Sashe 51
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hajiya ba ta yarda ba har sai da ta saka aka yi mata na ta bincike, a gurin malamanta da kuma malaman kawayenta, sai dai duk inda take abu daya ake fada mata cewar arzikin danta hana tare da matar da ya rabu da ita, wasu ma har kara rura wutar abun suke ana fada mata cewar da ace be sake ta ba da yana daf da samun wani abun. Sai dai hakan be gamsar da ita ba har sai da ta sake saka kawarta Hajiya Mairo a gaba suka tafi gurin wani malamin. Ba su tsaya bin layi ba abun ka da masu kudi, sai aka bi da su ta wata hanyar suka shiga cikin dakin malamin. After sun gaisa ya dauko kasa ya fara bincike domin shi haka yake ba ya bari mutum ya fada masa dalilin zuwansa, sai dai shi ya fada maka abunda ya kawo ka. Yayi kusan minti ashirin yana duba kasar sannan ya dago ya kalli Hajiya Mairo.
“Waye Aminu? Gashi nan yau sun nuna min da Maganarsa kuka zo”
“Tabbas hakika maganar Aminu ta kawo mu, yaron abokiyata ne kuma aminiyata”
Ya gyada kai sannan ya kalli Hajiyar Zuwaira wato mahaifiyar Aminu ya ce.
“Sun fada min komai, dan ki na fama da gurguncewar cigaban rayuwa haka ne?”
Tai saurin gyada kai.
“Haka ne”
“To ai danki ya baro kyau tun ranar haihuwa, ga shi dauke da kwaryar alheri sai kuma ya bari ta fadi ta fashe”
Hajiya Zuwaira ta yi masa kallon rashin fahimta. Sai yai yar dariya ya gyara zamansa.
“Na san baki fahimta ba, wato tauraruwar danki sakaina'u ce, irin wannan tauraruwar bata iya haske har sai ta hadu da yar'uwarta mai iya daukar nauyinta, ma'ana mai taimaka mata ta haskaka, da danki zai hadu da taurari dubu idan be hadu da wannan tauraruwar ba gasri to abu ne mai wahala ya iya haskaka ya daukaka yadda yake so, daman ko wane dan'adam yana da tauraruwarsa to ita ta danki haka take”
“To amman Malam.... ”
Sai ya daga mata hannu.
“Wacece Halima?”
“Matar da ya saki ce ita ce uwargidansa”
“To ita ce mai wannan tauraruwar gasri, tauraruwa ce mai tsananin haske da kaifi gaske, tana haska ko wane irin tauraruwa, ban ce dan ki ba zai arziki ba, amman da ace yana tare da ita ina mai tabbatar miki ko matar gobna bata ita ta nuna miki yatsa ba”
“Amman Malam ai can baya tare da ita kuma yana al'amuranshi”
“Amman ya kai kamar haka?”
Ta girgiza kai alamar a'a.
“To kin gani, zai iya samun mai irin tauraruwar amman abun ne mai wahalar gaske”
Hajiya Mairo ta ce.
“To amman Malam dole sai Aminu ne kawai idan ya aureta zai yi arziki ko kuwa idan wani ya aureta shi ma zai iya yin arzikin?”
“Sosai kuwa ai kowa ta raba zai yi arziki, ita daman haka tauraruwar take”
Cikin damuwa Hajiya Zuwaira ta ce
“Yanzu babu yadda za'ayi tauraruwar tasa tai haske? Kenan dole sai da ita?”
“Akwai mana, amman aiki ne mai wahalar gaske kuma za a ci kudi”
“Karka damu indai har za a samu biyan bukata ba matsala”
“Za ki siye sa daya, da fararen balbelu uku sai fafaren kaji bakwai, sannan za a biya masu aiki 30k”
Murmushi Hajiya tai.
“Wannan ai ba wata matsala ba ce, sai dai ba zan iya siyowa ba zan dai bada kudin sai ka siyo komai da kanka, sai dai ba ka fada mana nawa za a biya ka”
“Ni sai bukata ta biya sannan za a biyani”
A take a gurin ya lissafa mata kusan dubu dari biyu da za a bada na kayan aiki, sai ta karbi account dinsa da zimmar idan ta koma gida zata turo masa, bata bar gurin ba sai da ta aje masa 10k na shan ruwa. Har suka dawo ita da Hajiya Mairo ba su daina mamaki da jinjina lamarin ba.
Ba ma kamar Hajiya Mairo domin ita nata tunanin dabam.
ABDALLAH POV.
Tun daga lokacin da suka samu matsala da Suwaiba ta canja masa, ya lura da hakan a dabi'unta da halayyarta da kuma yadda take mu'amalantarsa a yanzu.
Shi kau iya kokarin da yake na ya fahimtar da ita ne ta daina ganin laifinsa ko kishin Halimatu, a iya ganinsa shi be ga dalilin wannan kishin da take ba, be san abunda zai saka ta ji haushi dan yayi ma yar'uwarsa alheri ba, tun da ita ma babu abunda ya rageta duk wani abu da take bukata yana yi ma kuma yai ma yan'uwanta, sai dai duk bata ga na kowa ba sai na Halimatu. Duk yadda take kokarin avoiding dinsa shi kuma kara shige mata yake yana nuna kamar wani abu na bacin rai be taba shiga tsakaninsu, daman can haka yake idan yai fada da ita kokarin mantawa yake saboda kullum auna tunaninta yake yana ganin be kai na shi ba, a ganinsa mace mai rauni ce kuma ba komai suke iya tsayawa su yi tunani ba, duk yadda abu ya zo musu haka suke karbarsa shiyasa shaidan yake yin galaba akansu. Idan har ya ce zai rike ta a ransa zata iya shiga matsala, matukar ya rike bacin ran mutun a zuciyarsa sai wani abun ya faru da mutun domin yana da kofi, idan har ka bata masa rai za ka ga daidai ba, shi kansa har mamakin kansa yake wani lokacin abu yake kamar wani maye.
sai da yai shirin office saf sannan ya nufi dakin matarsa yana kamshi turare mai dadi. Yana shigowa ta wani dauke kai be damu ba ya karasa kusa da ita ya kama hannunta ya sumbata.
“Zan tafi office sai na dawo”
Bata ce masa koma ba, shi ma kuma be jira ya ji wani abu daga gurinta ba, daman be yi tsammanin ta fada masa wani abun ba ko da Allah ya tsare ne ba tun da fushi take da shi, ba kamar da ba da har bakin mota take rakoshi. Daga gidanshi gidan Hajiya ya nufa as usual daman sai ya biya ya gaisheta yake wucewa office, ko a dawowa ma idam time be kure masa ba sai yayi mata sallama yake dawowa gida. Ya dauki Hajiya kamar wata abokiyasa yana jindadin fira da ita sosai duk wano sirri na shi ko shawara ita ce, kamar yadda ita ma ta fi shakuwa da shi fiye da Abdulhamid.
Ba kasafai Abdulhamid yake zuwa da safe gaishe da Hajiya ba, wani lokacin sai da rana ko dare, wani lokacin ma sai ya wuni be shigo ba sai dai yai mata waya. A kujerar da mahaifiyarsa take zaune ya zauna yana mika mata gaisuwa.
“Lafiya Kalau ya aka tashi ya yaran”
Ta amsa masa fuskarta da alamun magana.
“Abdulhamid”
Daman haka yake masa he can't say Abdulhamid ina kwana saboda yana jin age mate dinsa ne, tun da yake a rayuwarsa be taba bude baki yace wa Abdulhamid ina kwana ko ina wuni ba, sai dai ya kira sunansa.
“Likita ykk”
“Lafiya kalau”
Ya amsa yana kallon yanayin Hajiya da kuma shi kansa Abdulhamid din.
“Lafiya wai?”
“Lafiya kalau wai Halimatu ce tace ta gaji da zama da shi saki take so.... ”
Ji yai kamar an zuba masa ruwan sayi a kai a take tsigar jikinsa ta tashi.
“Saki?”
“Eh”
Hajiya ta amsa masa.
“Why?”
Abdulhamid ya daga kafadunsa alamar be san dalili ba.
“No dole akwai wani abu, akwa abunda kai wa yarinyar nan Abdulhamid haka nan kawai Halimatu ba zata ce ka sake ta ba, i know who's her”
Hajiya ta tabe baki tana fadin.
“Ni nace dai ko ta gaji da zama da kai haka nan ne ba”
“No bana tunanin haka duk dai na san matsalar ce tai haifar da komai, amman wata kila tana jin kunyar kan ta ne akan abunda ya faru”
Cewar Abdulhamid, a take Abdallah ya gyara zamansa yana girgiza masa kai.
“idan har akan matsalar ne be kamata ta saka kanta cikin damuwa ba, matar da zata bar yayanta ta bar aikinta ta yarda ta aureka bayan kuma ta san irin lalurar da kake tare da ita, be kamata dan wani abun ya same ta ka barta ta shiga damuwa ba, and she told you ba su yi raped dinta ba, miyasa ba za ku yarda da ita ba?, Abdulhamid Halimatu kamar amanace a gurinka kuma matarka ce ka zaunar da ita ta nuna mata baka da matsala da hakan kuma ta kwantar da hankalinta, Abdulhamid yarinyar nan.... ”
Be karasa ba Abdulhamid ya tari numfashinsa.
“Halima ba yarinya ba ce, yaranta hudu ta san me take yi. She told me babu wanda yai forcing dinta ta aure ni and now she want divorce”
“Ai sakin ma shi ya fi alheri”
Abdallah ya juyo ya kalleta cike da damuwa.
“No Hajiya ke kika haifar da wannan matsalar kika saka Abdulhamid ya rika ji a ransa kamar an yi raped matarsa, and now kina kokarin ki karfafa nasa guiwa ya sake ta haba Hajiya be.... ”
“No tun kamin ayi wannan abun i suspect something, and yes na kai ta an mata hiv test and the result din positive, maybe dai tana jin kunyar kanta ne.... ”
Da mugun mamaki Abdallah yake kallon dan'uwansa.
“Don't tell me you don't trust your wife...? Why all the insult bro? Taya za kai ta ayi mata hiv test? Kasan halin da za ta shiga?”
“Ba zaka fahimta ba ne Abdallah, ni na san abunda yake nan, and matar nan yanzu har shaye-shaye take fa, na ga kwalaben maye a dakinta, and wani lokacin zan tarar tana ta bachi kamar wacce ta mutu, idan ta farka idonta har canjawa yake”
Kamar an saka scissors an yanke jiyojin jikinsa haka ya ji, be taba jin tausayinta irin yanzu ba, yana jin da ace shi ne Halimatu ta fada masa cewar ba'ayi mata fyade ba babu abunda zai hana shi yarda da ita, even if an yi mata fyaden ma zai iya zama da ita a haka.
“Waye Aminu? Gashi nan yau sun nuna min da Maganarsa kuka zo”
“Tabbas hakika maganar Aminu ta kawo mu, yaron abokiyata ne kuma aminiyata”
Ya gyada kai sannan ya kalli Hajiyar Zuwaira wato mahaifiyar Aminu ya ce.
“Sun fada min komai, dan ki na fama da gurguncewar cigaban rayuwa haka ne?”
Tai saurin gyada kai.
“Haka ne”
“To ai danki ya baro kyau tun ranar haihuwa, ga shi dauke da kwaryar alheri sai kuma ya bari ta fadi ta fashe”
Hajiya Zuwaira ta yi masa kallon rashin fahimta. Sai yai yar dariya ya gyara zamansa.
“Na san baki fahimta ba, wato tauraruwar danki sakaina'u ce, irin wannan tauraruwar bata iya haske har sai ta hadu da yar'uwarta mai iya daukar nauyinta, ma'ana mai taimaka mata ta haskaka, da danki zai hadu da taurari dubu idan be hadu da wannan tauraruwar ba gasri to abu ne mai wahala ya iya haskaka ya daukaka yadda yake so, daman ko wane dan'adam yana da tauraruwarsa to ita ta danki haka take”
“To amman Malam.... ”
Sai ya daga mata hannu.
“Wacece Halima?”
“Matar da ya saki ce ita ce uwargidansa”
“To ita ce mai wannan tauraruwar gasri, tauraruwa ce mai tsananin haske da kaifi gaske, tana haska ko wane irin tauraruwa, ban ce dan ki ba zai arziki ba, amman da ace yana tare da ita ina mai tabbatar miki ko matar gobna bata ita ta nuna miki yatsa ba”
“Amman Malam ai can baya tare da ita kuma yana al'amuranshi”
“Amman ya kai kamar haka?”
Ta girgiza kai alamar a'a.
“To kin gani, zai iya samun mai irin tauraruwar amman abun ne mai wahalar gaske”
Hajiya Mairo ta ce.
“To amman Malam dole sai Aminu ne kawai idan ya aureta zai yi arziki ko kuwa idan wani ya aureta shi ma zai iya yin arzikin?”
“Sosai kuwa ai kowa ta raba zai yi arziki, ita daman haka tauraruwar take”
Cikin damuwa Hajiya Zuwaira ta ce
“Yanzu babu yadda za'ayi tauraruwar tasa tai haske? Kenan dole sai da ita?”
“Akwai mana, amman aiki ne mai wahalar gaske kuma za a ci kudi”
“Karka damu indai har za a samu biyan bukata ba matsala”
“Za ki siye sa daya, da fararen balbelu uku sai fafaren kaji bakwai, sannan za a biya masu aiki 30k”
Murmushi Hajiya tai.
“Wannan ai ba wata matsala ba ce, sai dai ba zan iya siyowa ba zan dai bada kudin sai ka siyo komai da kanka, sai dai ba ka fada mana nawa za a biya ka”
“Ni sai bukata ta biya sannan za a biyani”
A take a gurin ya lissafa mata kusan dubu dari biyu da za a bada na kayan aiki, sai ta karbi account dinsa da zimmar idan ta koma gida zata turo masa, bata bar gurin ba sai da ta aje masa 10k na shan ruwa. Har suka dawo ita da Hajiya Mairo ba su daina mamaki da jinjina lamarin ba.
Ba ma kamar Hajiya Mairo domin ita nata tunanin dabam.
ABDALLAH POV.
Tun daga lokacin da suka samu matsala da Suwaiba ta canja masa, ya lura da hakan a dabi'unta da halayyarta da kuma yadda take mu'amalantarsa a yanzu.
Shi kau iya kokarin da yake na ya fahimtar da ita ne ta daina ganin laifinsa ko kishin Halimatu, a iya ganinsa shi be ga dalilin wannan kishin da take ba, be san abunda zai saka ta ji haushi dan yayi ma yar'uwarsa alheri ba, tun da ita ma babu abunda ya rageta duk wani abu da take bukata yana yi ma kuma yai ma yan'uwanta, sai dai duk bata ga na kowa ba sai na Halimatu. Duk yadda take kokarin avoiding dinsa shi kuma kara shige mata yake yana nuna kamar wani abu na bacin rai be taba shiga tsakaninsu, daman can haka yake idan yai fada da ita kokarin mantawa yake saboda kullum auna tunaninta yake yana ganin be kai na shi ba, a ganinsa mace mai rauni ce kuma ba komai suke iya tsayawa su yi tunani ba, duk yadda abu ya zo musu haka suke karbarsa shiyasa shaidan yake yin galaba akansu. Idan har ya ce zai rike ta a ransa zata iya shiga matsala, matukar ya rike bacin ran mutun a zuciyarsa sai wani abun ya faru da mutun domin yana da kofi, idan har ka bata masa rai za ka ga daidai ba, shi kansa har mamakin kansa yake wani lokacin abu yake kamar wani maye.
sai da yai shirin office saf sannan ya nufi dakin matarsa yana kamshi turare mai dadi. Yana shigowa ta wani dauke kai be damu ba ya karasa kusa da ita ya kama hannunta ya sumbata.
“Zan tafi office sai na dawo”
Bata ce masa koma ba, shi ma kuma be jira ya ji wani abu daga gurinta ba, daman be yi tsammanin ta fada masa wani abun ba ko da Allah ya tsare ne ba tun da fushi take da shi, ba kamar da ba da har bakin mota take rakoshi. Daga gidanshi gidan Hajiya ya nufa as usual daman sai ya biya ya gaisheta yake wucewa office, ko a dawowa ma idam time be kure masa ba sai yayi mata sallama yake dawowa gida. Ya dauki Hajiya kamar wata abokiyasa yana jindadin fira da ita sosai duk wano sirri na shi ko shawara ita ce, kamar yadda ita ma ta fi shakuwa da shi fiye da Abdulhamid.
Ba kasafai Abdulhamid yake zuwa da safe gaishe da Hajiya ba, wani lokacin sai da rana ko dare, wani lokacin ma sai ya wuni be shigo ba sai dai yai mata waya. A kujerar da mahaifiyarsa take zaune ya zauna yana mika mata gaisuwa.
“Lafiya Kalau ya aka tashi ya yaran”
Ta amsa masa fuskarta da alamun magana.
“Abdulhamid”
Daman haka yake masa he can't say Abdulhamid ina kwana saboda yana jin age mate dinsa ne, tun da yake a rayuwarsa be taba bude baki yace wa Abdulhamid ina kwana ko ina wuni ba, sai dai ya kira sunansa.
“Likita ykk”
“Lafiya kalau”
Ya amsa yana kallon yanayin Hajiya da kuma shi kansa Abdulhamid din.
“Lafiya wai?”
“Lafiya kalau wai Halimatu ce tace ta gaji da zama da shi saki take so.... ”
Ji yai kamar an zuba masa ruwan sayi a kai a take tsigar jikinsa ta tashi.
“Saki?”
“Eh”
Hajiya ta amsa masa.
“Why?”
Abdulhamid ya daga kafadunsa alamar be san dalili ba.
“No dole akwai wani abu, akwa abunda kai wa yarinyar nan Abdulhamid haka nan kawai Halimatu ba zata ce ka sake ta ba, i know who's her”
Hajiya ta tabe baki tana fadin.
“Ni nace dai ko ta gaji da zama da kai haka nan ne ba”
“No bana tunanin haka duk dai na san matsalar ce tai haifar da komai, amman wata kila tana jin kunyar kan ta ne akan abunda ya faru”
Cewar Abdulhamid, a take Abdallah ya gyara zamansa yana girgiza masa kai.
“idan har akan matsalar ne be kamata ta saka kanta cikin damuwa ba, matar da zata bar yayanta ta bar aikinta ta yarda ta aureka bayan kuma ta san irin lalurar da kake tare da ita, be kamata dan wani abun ya same ta ka barta ta shiga damuwa ba, and she told you ba su yi raped dinta ba, miyasa ba za ku yarda da ita ba?, Abdulhamid Halimatu kamar amanace a gurinka kuma matarka ce ka zaunar da ita ta nuna mata baka da matsala da hakan kuma ta kwantar da hankalinta, Abdulhamid yarinyar nan.... ”
Be karasa ba Abdulhamid ya tari numfashinsa.
“Halima ba yarinya ba ce, yaranta hudu ta san me take yi. She told me babu wanda yai forcing dinta ta aure ni and now she want divorce”
“Ai sakin ma shi ya fi alheri”
Abdallah ya juyo ya kalleta cike da damuwa.
“No Hajiya ke kika haifar da wannan matsalar kika saka Abdulhamid ya rika ji a ransa kamar an yi raped matarsa, and now kina kokarin ki karfafa nasa guiwa ya sake ta haba Hajiya be.... ”
“No tun kamin ayi wannan abun i suspect something, and yes na kai ta an mata hiv test and the result din positive, maybe dai tana jin kunyar kanta ne.... ”
Da mugun mamaki Abdallah yake kallon dan'uwansa.
“Don't tell me you don't trust your wife...? Why all the insult bro? Taya za kai ta ayi mata hiv test? Kasan halin da za ta shiga?”
“Ba zaka fahimta ba ne Abdallah, ni na san abunda yake nan, and matar nan yanzu har shaye-shaye take fa, na ga kwalaben maye a dakinta, and wani lokacin zan tarar tana ta bachi kamar wacce ta mutu, idan ta farka idonta har canjawa yake”
Kamar an saka scissors an yanke jiyojin jikinsa haka ya ji, be taba jin tausayinta irin yanzu ba, yana jin da ace shi ne Halimatu ta fada masa cewar ba'ayi mata fyade ba babu abunda zai hana shi yarda da ita, even if an yi mata fyaden ma zai iya zama da ita a haka.