Sashe 95
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“To ya kamata a tambaye ta, ko kuma a ga likitanta, yanzu dole sai ta farka zamu iya yin wasu gwaje gwajen, amman jinin zuciyarta yana gudu da karfi fiye da kima wanda hakan matsala ne babba gaskiya, har yanzu da take sume zuciyarta na bugawa fiye da yadda ake son tana bugawa”
“Babu wani abu da zaka iya yi mata Doc i trust you”
“Yeah dole ne sai mun san irin gwaje gwajen da akai mata, kuma tana karkashin shan magani ko a a? Kamin yanzu ya zuciyarta so dole sai ta farka ko kuma idan kasan likitan da ke dubata zaka iya hada ni da shi”
“Ban sani ba, ban san komai akan hakan ba, dole sai ta farka ko kuma wani daga danginta ya fada”
“Yanzu dai best medicine shine a daina bata mata rai ko barinta da damuwa, duk maganin da za a bata zai taimaka mata ne kawai abun yai kasa, amman ba zai iya wakar da ita ba, matukar ba ta daina damuwa ko kuma a daina bata mata rai ba”
“Thank you”
Shine abunda ya fada ya juya zuciyarsa cike da tunani kala kala ya fice daga office din. Harabar asibitin ya fito ya nufi gurin da ya aje motarsa ya shiga yai mata key, ba gida ya jufa kai tsaye ba, family house din su Halimatu ya nufa a gurin yai musu gaisuwa ya kuma shiga har cikin gidan yai ma mahaifiyarta da yan'uwanta gaisuwa. Ko da ya fito unguwar ana Sallah magariba a hanya ya tsaya yai sallah sannan ya karasa gidan Hajiyarsa jikinsa duk a sanyaye, mutuwar mahaifin Halimatu ya tuna masa da mutuwar nasa mahaifin da kuma matarsa da yarsa, kuma ta tuna masa cewar Hajiya da Siyama ne kawai suka rage masa. A falon Hajiya ya zauna tasa aka kawo masa abincin amman ya kasa kallon abincin ma balle ya ci. Ita kanta mutuwar mahaifin Halimatu ya tuna mata da mutuwar mijinta mutum mai dattako da taimako.
Haka yai zaune ya zubawa katon tv ido duk da hankalinsa ba a can yake ba.
“Allah yai muka albarka Ahmad kai da Siyama, ya yalwantar zuri'ar Muhammadu ta karkashinku”
“Amin Hajiya”
Ya fada yana dauke kansa daga kallon tv ya kalleta.
“Ina tunanin aika abincin a gidansu What do you think?”
“Hakan na da kyau, a yanzu mai taimaka musu suke nema, Allah dai yai masa rahama”
“Amin, dazun da safe nake ta tunani a raina cewar ya kamata na samu mahaifinta da maganar mutumen nan mai bibiyarta, domin ina tunanin iyayenta ba su sani ba, a gidansu ma bana tunanin akwai wanda ya sani, a tare muka je meeting dazun ina son nai mata maganar ganin mahaifinta, amman duk sai naji ina jin nauyi na kasa yi mata magana, ashe duk lokacin ma ya rasu”
“Allah be kaddarar ganawarku bane, amman wannan yarinyar tana cikin taskon rayuwa, a halin da take ciki kuma wani ya fada mata, Wallahi ta bani tausayi sosai, tana bukatar farinciki ko yaya ne a yanzu”
Be yi kasa a guiwa ba ya labartawa Hajiya abunda Doc Nura ya fada masa.
“Irin wannan mahaifiyar da ace tana da kudi sai ta dauke ta ta kai ta can wata kasar ta huta ta wannan kunci har sai ta samu sauki ta dawo, Allah sarki rayuwa kenan Allah ya yaye mata”
“Amin”
Ya amsa yana sauke ajiyar zuciya.
HALIMATU POV.
Ba zan iya fadar awannin da na dauka a sume ba, dan dai ba a mutuwa a dawo na nace mutuwa nai na dawo, domin komai na dakin ganinsa nake fari tas, ina jin yawun bakina ya kafe, hayaniyar mutanen uku da ke tsaye kaina ma jinta nake kamar wani yare, ina jin suna taba jikin suna soka min abu suna danna zuciyata can kuma suka daga idona, na kusan minti goma shabiyar a haka sannan idanuwana suka fara gani daidai, sai dai jikin babu kuzari ko kadan yawun bakin ma har a yanzu babu su, numfashin ma ina jin kamar baya isata.
“Sannu”
Likitan ya fada, sai na gyada masa kai, ina kallonsa ya sake yi min wata allurar a cikin ruwan dake shiga cikin jikina. Bayan fitar likitocin na fara kokarin tuna abunda ya kawo ni dakin, a take kaina ya saka hawaye suka samu haya, a hankali na juya kaina sai nai arba da inna Lami, hakan ya tabbatar min da mahaifi na rasa kenan, domin da Mama na rasa da Inna Lami ba zata iya zuwa nan ba saboda kukan rashin yar'uwarta uwa daya uba daya.
“Sannu Halimatu Allah ya baki lafiya”
Unkura nai na tashi amman na kasa sai hawaye nake jikin nawa har lokacin babu kuzari.
“Lafiya kalau na fita na bar Baba, miya same shi?”
“Ai baya bata da kadan Halimatu, ciwon ciki ne ya taso masa sai amai ko kamin ayi wani abu yace garinku”
“Da gaske Uba na rasa”
Na fashe da wani irin kuka mai ban tausayi. Ban tana jin irin abunda na ji a yau ba, kamar nai hauka nake ji, kamar nai ihu na dawo da shi, ashe haka yaran da suka rasa iyayensu suke ji? Ashe haka mairaici yake da ciwo, ga ni kenan da nai aure har na haifi yara, ina ga kanena da basu yi auren ba, a take tausayinsu ya kara rufe min zuciya.
Na dade ina kukan duk yadda Inna rai rarashina sai na ji kamar tana kara kura wutar kukan ne, misalin karfe daya aka bani tea na sha sai lemun hausa da aka yanka min, a daren ban sake runtsawa ba har safe.
Duk yadda likitan ya so na sauna har nan da kwana biyu ban nuna masa amincewa ta ba, a dole ya sallame ni bayan ya bani shawarar na sake dawowa nan da kwana biyu domin a duba lafiyata. Ya fada min halin da zuciyata take ciki da kuma irin treatment din nake bukata.
Misalin goma muka baro asibiti tare da Inna, da wasu yan'uwanmu da suka zo dubamu, kamin mu isa gida Mama ta fado min rai, sai duk tsoro ya kamani kar na zo na rasa ta ita tun da tana da hawan jini, tun a napep din nai ta kokarin tsayar da hawayena amman abun ya gagara ashe hawayen mutuwa su suke yin kansu, ina ta ganin kamar idan na isa gida zan yi arba da Baba ne a inda ya saba zama, sautin muryarsa yana ta dawo min a kunne, yadda yake dariya da duk wani hali nasa na kirki zuciyata tana ta janyo min shi. Ban kara tsinkewa ba sai da nai arba da yan karbar gaisuwar a kofar gidanmu, lallai mutuwa babu wanda ba shi da tambonki, a lokacin dana shiga cikin gidan sai kukan kowa ya koma sabo, saboda yadda nake ta nawa kukan, idan na kalli kanena da mahaifiyata da abokiyar zamanta sai na rasa wa zan tausayawa.
Hakika mutuwa bata da dadi, duk wanda ya zo mana gaisuwa sai yai mana nasiha akan hadin kai da son junanmu, an yi ta zuwa mana gaisuwa mutane da yawa wasu har bana ganesu, abunda Abdallah yai min ya kara min son sa sosai a raina, ya nuna min na zama mai karfin zuciya da dakiya, ni ce babba idan kanena sukai ba daidai ba na musu fada kamar yadda zan yi ma yayana, ya kawo abinci mai yawa da kudi. Abdulhamid ma ya saka an kira masa ni yai min gaisuwa, Aminu kam da shi akai zaman uku har aka gama, ranar da akai sadakan ukun mama take fadin cewar Ahmad ya aiko muna da abinci da kudi mai dama kuma ya shigo har cikin gidan yai musu gaisuwa.
A daren ranar Abraham ya ziyarce ni, irin ziyarar da ya saba kawo min a duk lokacin da ya so ganina.
At first fuskata ya fara haskawa da wayarsa.
“Ki yi hakuri, rashin wani ba dadi duk da dai ban rasa kowa ba, amman na san babu dadi can I hug you”
“Na gode”
Na fada ban jira cewarsa ba na jiya na bar masa wajen, a daren ranar sai gidam ya zame mana kamar wani kango, muna ta firar Baba muna kuka, Aisha take cewa kara ni na yi aure na haihu har yaga yayana su ko auren ba su ba, sai naji duk tausayinta ya kara kamani.
Wasa wasa aka dauki sati daya babu Baba Mama da Inna suka shiga takaba, a lokacin ne na kara tabbatar da mutuwarsa, a kowace rana sai na tuna yadda nake zuwa gaishe shi da yadda yake shigowa cikin gida.
Haka na kwashe sati biyu ban leka gurin aikina ba, kowa kuma be leko ni daga can ba, sai dai wata na karewa na ga albashin 67000, maimakon na jidadi sai na ji rashinsa domin na saba a lokacin da nake aiki nakan cire wani abu nai ma Baba da Mama da Inna siyaya.
Washe garin ranar da na ga albashin na shirya na tafi gurin aikina, ban ji kowa ya min gaisuwa ba hakan yana nufin babu wanda ya san da zancen mutuwar kenan, na nufi office dina cikin rashin walwala, sai na samu matar can a ciki wato Zainab, mun gaisa da ita cikin mutuntawa sannan tai min bayani wai oga ne yace ta zauna na wucin gadi har zuwa lokacin da zan dawo.
“Okay”
“Amman ki fara zuwa ki fada masa kin dawo tukuna”
Ba musu na juya na fita daga office din na nufi hanyar da zata sadani da office dinsa, sai na shiga office na farko na shiga na biyu sannan na isa nasa. Ko da na shiga yana zaune jikin kujera yana waya, ganina ya saka ya yanke wayar ya taso da far'ar shi ta wayayin mutane kamar ba Ahmad ba ya tare ni.
“Wow my friend na dauka zaki yi wata fa”
Na yi kasa da kaina.
“Ina kwana ranka ya dade”
“Lfy kalau ya hakuri”
“Al-hamdulillah, na zo office na tararda wata”
“Yeah kin san gurin ba a barinsa hakanan ba kowa, shiyasa muka sakata kamin ki dawo, ina fatar ba mu yi laifi ba”
“Kamfaninka ne kana da dama da yancin da zaka yi duk abunda kake so, ciki har da korata ko canja min gurin”
Na fada muryata na fita so slow.
“Babu wani abu da zaka iya yi mata Doc i trust you”
“Yeah dole ne sai mun san irin gwaje gwajen da akai mata, kuma tana karkashin shan magani ko a a? Kamin yanzu ya zuciyarta so dole sai ta farka ko kuma idan kasan likitan da ke dubata zaka iya hada ni da shi”
“Ban sani ba, ban san komai akan hakan ba, dole sai ta farka ko kuma wani daga danginta ya fada”
“Yanzu dai best medicine shine a daina bata mata rai ko barinta da damuwa, duk maganin da za a bata zai taimaka mata ne kawai abun yai kasa, amman ba zai iya wakar da ita ba, matukar ba ta daina damuwa ko kuma a daina bata mata rai ba”
“Thank you”
Shine abunda ya fada ya juya zuciyarsa cike da tunani kala kala ya fice daga office din. Harabar asibitin ya fito ya nufi gurin da ya aje motarsa ya shiga yai mata key, ba gida ya jufa kai tsaye ba, family house din su Halimatu ya nufa a gurin yai musu gaisuwa ya kuma shiga har cikin gidan yai ma mahaifiyarta da yan'uwanta gaisuwa. Ko da ya fito unguwar ana Sallah magariba a hanya ya tsaya yai sallah sannan ya karasa gidan Hajiyarsa jikinsa duk a sanyaye, mutuwar mahaifin Halimatu ya tuna masa da mutuwar nasa mahaifin da kuma matarsa da yarsa, kuma ta tuna masa cewar Hajiya da Siyama ne kawai suka rage masa. A falon Hajiya ya zauna tasa aka kawo masa abincin amman ya kasa kallon abincin ma balle ya ci. Ita kanta mutuwar mahaifin Halimatu ya tuna mata da mutuwar mijinta mutum mai dattako da taimako.
Haka yai zaune ya zubawa katon tv ido duk da hankalinsa ba a can yake ba.
“Allah yai muka albarka Ahmad kai da Siyama, ya yalwantar zuri'ar Muhammadu ta karkashinku”
“Amin Hajiya”
Ya fada yana dauke kansa daga kallon tv ya kalleta.
“Ina tunanin aika abincin a gidansu What do you think?”
“Hakan na da kyau, a yanzu mai taimaka musu suke nema, Allah dai yai masa rahama”
“Amin, dazun da safe nake ta tunani a raina cewar ya kamata na samu mahaifinta da maganar mutumen nan mai bibiyarta, domin ina tunanin iyayenta ba su sani ba, a gidansu ma bana tunanin akwai wanda ya sani, a tare muka je meeting dazun ina son nai mata maganar ganin mahaifinta, amman duk sai naji ina jin nauyi na kasa yi mata magana, ashe duk lokacin ma ya rasu”
“Allah be kaddarar ganawarku bane, amman wannan yarinyar tana cikin taskon rayuwa, a halin da take ciki kuma wani ya fada mata, Wallahi ta bani tausayi sosai, tana bukatar farinciki ko yaya ne a yanzu”
Be yi kasa a guiwa ba ya labartawa Hajiya abunda Doc Nura ya fada masa.
“Irin wannan mahaifiyar da ace tana da kudi sai ta dauke ta ta kai ta can wata kasar ta huta ta wannan kunci har sai ta samu sauki ta dawo, Allah sarki rayuwa kenan Allah ya yaye mata”
“Amin”
Ya amsa yana sauke ajiyar zuciya.
HALIMATU POV.
Ba zan iya fadar awannin da na dauka a sume ba, dan dai ba a mutuwa a dawo na nace mutuwa nai na dawo, domin komai na dakin ganinsa nake fari tas, ina jin yawun bakina ya kafe, hayaniyar mutanen uku da ke tsaye kaina ma jinta nake kamar wani yare, ina jin suna taba jikin suna soka min abu suna danna zuciyata can kuma suka daga idona, na kusan minti goma shabiyar a haka sannan idanuwana suka fara gani daidai, sai dai jikin babu kuzari ko kadan yawun bakin ma har a yanzu babu su, numfashin ma ina jin kamar baya isata.
“Sannu”
Likitan ya fada, sai na gyada masa kai, ina kallonsa ya sake yi min wata allurar a cikin ruwan dake shiga cikin jikina. Bayan fitar likitocin na fara kokarin tuna abunda ya kawo ni dakin, a take kaina ya saka hawaye suka samu haya, a hankali na juya kaina sai nai arba da inna Lami, hakan ya tabbatar min da mahaifi na rasa kenan, domin da Mama na rasa da Inna Lami ba zata iya zuwa nan ba saboda kukan rashin yar'uwarta uwa daya uba daya.
“Sannu Halimatu Allah ya baki lafiya”
Unkura nai na tashi amman na kasa sai hawaye nake jikin nawa har lokacin babu kuzari.
“Lafiya kalau na fita na bar Baba, miya same shi?”
“Ai baya bata da kadan Halimatu, ciwon ciki ne ya taso masa sai amai ko kamin ayi wani abu yace garinku”
“Da gaske Uba na rasa”
Na fashe da wani irin kuka mai ban tausayi. Ban tana jin irin abunda na ji a yau ba, kamar nai hauka nake ji, kamar nai ihu na dawo da shi, ashe haka yaran da suka rasa iyayensu suke ji? Ashe haka mairaici yake da ciwo, ga ni kenan da nai aure har na haifi yara, ina ga kanena da basu yi auren ba, a take tausayinsu ya kara rufe min zuciya.
Na dade ina kukan duk yadda Inna rai rarashina sai na ji kamar tana kara kura wutar kukan ne, misalin karfe daya aka bani tea na sha sai lemun hausa da aka yanka min, a daren ban sake runtsawa ba har safe.
Duk yadda likitan ya so na sauna har nan da kwana biyu ban nuna masa amincewa ta ba, a dole ya sallame ni bayan ya bani shawarar na sake dawowa nan da kwana biyu domin a duba lafiyata. Ya fada min halin da zuciyata take ciki da kuma irin treatment din nake bukata.
Misalin goma muka baro asibiti tare da Inna, da wasu yan'uwanmu da suka zo dubamu, kamin mu isa gida Mama ta fado min rai, sai duk tsoro ya kamani kar na zo na rasa ta ita tun da tana da hawan jini, tun a napep din nai ta kokarin tsayar da hawayena amman abun ya gagara ashe hawayen mutuwa su suke yin kansu, ina ta ganin kamar idan na isa gida zan yi arba da Baba ne a inda ya saba zama, sautin muryarsa yana ta dawo min a kunne, yadda yake dariya da duk wani hali nasa na kirki zuciyata tana ta janyo min shi. Ban kara tsinkewa ba sai da nai arba da yan karbar gaisuwar a kofar gidanmu, lallai mutuwa babu wanda ba shi da tambonki, a lokacin dana shiga cikin gidan sai kukan kowa ya koma sabo, saboda yadda nake ta nawa kukan, idan na kalli kanena da mahaifiyata da abokiyar zamanta sai na rasa wa zan tausayawa.
Hakika mutuwa bata da dadi, duk wanda ya zo mana gaisuwa sai yai mana nasiha akan hadin kai da son junanmu, an yi ta zuwa mana gaisuwa mutane da yawa wasu har bana ganesu, abunda Abdallah yai min ya kara min son sa sosai a raina, ya nuna min na zama mai karfin zuciya da dakiya, ni ce babba idan kanena sukai ba daidai ba na musu fada kamar yadda zan yi ma yayana, ya kawo abinci mai yawa da kudi. Abdulhamid ma ya saka an kira masa ni yai min gaisuwa, Aminu kam da shi akai zaman uku har aka gama, ranar da akai sadakan ukun mama take fadin cewar Ahmad ya aiko muna da abinci da kudi mai dama kuma ya shigo har cikin gidan yai musu gaisuwa.
A daren ranar Abraham ya ziyarce ni, irin ziyarar da ya saba kawo min a duk lokacin da ya so ganina.
At first fuskata ya fara haskawa da wayarsa.
“Ki yi hakuri, rashin wani ba dadi duk da dai ban rasa kowa ba, amman na san babu dadi can I hug you”
“Na gode”
Na fada ban jira cewarsa ba na jiya na bar masa wajen, a daren ranar sai gidam ya zame mana kamar wani kango, muna ta firar Baba muna kuka, Aisha take cewa kara ni na yi aure na haihu har yaga yayana su ko auren ba su ba, sai naji duk tausayinta ya kara kamani.
Wasa wasa aka dauki sati daya babu Baba Mama da Inna suka shiga takaba, a lokacin ne na kara tabbatar da mutuwarsa, a kowace rana sai na tuna yadda nake zuwa gaishe shi da yadda yake shigowa cikin gida.
Haka na kwashe sati biyu ban leka gurin aikina ba, kowa kuma be leko ni daga can ba, sai dai wata na karewa na ga albashin 67000, maimakon na jidadi sai na ji rashinsa domin na saba a lokacin da nake aiki nakan cire wani abu nai ma Baba da Mama da Inna siyaya.
Washe garin ranar da na ga albashin na shirya na tafi gurin aikina, ban ji kowa ya min gaisuwa ba hakan yana nufin babu wanda ya san da zancen mutuwar kenan, na nufi office dina cikin rashin walwala, sai na samu matar can a ciki wato Zainab, mun gaisa da ita cikin mutuntawa sannan tai min bayani wai oga ne yace ta zauna na wucin gadi har zuwa lokacin da zan dawo.
“Okay”
“Amman ki fara zuwa ki fada masa kin dawo tukuna”
Ba musu na juya na fita daga office din na nufi hanyar da zata sadani da office dinsa, sai na shiga office na farko na shiga na biyu sannan na isa nasa. Ko da na shiga yana zaune jikin kujera yana waya, ganina ya saka ya yanke wayar ya taso da far'ar shi ta wayayin mutane kamar ba Ahmad ba ya tare ni.
“Wow my friend na dauka zaki yi wata fa”
Na yi kasa da kaina.
“Ina kwana ranka ya dade”
“Lfy kalau ya hakuri”
“Al-hamdulillah, na zo office na tararda wata”
“Yeah kin san gurin ba a barinsa hakanan ba kowa, shiyasa muka sakata kamin ki dawo, ina fatar ba mu yi laifi ba”
“Kamfaninka ne kana da dama da yancin da zaka yi duk abunda kake so, ciki har da korata ko canja min gurin”
Na fada muryata na fita so slow.