Sashe 92
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
“A a babu wani aminci a tsakaninmu, ya nemi yafiyata ne, kuma na rubuta labari ne a ranar children day a gurin ya gane cewar ni ce saboda labarin yarsa ya shigo ciki da kuma na kamfaninsa”
“Ban gane ba zuwa kikai kika fallasa kanka abayyanar jama'a”
“Aa....”
Daya bayan daya na bayyana masa yadda abun ya faru har da zancen siyen tikitin da Abraham yai, hakan kuma ba karamin bata masa rai yayi ba.
“Wayuya kawai taya shi Abraham din zai siya miki ticket kuma ki karba ki je”
“To ba gashi na ci gasar ba”
“Dalla can Sakarya kawai”
Ya kashe wayarsa, a iya tunanina nikam ban ga illar zuwa bukin da nai ba, to ina ruwana da shi ai ba san shi na je ba, dan yarana. Ko da na fito dakin dukansu suna zaune a tsakar gida har Mama sai zancen Aminu suke, kusa da Inna na zauna ina sauraren Mama da ke fadin.
“Namiji dai ba shi da kunya, yanzu duk abubuwan nan da Aminu yai miki har yana iya murje ido yai miki siyayya ya kawo miki yana rokon ki koma masa?ya manta irin cin mutuncin da yai miki ne ko kuwa ya runtse ido ne ya zo?”
“Hmmm Mama ke ma dai kya fada, ni wallahi yanzu ko mai sunansa bana son ji sai na rika ganin kamar ma halinsu daya”
Na Fada ina tabe baki,Sai Inna tai dariya tace.
“Kuma kin ga fa inda rabon shiryarwa sai a shirya tun da akwai yaya har hudu, ai ko aure kika yi a wani wajen hankalinki yana kansu, nikam da za ki bi ta tawa da kin koma masa tun dai ya gyara halinsa kuma mahaifiyarsa ma yanzu tana sonki”
Mama ta tari numfashin Inna tana girgiza kai.
“A a wahalar da ta sha ta isa haka nan, ai ba ayi rai dan wani rai ba, wani lokacin mai hali baya fasa halinsa, Allah dai ya baki wani na kwarai wanda zai so ki tsakani da Allah, wanda zai kaunace ki har karshen rayuwarki, ya zame miki gata hawayen da kika zubar ya share miki su, kuma ya so yayanki kamar nasa, wanda zai rika jin tausayinki yana tsoron cutar da ke”
Dan murmushi nai.
“Samun irin wannan namiji yana da wahala Mama, mutum daya na san zai iya min haka, shi kuma babu wannan damar a yanzu, nikam na yanke kauna daga yin aure a yanzu”
“Haba dai fata na gari lamiri, idan ba ki yi aure ba ki yi me? Aure ya haife ki kuma ya haifa miki yaya, ina kan fatana na ganki a dakin mijinki”
Aisha da Hafiza da Husna kamar jira suke suka hau yi mata yaya, ba ma kamar Hafiza sarkin Baki.
“Mu da ba a kauna ai sai a kai ku kofar gida a aje, wai har wani fata ake mata ga ku zaune, ita ba kara ita ba tayi auren har ta haifi amsu yi mata addu'a, mu da ko mashinshinin ba mu da fa?”
Duk dariya muka saka har ita, sannan su ma tai musu addu'ar. Sai a lokacin na dauko siyayar da Aminu yai min na bude ina dubawa, Atamfa ce har biyu da turare da sabulun wanka da wanki sai yan kayan tande tande, komai ban dauka a gurin na rabawa Mama da Inna atamfar salubun wanka da wanki kuma na bawa kanena turaren na bawa Baba, sauran kayan tande tande kuma a nan na bar su a tsakaninsu suka raba suka cinye.
Ina zaune a gurin amman ko chocolate din ban ci ba, sai aikin danna wayata nake.
“Gobe idan Allah ya kaimu ina son zuwa gidan Gwaggo Ramatu”
Mama ta fada.
“Gaskiya kam kin kwana biyu ba ki leka ta ga, gata ita kadai ta rage muku cikin Gwaggonin”
Na fada still idona yana kan wayata.
“Shiyasa ai nake son zuwa, sai na siya mata salubu na kai mata”
Da gangan na kalli Hafiza na ce
“Ga sabulun Hafiza nan ta baki ki kai mata”
Wata uwar harara ta watsa min.
“Eh ni da ba kya kauna, to ba zan bayar ba, kuma Mama dakinki zan aje shi idan ma ban ganshi ba ba ruwana ni”
Ta fada tana tashi ta bar mana gurin.
“To idan ba ruwanki ai ba ruwan kowa”
Na fada ina dariya Inna ma dariya take, haka ma Mama daman sun san Hafiza bata da na biyu a cikin gidan indai babin fada ne da matsifa, sai dai fa akwai son yan'uwanta kamar ranta, hakan yasa baka iya banbanta ni da ita kace kowa da uwarsa, mu zama kamar uwa daya daman kuma uban ne ya hada.
Washe gari ta kama friday farar rana kuma kuraren lokaci, hakan yasa na gama shiryawa su Amal da wuri suka wuce makaranta ni kuma na shirya a yau ma abayar na saka sai dai wannan maroon color ce, sai da nai musu sallama sannan na nufi gurin aikina.
Tun daga lokacin dana fito gida nake saka ran haduwa da Abraham saboda sabon da yai min na bibiya a baya wani lokaci amman har na isa ban ganshi ba, a yau ma ban ga Kabir ba, hankali ya dan tashi daman na san Ahmad ba zai kyale shi ba bayan abunda ya faru, to amman ina ya kai shi? A wane hali yake? Har na shiga cikin kamfanin ban daina yiwa kaina tambayoyi a game da Kabir ba. Can zuciyata ta kawo min cewar na taimaka masa da kudin na da samu ko zai samu lafiya, ba karamin dadi na ji ba da wannan idea ta fado min a rai.
Ina isa office dina na tura kofar na shiga, kamar dai jiya yau ma na tarar an goge ko'ina an saka air freshener mai kamshi, jaka ta na fara dorawa a saman tebur din na kunna desktop din sannan na nufi window ma bude, tsaye na hango shi jikin windows din office dinsa hannunsa daya a aljihu dayan kuma rike da cup. Maida window nai na rufe na dawo na zauna na bude na fara duba abubuwan da suke kan teburin. Misalin 12pm Yunus yai knocked ya turo kofar ya shigo.
“Halima ko?”
“Yeah”
“Kuna da meeting yau, ba ki duba takardun ba”
“Na duba amman ban gane ba, ni? Kasan ni bana zuwa meeting”
“Idan general ne dole da ke saboda mail din kamfanin na is under your control”
“A ina ake meeting din?”
“Karma hotel, ku kadai ake jira tuni sun fara taronsu ma”
Na mike tsaye da sauri.
“To ni da wa zan je?”
“Ki dauki Laptop dinki ki samu Oga a waje, yana mota yana jiranki”
Na dan ji wani iri, da shi kuma?
“Ba ni da Laptop”
“Shi zai baki”
“Okay”
Na fada ina daukar jakata na rataya sannan na nufi kofar fita ina gaba yana baya sai duk na ji na tsawwala ba dadi namiji ya saka ka a gaba ban san mi yake kallo a bayana ba duk kuwa da kasancewar na san abayar jikina bata matse ni ba sai dai hakan be saka na natsu ba har sai na na saka shi gaba ni na koma bayansa ina tafiya.
A harabar kamfanin na samu motar Ahmad fake ina fitowa sai direban dake gaban motar ya fito ya bude min motar, abunda ba a tana min ba, kuma ban tana ganin Ahmad wani yana jan shi a mota ba sai dai shi yaja amman yau hakimce yake gidan baya ya saka suit dark blue, kallo daya na masa na dauke kaina a yau kam kyaunsa har wani tsoro ya bani ko dan ban taba ganinsa hakimce kamar haka bane? Ko kuwa dan ban tana ganinsa da kalar tufafin bane oho, sai kamshin turare yake.
“Ina kwana...”
Ya furta min so calmly kamar ba shi ba, ganin cewar ni ban gaishe shi ba, wata kalar kunya naji sai kaina yai girma kamar dutsen dala.
“Ina kwana...”
Na mayar masa, be amsa ni ba ya maida hankalinsa gefen titi, har muka isa be kalli inda nake ba, nima kuma ban sake kallonsa ba har muka isa. Direban ya zagaya ya bude masa nikan ban jira a bude min na bude na fito daga motar mai sanyin ac wacce har ta fara saukar min da mura.
Wata yar karamar laptop direban ya miko min da pen sai wani littafi mai kamar diary, sannan dauko wata jaka wacce nake kyautata zaton ta Ahmad ce yai gaba ni da Ahmad din muka rufa masa baya, kana ganin kofar shiga dakin taron kasan taro ne na manyan mutane, domin an zuba securities a gurin gwanin sha'awa. Na yi zato ko sai mun yi musu wata magana ko nuna wani abun sannan su bar mu shiga ga mamaki ne sai kawai na ga an bude mana kofa, daf da zamu shiga cikin gurin Ahmad ya risuno saitin kunnena ya rada min.
“Ki kashe wayarki”
“Ban gane ba zuwa kikai kika fallasa kanka abayyanar jama'a”
“Aa....”
Daya bayan daya na bayyana masa yadda abun ya faru har da zancen siyen tikitin da Abraham yai, hakan kuma ba karamin bata masa rai yayi ba.
“Wayuya kawai taya shi Abraham din zai siya miki ticket kuma ki karba ki je”
“To ba gashi na ci gasar ba”
“Dalla can Sakarya kawai”
Ya kashe wayarsa, a iya tunanina nikam ban ga illar zuwa bukin da nai ba, to ina ruwana da shi ai ba san shi na je ba, dan yarana. Ko da na fito dakin dukansu suna zaune a tsakar gida har Mama sai zancen Aminu suke, kusa da Inna na zauna ina sauraren Mama da ke fadin.
“Namiji dai ba shi da kunya, yanzu duk abubuwan nan da Aminu yai miki har yana iya murje ido yai miki siyayya ya kawo miki yana rokon ki koma masa?ya manta irin cin mutuncin da yai miki ne ko kuwa ya runtse ido ne ya zo?”
“Hmmm Mama ke ma dai kya fada, ni wallahi yanzu ko mai sunansa bana son ji sai na rika ganin kamar ma halinsu daya”
Na Fada ina tabe baki,Sai Inna tai dariya tace.
“Kuma kin ga fa inda rabon shiryarwa sai a shirya tun da akwai yaya har hudu, ai ko aure kika yi a wani wajen hankalinki yana kansu, nikam da za ki bi ta tawa da kin koma masa tun dai ya gyara halinsa kuma mahaifiyarsa ma yanzu tana sonki”
Mama ta tari numfashin Inna tana girgiza kai.
“A a wahalar da ta sha ta isa haka nan, ai ba ayi rai dan wani rai ba, wani lokacin mai hali baya fasa halinsa, Allah dai ya baki wani na kwarai wanda zai so ki tsakani da Allah, wanda zai kaunace ki har karshen rayuwarki, ya zame miki gata hawayen da kika zubar ya share miki su, kuma ya so yayanki kamar nasa, wanda zai rika jin tausayinki yana tsoron cutar da ke”
Dan murmushi nai.
“Samun irin wannan namiji yana da wahala Mama, mutum daya na san zai iya min haka, shi kuma babu wannan damar a yanzu, nikam na yanke kauna daga yin aure a yanzu”
“Haba dai fata na gari lamiri, idan ba ki yi aure ba ki yi me? Aure ya haife ki kuma ya haifa miki yaya, ina kan fatana na ganki a dakin mijinki”
Aisha da Hafiza da Husna kamar jira suke suka hau yi mata yaya, ba ma kamar Hafiza sarkin Baki.
“Mu da ba a kauna ai sai a kai ku kofar gida a aje, wai har wani fata ake mata ga ku zaune, ita ba kara ita ba tayi auren har ta haifi amsu yi mata addu'a, mu da ko mashinshinin ba mu da fa?”
Duk dariya muka saka har ita, sannan su ma tai musu addu'ar. Sai a lokacin na dauko siyayar da Aminu yai min na bude ina dubawa, Atamfa ce har biyu da turare da sabulun wanka da wanki sai yan kayan tande tande, komai ban dauka a gurin na rabawa Mama da Inna atamfar salubun wanka da wanki kuma na bawa kanena turaren na bawa Baba, sauran kayan tande tande kuma a nan na bar su a tsakaninsu suka raba suka cinye.
Ina zaune a gurin amman ko chocolate din ban ci ba, sai aikin danna wayata nake.
“Gobe idan Allah ya kaimu ina son zuwa gidan Gwaggo Ramatu”
Mama ta fada.
“Gaskiya kam kin kwana biyu ba ki leka ta ga, gata ita kadai ta rage muku cikin Gwaggonin”
Na fada still idona yana kan wayata.
“Shiyasa ai nake son zuwa, sai na siya mata salubu na kai mata”
Da gangan na kalli Hafiza na ce
“Ga sabulun Hafiza nan ta baki ki kai mata”
Wata uwar harara ta watsa min.
“Eh ni da ba kya kauna, to ba zan bayar ba, kuma Mama dakinki zan aje shi idan ma ban ganshi ba ba ruwana ni”
Ta fada tana tashi ta bar mana gurin.
“To idan ba ruwanki ai ba ruwan kowa”
Na fada ina dariya Inna ma dariya take, haka ma Mama daman sun san Hafiza bata da na biyu a cikin gidan indai babin fada ne da matsifa, sai dai fa akwai son yan'uwanta kamar ranta, hakan yasa baka iya banbanta ni da ita kace kowa da uwarsa, mu zama kamar uwa daya daman kuma uban ne ya hada.
Washe gari ta kama friday farar rana kuma kuraren lokaci, hakan yasa na gama shiryawa su Amal da wuri suka wuce makaranta ni kuma na shirya a yau ma abayar na saka sai dai wannan maroon color ce, sai da nai musu sallama sannan na nufi gurin aikina.
Tun daga lokacin dana fito gida nake saka ran haduwa da Abraham saboda sabon da yai min na bibiya a baya wani lokaci amman har na isa ban ganshi ba, a yau ma ban ga Kabir ba, hankali ya dan tashi daman na san Ahmad ba zai kyale shi ba bayan abunda ya faru, to amman ina ya kai shi? A wane hali yake? Har na shiga cikin kamfanin ban daina yiwa kaina tambayoyi a game da Kabir ba. Can zuciyata ta kawo min cewar na taimaka masa da kudin na da samu ko zai samu lafiya, ba karamin dadi na ji ba da wannan idea ta fado min a rai.
Ina isa office dina na tura kofar na shiga, kamar dai jiya yau ma na tarar an goge ko'ina an saka air freshener mai kamshi, jaka ta na fara dorawa a saman tebur din na kunna desktop din sannan na nufi window ma bude, tsaye na hango shi jikin windows din office dinsa hannunsa daya a aljihu dayan kuma rike da cup. Maida window nai na rufe na dawo na zauna na bude na fara duba abubuwan da suke kan teburin. Misalin 12pm Yunus yai knocked ya turo kofar ya shigo.
“Halima ko?”
“Yeah”
“Kuna da meeting yau, ba ki duba takardun ba”
“Na duba amman ban gane ba, ni? Kasan ni bana zuwa meeting”
“Idan general ne dole da ke saboda mail din kamfanin na is under your control”
“A ina ake meeting din?”
“Karma hotel, ku kadai ake jira tuni sun fara taronsu ma”
Na mike tsaye da sauri.
“To ni da wa zan je?”
“Ki dauki Laptop dinki ki samu Oga a waje, yana mota yana jiranki”
Na dan ji wani iri, da shi kuma?
“Ba ni da Laptop”
“Shi zai baki”
“Okay”
Na fada ina daukar jakata na rataya sannan na nufi kofar fita ina gaba yana baya sai duk na ji na tsawwala ba dadi namiji ya saka ka a gaba ban san mi yake kallo a bayana ba duk kuwa da kasancewar na san abayar jikina bata matse ni ba sai dai hakan be saka na natsu ba har sai na na saka shi gaba ni na koma bayansa ina tafiya.
A harabar kamfanin na samu motar Ahmad fake ina fitowa sai direban dake gaban motar ya fito ya bude min motar, abunda ba a tana min ba, kuma ban tana ganin Ahmad wani yana jan shi a mota ba sai dai shi yaja amman yau hakimce yake gidan baya ya saka suit dark blue, kallo daya na masa na dauke kaina a yau kam kyaunsa har wani tsoro ya bani ko dan ban taba ganinsa hakimce kamar haka bane? Ko kuwa dan ban tana ganinsa da kalar tufafin bane oho, sai kamshin turare yake.
“Ina kwana...”
Ya furta min so calmly kamar ba shi ba, ganin cewar ni ban gaishe shi ba, wata kalar kunya naji sai kaina yai girma kamar dutsen dala.
“Ina kwana...”
Na mayar masa, be amsa ni ba ya maida hankalinsa gefen titi, har muka isa be kalli inda nake ba, nima kuma ban sake kallonsa ba har muka isa. Direban ya zagaya ya bude masa nikan ban jira a bude min na bude na fito daga motar mai sanyin ac wacce har ta fara saukar min da mura.
Wata yar karamar laptop direban ya miko min da pen sai wani littafi mai kamar diary, sannan dauko wata jaka wacce nake kyautata zaton ta Ahmad ce yai gaba ni da Ahmad din muka rufa masa baya, kana ganin kofar shiga dakin taron kasan taro ne na manyan mutane, domin an zuba securities a gurin gwanin sha'awa. Na yi zato ko sai mun yi musu wata magana ko nuna wani abun sannan su bar mu shiga ga mamaki ne sai kawai na ga an bude mana kofa, daf da zamu shiga cikin gurin Ahmad ya risuno saitin kunnena ya rada min.
“Ki kashe wayarki”