← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 85 OF 136

Sashe 85

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“and... Dan fashin da yake bibiyarki zai iya cutar da rayuwarki ki san da wannan, ni ko ba zan iya ba ki kariya ba na san jami'an tsaro za su ba ki, kuma In-Sha-Allah zan tsaya miki har ki samu salama, ba bayyana ki zan yi ba, ba nunawa kowa fuskarki zan yi ba balle har na fadi sunanki, taimakonki zan yi, and i promise you a cikin albashi na na wannan watan kina da 20,000 dan Allah ki same ni ko a ina ina son ganinki, ko wace irin uwa ce ke ina son ganinki dan Allah....”

Cikin kuka Ummulkhar take fadin hakan hannunta rike da loudspeaker dayan kuma rike da takardar yayinda idanuwanta suke zubar da hawaye.
Babu wanda zuciyarsa ta raya masa sai matar nan, sosai ya maida hankali yana kallon gurin da take zaune tare da yaranta, the way ta take sharar hawaye ya kara karafafa zatonsa a kanta, labarin yarsa ya shigo ciki duk kuwa da bata fadi sunansa ba ko sunan yarsa sai dai ta fadi cewar mahaifin yarta ya zargeta da kisan yarsa saboda kaddarar mutuwarta ya fada mata, kamar yadda kadarar gushewar hankalin abokin aikinta ya fada a kanta, an keta mata haddi an ketawa yarta, mijinta ya ci zarafinta, a kokarin kwatar hakkin yarta mijinta ya saketa, ga labarin samun aikin kamfanin da tai ya shigo ciki sai dai shi ma bata fadi sunan kamfanin ba.....

Wani irin kallonta yake, har ya ji kamar gilashin dake idon sa ya tare ganinsa sai ta ya cireshi yana cigaba da kallonta, ita kuma ta soke kai kasa yana ta latsa waya tana sharar kwalla, wa akai wa fyade? Wacen karamar ko babbar? No wait mutunen da take bawa abincin a kusa da kamfaninsu abokin aikinta ne? Is that why take kokarin kula da shi? Waye mijin na ta? Waya ke bibiyarta?
A lokaci daya ya jerowa kansa wadannan tambayoyin, da bashi da amsar su, and he can't take his eyes on her kamar his life defend on her, tun bata lura da kallon da yake mata ba har ta lura ta soma rasa natsuwarta, sai a sannan ya saka gilashin idonsa ya cigaba da kallonta ta yadda ba zata fahimta ba, zuciyarsa cike take da tambayoyin da ita kadai zata iya amsa mashi su, ita kadai duk wannan abun akanta? Be tana jin labarin da ya shiga zuciyarsa ta tsuma zuciyarsa ba irin na yau, bw tana jin labari mai tausayi da tashin hankali ba irin yau, kuma a haka she's still alive tana ta farincikinta ita da yaranta, har akai abunda za ayi a gurin aka tashi be kawarda hankalinsa daga kanta ba.....

______________________________

Yau na yi 5,176k words na biya bashi 🙌😍

#Team Aminu
#Team Abdallah
#Team Ahmad
#GN
#KhadeejaCandy
7/21/21, 10:46 PM - Buhainat: I think you'd like this story: "GOBE NA (My Tomorrow)" by KhadeejaCandy on Wattpad https://www.wattpad.com/story/247701926?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=story_info&wp_page=story_details_button&wp_uname=KhadeejaCandy&wp_originator=ZkyWKvWuHXhIRzZDEluZ%2BuUXayIbDBikXAQA%2BM4xeAsJY%2Fh9rtovTCoQphCdFYUPM4K1nHTquOLcFfifZUhwZ0RRyERddTi4AY1OYORg8gUhN9fNU%2FLr6t3SMGO9O8M2

*GOBE NA...*

By Khadeeja Candy

4️⃣3️⃣

ABDALLAH POV.

He's walking slowly tun daga inda ya aje motarsa har zuwa cikin falon Hajiya, gidan sai kamshin sabon fenti da aka yi jiya yake. A gajiye ya shigo falon sai ya tarar babu kowa sai sanyin ac. Zaunawa yai a saman sabin kujeru da Hajiya ta sake ya ciro wayarsa yana latsawa, ya kusan minti talatin a haka sannan Hajiya ta fito rike da wuka da katon mangoro a plate.

“Husani kai ne ka shigo”

Ya dago a hankali ya kalleta.

“Eh Hajiya barka da yamma”

“Yauwa sannu dai, ya aikin? Yau baka shigo da safe ba”

“Na fita aikin ne da wuri saboda tiyati za ayi, shiyasa”

“Okay abincin fa akawo?”

“A a gida zanje yanzu”

Daga haka bata sake ce masa komai ba, shi ma kuma be ce mata ba, daman kusan kullum idan ya shigo gidan shiru yake ko wata maganar ake sai daiya bisu da ido.

“Ana ta shirye shiryen biki har yanzu baka ce komai ba”

“Allah ya sanya alheri”

Ya fada a takaice, sai kuma yai shiru kamin ya sake kallonta.

“Hajiya na yi wani laifi”

A take ta dago kai ta kalleshi da sauri.

“Mi kai?”

“Kin min tsakani da Halima, tun daga lokacin ban sake kula ta ba, sai kwana goma sa suka wuce, na ganta a hanya tana tafiya da tufafin da be dace ba, hakan yasa na tsaya na dauke a motata saboda kare mutuncinta, ki yafe min dan Allah”

“In ban da kai da abun ka, miye amfanin kare mutuncin macen da bata san mutuncin kanta ba, da wata ce ai ba zata yi shigar banza ta fita ba, talla take yi kenan Allah ya kyauta”

Yawu ya hade da karfi da ba Hajiya ba ce da be lamuncin jin wani kalami marar dadi daga bakin kowa ba akan Halimatu idan ba zai iya cewa komai ba to ba zai saurara ba.

“Wato dai na gane ba zaka iya fita daga tsafgar yarinyar nan ba, saboda ka samu salama kuma ku samu fahimta da dan'uwanka yasa na yi muku tsakani amman hakan be wadatar ba, tun da ga shi nan har yanzu ba ku jutuwa da juna, kuma ka kasa daina kulata, har yanzu dai tana nan cikin ranka, yarinyar da ta haifarda rashin jituwa tsakaninku? Yanzu shirye shiyen auren dan'uwanka ake amman babu ruwanka komai sai dai ka bishi da ido haka ake? Ku uku kawai Allah ya bani idan ba ku hada kai ba ya kuke son zama?”

“Ba daga ni ba ne Hajiya, Abdulhamid yana ta ganin laifina ne har yanzu, ko magana nai masa sai idan yaga dama zai amsa ni”

“To ai dole ya rika maka haka, taya zaka rika bibiyar matar da ya saka? Wacce ta zama makiyiyarmu? Ta ruguza rayuwarku?”

Kallon mahaifiyar tasa yai ya dauke kai, wani lokacin idan tana yin abu kamar wacce bata taba karatu ba, ne san abunda yasa son zuciya yake rinjiyarta ba. Be ce sake ce mata uffan ba har tai fadan ta gama, sannan yai mata sallama ya fice zuwa gidansa. Da dan kuzarinsa ya shiga gidan yaransa na harabar gidan suna wasa kasancewar yau Thursday after school babu islamiya a yau. Da gudu suka zo suka masa oyoyo ya daga su sama yana dariya ya sauke sannan ya rika hannunsu suka shiga cikin falon, a falon ya sake musu hannu ya nufi kitchen gurin da yake jiyo motsin Suwaiba. Daga baya ya rumgumeta yana sumbatar gefen kumatunta.

“Madam me kike girka mana”

“Me nake girkawa dai ni da yarana kai da bazawarar ka ta dauke maka nauyin cin abincin gidana”

Ta fada tana yatsina fuska. Sai yai murmushi rabon da Halima ta aiko masa da abinci tun ranar da ya dauko ta a mota, ya juyo da ita tare da saita idanuwansa cikin nata.

“Kin ga abunda ke hada ni da ke mita, da rashin yarda, wanda ya baki labarin tana aiko min abincin be baki labarin ta daina ba?”

“Kana kareta ne kawai, amman yq za ayi ta daima bayan ta fara kuma silar hakan ka daina cin abincin rana a gidanka? Daman can ai irin yan barikin zaurawan nan sun fi kowa iya karuwanci”

“Abunda take min kyautatawa ce kawai a matsayina na dan'uwanta kuma kin fi kowa sani Halima na tsattsiya ce”

Yana fadar hakan ya sake ya juya ya fice daga kitchen din fuskarsa na nuna rashin jindadin kalaman Suwaiba, tabe baki tai ta bishi da kallo haushi, ita kadai ta san abunda take ji ta rasa gane wani irin so yake ma Halima? Ko da yake ba laifinsa ba ne laifin Halimar ne daman shi namiji ai kamar yaro ne, duk inda aka bi da shi can yake, ta dade tana masa maganar abincin da Halima take aika masa a office duk kuwa da kasancewar ya sha nuna mata cewar baya son maganar, ta hanyar Yayanta da ke aiki Asibiti a matsayin nurse ta samu labarin.

“Sai na ci miki mutunci Wlh, sai na bayyana halinki a gaban kowa, daga lokacin zan gani idan za ki sake bibiyar Abdallah banza ballagaza kawai, in banda jahilci taya zaka auri yaya kuma ka koma bibiyar kane, kaji iskanci, sai an tozarta ki Wallahi”

Ta fada tana kwafa sannan ta juya ta cigaba da aikinta...

AHMAD POV.

tukin motar kawai yake amman hankalinsa yana can ya tafi gurin labarin da ya ji, sai a yanzu ya fahimci a kashi 100 na kaddarar rayuwa shi ko kashi daya be dauka ba, domin shi ya da mata sai mahaifi kawai ya rasa, amman ita ta rasa abubuwa da yawa a ciki akwai farinciki akwai gata akwai mutunci, a haka kuma har tana filin sake daukar wani kalar bacin rai a zuciyarta, tunawa yai da yadda take yawan masifa wata kila saboda tana cikin damuwa ne, ta yi kokari ta jajirce da har bata haukace ba ko kuma wani ciwon ya hana ta tashi kamar yadda shi a yanzu ciwon zuciya yake neman kai shi kasa. Tunawa da yai da irin abunda yai mata a wacan lokacin da kuma kadeta da yai yasa jin wani iri, anya mai irin wannan rayuwar ya cancanci a sake shimfida masa wata bakar magana ma balle har a aikata masa wani abu marar dadi? An keta mata an keta haddin yarta shi ya fi komai tsaya masa a rai, see yadda yake kyamar auren matar da ta auri wani auren sunna ma, to ita faya zata ji an yi mata da karfi? And ayi wayarta yar da bata san komai ba? And a lokacin kwatar hakkin yarta mijinta ya saketa bayan kuma kanensa ne ya ketawa yar haddi, wani irin mugun miji ne wannan? Baya son ta aureta ne? Ko dole akai mata? Aunata yake a matsayin Siyama, ya zai ji idan wani ya taba masa kanwa kamar haka? And the most saddest thing bata da mai tsaya mata tun a wacan lokacin, she's the first born ya tuna a cikin wasikarta ta fadi hakan, and the other sad part is ya kara mata damuwa da zarginta da mutuwar Namra, sai a yanzu yake gode Allah da Hajiya ta hana shi daukar mataki a kai da ya cutar da innocent soul.

“Gwarzo... Ba gida za mu je ba?”
Chapter 85 · 0% Book details