karfin hali, miye abun godiya a ciki ai yi wa kai ne”
“Yi wa kai ko kashe kai? Akan me za ka dauki nauyin irin wannan dawainiyar haka? Ya fada ko ruwan da aka sha a gurin wunin nan kai ka kawo su”
A satin suka fara zuwa makaranta, daga uniform har Littafai da school bus da ke zuwa daukarsu da komai Abdallah yai, aikina kawai wanke musu uniform shi ma ba kullum ba domi kanena ne suke wankewa su goge musu, bangaren abinci na samu sauki sosai domin a makarantar ake ba su na safe da kuma na karfe sha biyu daya da rabi kuma a kawo su gida. Tun daga lokacin ban sake saka Abdallah a ido ba da na kira wayarsa nai masa godiya ma kin dauka yai.
Wata rana muna cikin fira da Abdulhamid na ke masa zancen yarana akan tafiyar da zan yi na bar su a gidan.
“Amman za su rika zuwa suna ganina a gidanka”
Na fada ina karantar yanayinsa.
“Haka ne”
Ya fada yana hade yawu, ni kuma na ji wani iri, be karfafa min guiwa ba kuma ba ce zai hana su zuwa ba, a ranar har muka karkare ba mu tattauna wani abun arziki ba. Misalin goma na dare na shigo gida, dakinmu na wuce kai tsaye sai na samu dukansu sun kwanta a saman katifa sun yi bachi har Amal da bata bachi da wuri. Ido na kura musu ina ta kallonsu kamin na zauna na kai hannuna na safa su, ina ta jin su kamar wasu marayu zan auri wanda baya farinciki da zuwansu a gidansa ga mahaifinsu har yau be leko ko ya turo a duba lafiyarsu ba, gaba daya ma sai na ji kamar na fasa auren kuma babu dama. Shinfida nai musu na kwantar da su a inda nasaba kwantar da su Amal kuma na rumgumeta mu kai bachi rumgume da juna. Tun daga lokacin wata irin shakuwa da kauna ta kara shiga tsakanina da yayana ba ma kamar Amal da take karama, har ta kai ko laifinsu bana son a gani dana ji kukan daya daga cikinsu sai na ji babu dadi. Ban sanarda kowa zancen auren ba sai ana sauran sati biyu ciki kuwa har da aminiyata Hajara, a ranar da ta sallamo gidanmu ta nuna min bachin ranta sosai har take labarta min wai mijinta ya fara gina gida mai part biyu saboda ni da ita.
“Hajara ba ki da hankali”
“Babu wani rashin hankali Halimatu, abokiyar zama tana da dadi ko da dan yau da gobe, kuma ko Abban Afra be aure ki ba zai karo aure saboda akwai son karin auren a ransa, ba ki san kudirinmu ba, ba ki san iya abunda muka shirya akanki ba”
“Wai ba ki ma kishin mijinki?”
“Wallahi ban taba jin kishi akan ki auren mijina ba, na san waye mijina za sama miki rayuwa mai kyau irin wacce kika rasa a gidan Aminu, kuma zai rike yaran nan da muhimmanci ko ba komai ai hakan zai bawa Aminu haushi tunda abokinsa ne”
“Wallahi ni ba zan iya ba Hajara, taya zan yi kishi da yar'uwata?”
“Ba zaman kishi za mu yi ba, zaman yan'uwa za mu yi”
Duk yadda tai ta kokarin convince dina na yarda da ita sai na kasa, ni kallon marar tunani ma na koma yi mata, a ranar dai mun sha fira sai da yamma ta tafi. Washe gari sai ga kawata Sa'adatu na yi mamakin ganinta ba ni kadai ba har da kanwata Hafiza domin ni dai na san ban fada mata cewar zan yi aure ba, rabona da ita ma tun a lokacin da ta fada min cewar za tai tafiya tafiyar da Hafiza ke labarta min cewar da Aminu tai yi ta. A al'adar ko ma na kira shi da dabi'a bana iya cin fuskarka mutum a kusa da shi kamar yadda na ke saurin yarda da mutane, komai mutum yai min zan shanye na mai da komai ba komai ba. Haka muka zauna muka sha fira da ita daman a gidan babu wanda ya san akwai wata alaka tsakaninta da Aminu daga ni sai Hafiza, hakan yasa Inna da Mama suka sakar mata fuska kamar yadda suka basa tun ina budurwa.
Sosai ta nuna min rashin jindadin mutuwar aurena da Aminu da kuma tambayar wai da su Namra zanje gidan sabon mijin nawa ko a'a.
“Ya ce na je da su, ni kuma na ga kara dai na bar su a gida tun da sun fara sabawa da nan din”
“Eh kuma kin yi tunani, tun da na ji ance saurayi ne wanda za ki aura”
Na kalleta da mamaki.
“A ina kika ji?”
“Hmmm Halimatu kenan, ai abun duniya baya boyuwa ballantana ma kin san wannan babban sakamako ne Allah yai miki Allah yasa dai kyakkyawa ne kamar yadda kike kyakkyawa kin san ke fa matar manya ce”
Murmushi nai tare da canja mata fuska, hakan yasa ta hade duk wani zancen da ke kunce a bakinta tai min sallama ta wuce har da mikawa su Amal 2k ni dai ko rakiya ban mata ba.
Duk yadda kawaye da yan'uwa suke ba ni kayan gyara da tsima jiki kin sha nai sanin mijin da zan aura, dan haka ba zan sha abun da zai zo ya dame ni ba ko ya zame min matsala. Sai dai bana nunawa kowa sanin cewar babu wanda yasan da matsalar Abdulhamid sai ni. Daga ni har shi ba mu tsara yin wani event ba, dama ni ba budurwa ce shi ne dai ya kamata yai hakn kuma be yi ba, wata kila saboda shi ma din kansa ya san be cika cikakakken ango ba ko kuma dan baya da son hayaniya ne oho.
Ranar da aka daura aurena da Abdulhamid sai na kasa farinciki kamar wacce akai ma auren dole, wata kila saboda na san irin mijin da na aura ko saboda zan tafi na bar yayana ko kuwa saboda dan'uwan Abdallah na aura wanda ya saka ce min komai akan hakan har yanzu. Duk wata murna ta iya fuska ce da hakora amman bata kai zuci ba, gaba daya ma neman son Abdulhamid nai da ke zuciyata na rasa, da na tuna cewar baya son yarana sai ji kamar bana bukatar zama shi, duk kuwa da kasancewar be fito kai tsaye ya fada min ba amman alamu ya nuna haka. A wunin ranar da akai wunin biki Amal na biye da ni duk inda zanje, ba Amal kadai ba har da Namra Aiman da Adnan ne kawai ke ta sha'aninsu su kan fito basu kula ba, Amal har wani sabon kuka ta tsira ba tare da am mata komai ba. Tun da magariba kanena Zayyanu ya karbe ta ya fita da ita da Namra saboda ya dauke musu hankali kar su ga tafiyata.
Inna da Mama sun min huduba kamar yadda su kai min a farkon daren da za a kai ni gidan Aminu, sai abun ya dawo min sabo ina ta hawaye kamar bakuwar aure. Baba ma ya min tasa bayan wacce yake ywan min tun daga lokacin da aka saka ranar auren. Ban san abunda ya hana jin bana son tarewa a ranar ba sai naji kamar ace sai nan da kwana biyu zan tare. Motoci da Abdulhamid ya turo na daukar amarya motoci ne amsu kyau da tsada, ba mota daya ko biyu aka kawo ba, motoci da yawa aka kawo na daukar amarya da kawayenta ni kaina abun har mamaki ya ba ni sai ka ce wata budurwa, ko da yake a gurinsa auren fari ne dole abokai da yan'uwa su yi masa kara.
“Hafiza ga yayanki dan Allah ki kula min da su, na san kowa yana kula da su yadda ya dace amman zan kara tunatar da ke ne saboda na san halin yara da cin rai, ta bangaren makarantar su a kula min da su dan Allah”
Haka na fadawa Hafiza kanwata wacce muka fi shakuwa, ina jin wani abu ba dadi kamar ina bar mata wasiya. Dafa ni tai tana karfafa min kuiwa.
“Karki damu Yaya Halimatu za'a kula da su In-Sha-Allah, Allah dai ya baku zama lafiya da hakuri, idan kika cire komai a ranki sai ki ga kin saba kamar can baya”
“Na gode Hafiza”
Misalin tara da yan mintuna aka kai ni gidan Abdulhamid da ke can bayan science, har muka isa kafata ta taka cikin katon gidan mai kyau ban daina jin kewar yayana a raina ba, ba ma kamar Amal sarkin takuwa yau ko a jikin wa zata kwana oho...
AMINU POV.........✍️
___________________________
To fa Halimatu za a fara sabuwar rayuwa, Allah bada zaman lafiya.
Anya dai ta kyautawa Abdallah kuwa? 🙄😏
7/20/21, 8:30 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
1️⃣6️⃣
Milk shadda ce a jikinsa sai farar hula, fuskarsa na ta sheki kamar shi ne angon ga wani kamshin tutare da yake mai sanarda zuwansa tun kamin ya iso. Abu biyu ne babu a tare da shi walwala da sai kuma yar ramar da yai kadan. Da sallama ya shigo falon Hajiyarsa sannan ya zauna da bismillah, kamin ya mika mata gaisuwa daga inda yake zaune. Sai ta amsa masa tana ta kallon yanayinsa yanayin da ya sauya masa tun sati biyu da suka gabata.
“Hajiya ta sai yanzu ake karyawa?”
Ya fada yana kallon kofin tea da ke hannunta.
“Aa yau da dumamen tuwo na karya sai yanzu na ke shan tea”
Be sake cewa komai ba ya maida hankalinsa a gurin tv da ke kunne.
“Ba kaje aiki ba yau ko kuma ba a aikin ne yau?”
“Zan je yanzu, Suwaiba na kai gidan Abdulhamid, daman ta matsa min tun kwanaki baya tana son zuwa na hana ta sai yau dai na kai ta”
Har lokacin da yake maganar be kalli gefenta ba. Yana shirin mikewa tsaye ta ce.
“Jiya Mal Dalhatu ya zo nan”
Da sauri Abdallah ya juyo ya kalleta jin ta ambaci mahaifin Halimatu.
“Mi ya kawo shi?”
“Yace yana ta son ya zo yai mana godiya be samu dama sai yau saboda yanayin jikinsa”
Dan murmushi yai ya kawardar fuskarsa.
“Baba Karami akwai karfin hali, miye abun godiya a ciki ai yi wa kai ne”
“Yi wa kai ko kashe kai? Akan me za ka dauki nauyin irin wannan dawainiyar haka? Ya fada ko ruwan da aka sha a gurin wunin nan kai ka kawo su”