Sashe 41
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abdulhamid be shigo ba sai bayan sallah magariba, na masa sannu da zuwa kamar yadda na saba na raka shi har daki na hada masa ruwan wanka domin na san wanka ne abunda mijina yafi bukata a duk lokacin da ya dawo daga gurin aiki. Kamin ya fito na jera masa abinci da ruwa mai sanyi sannan na fiddo masa da jallabiyarsa, da kaina na karbi karamin tawul din na natse masa jiki sannan na shafa masa mai sannan ya saka gajeren wando ya dora Jallabiyar sama. Zaunawa yai ni kuma na soma zuba masa abincin ina ta kallon yanayinsa kamar yadda na lura da kwana biyun nan ya fiye kallona.
A tare muka soma cin abincin kamar yadda muka saba sai da na tabbatar ya kusa koshi sannan na fara bijiro masa da maganar.
“Hubby Akwai wata magana da nake son mu yi mai muhimmanci....”
Tarar numfashina yai.
“Ya jikinki....? Na manta dazun da muka tashi ban tambaye ki ciwon marar ba”
Wani dif na ji numfashina yai dogon zango, kamar wacce zata suma sannan ya dawo min kamar an jefo shi.
“Na ji sauki, akan hakan ne nake son mu yi magana”
“Uhm ina jinki”
Yadda yai maganar da yadda ya fuskance ni sai ya saka ni tsoro da fargaba kwarjinisa duk sai ya cika ni, har na kasa furta komai.
“Ina jinki”
Spoon din hannuna na aje na kama hannunsa na rike na saka idona cikin nasa.
“Ban san yadda zaka dauki abunda zan fada maka ba, ban san ya za ka ji a zuciyarka ba, ban san wani irin kallo za kamin ba, za ka iya cigaba da zama da ni akan kaddarar da ta same ni ko a'a, ban sani ba iyakar abunda na sani shine bana da kwanciyar hankali idan ban fada maka.....”
Idona ne ya cika da hawaye sai nai saurin kawar da fuskata daga barin kallonsa.
“Me kika aikata?”
Yawun bakina na hade na sake kallonsa a karo na biyu sannan na ce
“Ban aikata komai ba, darajata aka taba....!”
“Ban gane ba”
Shiru nai na kasa cewa komai sai hawaye na ke shar kamar ba gobe, shi kuma bayan kallona babu abunda yake.
“Zaka iya tuna lokacin da ka tafi Abuja karbar wasu takardu? Ka bar ni ni kadai?.....”
Cikin natsuwa irin ta masu gaskiya na zayyana masa komai, ba natsuwa irinta ta masu kwanciyar hankali ba, kallon kallo muka ko yi ma junanmu akuya kallom kura, idona na hawaye ina kallonsa, yayinda shi ma yake min kallon da ban san na minene ba, yarda ko akasin hakan ko kuma tausayi? Sosai nake Kallona na kasa dauke idona daga kansa, so nake ya fada min cewar ya aminta da ni tausayi da kulawa da kauna nake son gani a fuskata, so nake na ga idonsa sun cika da hawaye saboda mu yi kukan a tare mu yi jumamin a tare.
Be ce min komai ba, be kuma daina kallona ba, be nuna min wata alama ta yarda ko akasin hakan ba, ban tsinka jimami a idonsa ba balle har na iya hararo tausayi a zuciyarsa.
Ni din ce da kaina na tsargu na mike tsaye na bar masa gurin, ina jin zuciyata na min wani irin zafi kamar zata fashe, idonuwana kuma suna ta min yaji saboda hawaye daya hana ni gani daidai. Dakina na dawo na kwanta saman gadona na mika hannuna na janyo fillo ya dora kaina dayan hannun kuma na rika shafa gadon da shi kamar ban san abunda nake ba, kwancin ya gagareni sai na sauko na zauna a kasa na dora kaina a saman gadon.
Uwa ce ni, amman a yau ji nake kamar ace akwai wata uwar a kusa da ni ta rarrashen ta fada min komai zai wuce, ina son naji wata kalma mai dadi ina son na ji an fada min cewar wata rana zan yi dariya wata rana zan yi farinciki, ina ma a ce Mama ta san da maganar nan da ita kadai zata iya ba ni hakuri ita ce kadai zata taya ni mu yi kuka tare kamar yadda nai da Namra.
“Kaicon ki Halimatu? Wace ƴa ce za a yi mata fyade kuma ayi ma uwarta? Nai kukan yata kuma nai nawa? Yau kenan ya gobena zata kasance?”
Mikewa nai tsaye ina kara magana da kaina kamar wata tabbabiya.
“Ya isa shikenan komai ya wuce, abunda ya faru ya riga ya faru ba zan iya canja shi ba, ba kuma zan iya goge shi ba, shikenan ai kaddarata ce wannan”
Ina kaina nan na fadi kasa zaune na fashe da wani irin kuka da ban san ta ina hawayen ke fito min ba. Na kan yi kuka har na samuwa natsuwa ko kuma na samu sukuni amman a yau sai na nemi natsuwa da sukunin na rasa, kukan ya ko ya tsaya min kamar yadda hawayen ma ce min sallamu alaikum. Wani kalar sara na ji kaina na yi idonawa har rufewa suke saboda ciwo, har kuma lokacin hawayen ba su daina min zuba ba. Karfin hali nai na tashi na shiga kitchen na dauko flask din na hadawa kaina tea da cup nai ta feta har ya sha iska sannan na kurba kadan, wani abun mamaki sai na kas hadewa kamar wacce tasha wani abun mutuwa, kuka ya subuce min.
‘Ke fa uwace Halimatu, idan Namra ko Amal ko Adnan ko Amir suka shiga damuwa gurinki za su zo, ke za ki sama musu mafita, so be a strong woman....’
Shine abunda zuciyata yake fada min, kai na gyada ina karfafawa kaina kuiwa sannan na shiga bandaki nai wanka har kan nawa da ke ciwo sai da wanke dan kaiwa na samu salama. Daure da tawul na fito na nufi gaban madubi na zauna ina ta kallon kaina, hawayen idona be daina zuba ba kamar yadda ruwan kaina suke zuba. Ina jin motsin shigowar Abdulhamid gabana ya yanke ya fadi, daga jikin kofar dakin ya tsaya yana kallona.
“Amman Halima ba su bar wata alama da za a gane cewar yan fashi sun shigo gidan nan ba? Ba su fasa komai ba? Ba su dauki komai ba? Ba su harbi kowa ba? Kuma duk a unguwar nan ba su shiga ko'ina ba sai nan? Kuma ba su zo ba sai ranar da bana nan?”
Ta cikin madubin na aika masa da kallo sai murmushi ya bayyana a fuskata, still hawaye na sauko min.
“Wacce zan fara amsawa a cikin tambayoyinka?”
“Halima babu yadda za ayi 6arawo mai makami ya shigo gidan nan be bar wata alama da zata nuna cewar ya shigo ba, and if gaskiya ne miyasa ba ki fada min tun farko ba sai yanzu, and miyasa kika yi kokarin zubar da cikin? Ba ki fada min ba sai da kika fara gano cewar na gane halin da ake ciki shiyasa kika kirkiri wannan? Na kasa yarda cewar ke ce Halima!”
Wannan karon juyowa nai na fuskance shi.
“Ni din ce dai Abdulhamid, ka yi tunani iya yadda zuciyarka ta kawo maka, Halimatu ce! Karka damu wannan din ma yana cikin kaddararta, na yarda wani sabwar kaddarar ce ta fuskance ni kuma ta bude min sabon shafi, na shirya karbar ta da hannu biyu, na sani bakinciki baya taba dawwama, kamar yadda jindadi ba ya dawwama, ko dai bakincikin ya tafi ya bar ni, ko kuma ni na mutu na bar shi, kuma gaskiya a duk inda take gaskiya ce zata bayyana ko da bayan raina...”
Takowa yai ya karaso kusa da ni ya dafa ni ya tayarda ni tsaye ya kalle ni da idonsa da ke zubar da kwalla.
“Saboda ina kaunarki na aureki, har ga Allah na yarda da ke..... amman zuciyata ta kasa natsuwa da wannan, duk wani kuduri da nake da shi akanki ne, duk wani buri da nake da shi akan ki ne, na san kin yi jihadin aurena bayan kin san bana iya komai, wannan kadai ya isa ya nuna cewar kina kaunata, amman be isa ya wadatar da cewar za ki iya tsare kanki ba, wannan abun da ya faru laifina ne na cutar da ke, taya son rai yasa na cilasta miki aurena bayan na san ba zan iya sauke hakokinki ba, komai kika aikata ba ki yi laifi ba Halima saboda ni ne ba mutum ba, da ace ni din namiji ne kamar kowa da duk hakan be faru ba da baki rasa komai ba”
Hannayensa ya kai ya riko fuskata ya matso da tasa fuskar daf da tawa yana hawaye kamar yadda ni ma nake.
“Wannan sirrinmu ne, babu wanda zai ji? Karki fadawa kowa mu bar wannan a tsakaninmu, na miki alkawari ba zan ta a fadawa kowa ba, babu wanda zai ji wannan abun daga gareni, kuma zan cigaba da zama da ke kamar yadda muka saba, na sani ni ma wannan jarabawata ce, and i think this is the only way da zan iya repay na aurena da kika a yadda na ke marar lafiya, saboda Allah ya kaddaro min haka a rayuwata, na yafe miki har Allah na yafe miki kuma ina fatar Allah ya yafe miki....!”
Yana kaiwa nan ya hade yawun bakinsa ya dauke hannayensa daga fuskata ya juya yana cigaba da hawaye ya fice. Ban yi zaton akwai wani sauran karfi a jikina ba, a take kafafuwana suka fara rawa sai gani a kasa zaune jikina na ta rawa kamar wacce ta fito daga cikin kankara.!
ABDALLAH POV.
Cikin wani irin bachin rai ya shigo gidan, tun daga yanayin parking dinsa ma ya isa a gane hakan balle kuma idan a kai arba da fuskarsa, zuciyarsa har wani bugawa take da karfi kamar zata fito.
Dukan yaransa suna falo kasancewar yau Thursday babu islamiya school, suna masa sannu da zuwa amman be amsa musu ba kai tsaye ya nufi dakin Mahaifiyarsu. Tana zaune saman gado tana waya ganinsa da kuma yanayinsa yasa ta katse wayar tana kallonsa.
“Me yake damunki Suwaiba?”
Da karfi ya aika mata da tambaya sai da hantar cikinta ta kada.
“Me na aikata?”
“Ba ki san abunda kika aikata ba? Ba a nan muka gama maganar Halimatu ba? Akan me za ki dauki wannan maganar ki kaita social media a page irin wannan?”
A tare muka soma cin abincin kamar yadda muka saba sai da na tabbatar ya kusa koshi sannan na fara bijiro masa da maganar.
“Hubby Akwai wata magana da nake son mu yi mai muhimmanci....”
Tarar numfashina yai.
“Ya jikinki....? Na manta dazun da muka tashi ban tambaye ki ciwon marar ba”
Wani dif na ji numfashina yai dogon zango, kamar wacce zata suma sannan ya dawo min kamar an jefo shi.
“Na ji sauki, akan hakan ne nake son mu yi magana”
“Uhm ina jinki”
Yadda yai maganar da yadda ya fuskance ni sai ya saka ni tsoro da fargaba kwarjinisa duk sai ya cika ni, har na kasa furta komai.
“Ina jinki”
Spoon din hannuna na aje na kama hannunsa na rike na saka idona cikin nasa.
“Ban san yadda zaka dauki abunda zan fada maka ba, ban san ya za ka ji a zuciyarka ba, ban san wani irin kallo za kamin ba, za ka iya cigaba da zama da ni akan kaddarar da ta same ni ko a'a, ban sani ba iyakar abunda na sani shine bana da kwanciyar hankali idan ban fada maka.....”
Idona ne ya cika da hawaye sai nai saurin kawar da fuskata daga barin kallonsa.
“Me kika aikata?”
Yawun bakina na hade na sake kallonsa a karo na biyu sannan na ce
“Ban aikata komai ba, darajata aka taba....!”
“Ban gane ba”
Shiru nai na kasa cewa komai sai hawaye na ke shar kamar ba gobe, shi kuma bayan kallona babu abunda yake.
“Zaka iya tuna lokacin da ka tafi Abuja karbar wasu takardu? Ka bar ni ni kadai?.....”
Cikin natsuwa irin ta masu gaskiya na zayyana masa komai, ba natsuwa irinta ta masu kwanciyar hankali ba, kallon kallo muka ko yi ma junanmu akuya kallom kura, idona na hawaye ina kallonsa, yayinda shi ma yake min kallon da ban san na minene ba, yarda ko akasin hakan ko kuma tausayi? Sosai nake Kallona na kasa dauke idona daga kansa, so nake ya fada min cewar ya aminta da ni tausayi da kulawa da kauna nake son gani a fuskata, so nake na ga idonsa sun cika da hawaye saboda mu yi kukan a tare mu yi jumamin a tare.
Be ce min komai ba, be kuma daina kallona ba, be nuna min wata alama ta yarda ko akasin hakan ba, ban tsinka jimami a idonsa ba balle har na iya hararo tausayi a zuciyarsa.
Ni din ce da kaina na tsargu na mike tsaye na bar masa gurin, ina jin zuciyata na min wani irin zafi kamar zata fashe, idonuwana kuma suna ta min yaji saboda hawaye daya hana ni gani daidai. Dakina na dawo na kwanta saman gadona na mika hannuna na janyo fillo ya dora kaina dayan hannun kuma na rika shafa gadon da shi kamar ban san abunda nake ba, kwancin ya gagareni sai na sauko na zauna a kasa na dora kaina a saman gadon.
Uwa ce ni, amman a yau ji nake kamar ace akwai wata uwar a kusa da ni ta rarrashen ta fada min komai zai wuce, ina son naji wata kalma mai dadi ina son na ji an fada min cewar wata rana zan yi dariya wata rana zan yi farinciki, ina ma a ce Mama ta san da maganar nan da ita kadai zata iya ba ni hakuri ita ce kadai zata taya ni mu yi kuka tare kamar yadda nai da Namra.
“Kaicon ki Halimatu? Wace ƴa ce za a yi mata fyade kuma ayi ma uwarta? Nai kukan yata kuma nai nawa? Yau kenan ya gobena zata kasance?”
Mikewa nai tsaye ina kara magana da kaina kamar wata tabbabiya.
“Ya isa shikenan komai ya wuce, abunda ya faru ya riga ya faru ba zan iya canja shi ba, ba kuma zan iya goge shi ba, shikenan ai kaddarata ce wannan”
Ina kaina nan na fadi kasa zaune na fashe da wani irin kuka da ban san ta ina hawayen ke fito min ba. Na kan yi kuka har na samuwa natsuwa ko kuma na samu sukuni amman a yau sai na nemi natsuwa da sukunin na rasa, kukan ya ko ya tsaya min kamar yadda hawayen ma ce min sallamu alaikum. Wani kalar sara na ji kaina na yi idonawa har rufewa suke saboda ciwo, har kuma lokacin hawayen ba su daina min zuba ba. Karfin hali nai na tashi na shiga kitchen na dauko flask din na hadawa kaina tea da cup nai ta feta har ya sha iska sannan na kurba kadan, wani abun mamaki sai na kas hadewa kamar wacce tasha wani abun mutuwa, kuka ya subuce min.
‘Ke fa uwace Halimatu, idan Namra ko Amal ko Adnan ko Amir suka shiga damuwa gurinki za su zo, ke za ki sama musu mafita, so be a strong woman....’
Shine abunda zuciyata yake fada min, kai na gyada ina karfafawa kaina kuiwa sannan na shiga bandaki nai wanka har kan nawa da ke ciwo sai da wanke dan kaiwa na samu salama. Daure da tawul na fito na nufi gaban madubi na zauna ina ta kallon kaina, hawayen idona be daina zuba ba kamar yadda ruwan kaina suke zuba. Ina jin motsin shigowar Abdulhamid gabana ya yanke ya fadi, daga jikin kofar dakin ya tsaya yana kallona.
“Amman Halima ba su bar wata alama da za a gane cewar yan fashi sun shigo gidan nan ba? Ba su fasa komai ba? Ba su dauki komai ba? Ba su harbi kowa ba? Kuma duk a unguwar nan ba su shiga ko'ina ba sai nan? Kuma ba su zo ba sai ranar da bana nan?”
Ta cikin madubin na aika masa da kallo sai murmushi ya bayyana a fuskata, still hawaye na sauko min.
“Wacce zan fara amsawa a cikin tambayoyinka?”
“Halima babu yadda za ayi 6arawo mai makami ya shigo gidan nan be bar wata alama da zata nuna cewar ya shigo ba, and if gaskiya ne miyasa ba ki fada min tun farko ba sai yanzu, and miyasa kika yi kokarin zubar da cikin? Ba ki fada min ba sai da kika fara gano cewar na gane halin da ake ciki shiyasa kika kirkiri wannan? Na kasa yarda cewar ke ce Halima!”
Wannan karon juyowa nai na fuskance shi.
“Ni din ce dai Abdulhamid, ka yi tunani iya yadda zuciyarka ta kawo maka, Halimatu ce! Karka damu wannan din ma yana cikin kaddararta, na yarda wani sabwar kaddarar ce ta fuskance ni kuma ta bude min sabon shafi, na shirya karbar ta da hannu biyu, na sani bakinciki baya taba dawwama, kamar yadda jindadi ba ya dawwama, ko dai bakincikin ya tafi ya bar ni, ko kuma ni na mutu na bar shi, kuma gaskiya a duk inda take gaskiya ce zata bayyana ko da bayan raina...”
Takowa yai ya karaso kusa da ni ya dafa ni ya tayarda ni tsaye ya kalle ni da idonsa da ke zubar da kwalla.
“Saboda ina kaunarki na aureki, har ga Allah na yarda da ke..... amman zuciyata ta kasa natsuwa da wannan, duk wani kuduri da nake da shi akanki ne, duk wani buri da nake da shi akan ki ne, na san kin yi jihadin aurena bayan kin san bana iya komai, wannan kadai ya isa ya nuna cewar kina kaunata, amman be isa ya wadatar da cewar za ki iya tsare kanki ba, wannan abun da ya faru laifina ne na cutar da ke, taya son rai yasa na cilasta miki aurena bayan na san ba zan iya sauke hakokinki ba, komai kika aikata ba ki yi laifi ba Halima saboda ni ne ba mutum ba, da ace ni din namiji ne kamar kowa da duk hakan be faru ba da baki rasa komai ba”
Hannayensa ya kai ya riko fuskata ya matso da tasa fuskar daf da tawa yana hawaye kamar yadda ni ma nake.
“Wannan sirrinmu ne, babu wanda zai ji? Karki fadawa kowa mu bar wannan a tsakaninmu, na miki alkawari ba zan ta a fadawa kowa ba, babu wanda zai ji wannan abun daga gareni, kuma zan cigaba da zama da ke kamar yadda muka saba, na sani ni ma wannan jarabawata ce, and i think this is the only way da zan iya repay na aurena da kika a yadda na ke marar lafiya, saboda Allah ya kaddaro min haka a rayuwata, na yafe miki har Allah na yafe miki kuma ina fatar Allah ya yafe miki....!”
Yana kaiwa nan ya hade yawun bakinsa ya dauke hannayensa daga fuskata ya juya yana cigaba da hawaye ya fice. Ban yi zaton akwai wani sauran karfi a jikina ba, a take kafafuwana suka fara rawa sai gani a kasa zaune jikina na ta rawa kamar wacce ta fito daga cikin kankara.!
ABDALLAH POV.
Cikin wani irin bachin rai ya shigo gidan, tun daga yanayin parking dinsa ma ya isa a gane hakan balle kuma idan a kai arba da fuskarsa, zuciyarsa har wani bugawa take da karfi kamar zata fito.
Dukan yaransa suna falo kasancewar yau Thursday babu islamiya school, suna masa sannu da zuwa amman be amsa musu ba kai tsaye ya nufi dakin Mahaifiyarsu. Tana zaune saman gado tana waya ganinsa da kuma yanayinsa yasa ta katse wayar tana kallonsa.
“Me yake damunki Suwaiba?”
Da karfi ya aika mata da tambaya sai da hantar cikinta ta kada.
“Me na aikata?”
“Ba ki san abunda kika aikata ba? Ba a nan muka gama maganar Halimatu ba? Akan me za ki dauki wannan maganar ki kaita social media a page irin wannan?”