Sashe 71
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kamar dai ko wane kamfani shi ma wannan yana da masu gadi dake sanye da uniform mai sunan kamfanin wato Crown Company Limited. Sai dai ba su kadai ba har da Sojoji a gurin.
Sai da suka auna jikina idan bana dauke da bom sannan suka ba ni damar shiga ciki, ba ni kadai suke yi wa haka ba, har masu mota sai sun bude musu bayan mota sun duba sannan su basu damar wuce ciki.
A iya zamana garin gusau ban taba shiga cikin kamfanin ba, to me ma zai kaini tun da ba siye ko siyarwa zan yi ba, a yanzu ma dan ina neman aiki ne kamar yadda nake cewar kamfanin yana neman ma'aikata yan boko wadanda za su iya communicating da wasu mutanen amman da yalshen nasara wato turanci.
Sai dai ban san inda ake bi a shiga kamfanin ba, domin na lura da kofar kamfanin ta kasu gida uku wasu na fita da shiga a ta farkon wasu a ta biyu wasu a ta uku, tsaye nai a gurin ina ta tunanin wacce zan shiga, ta farko haka zuciyata ta raya min dan haka na nufi kofar gadan gadan, a nan ma wasu matsaran ne rike da abun awonsu kamar dai na bakin gate.
Sai dai da alama su basa barin mutum ya shiga sai idan ya nuna musu wata yar takardar wacce nake ganin kowa yana ba su su duba kamin su barshi ya shiga ciki. Hakan yasa ban karasa a gurin ba sai na juyo na nufi kofar tsakiya wacce mutane suka fi fitowa a cikin, wani abun burgewa ma kofar ita take bude kanta sai jujjuyawa take gwanin sha'awa, ina kokarin kutsa kai na shiga cikin kamfanin na Abban Baby Namra ya fito daga ciki yana sanye da shadda mai ruwan madara, ba laifi na dan saki fuskata domin har ga Allah na yi nufin gaisheshi sai kawai na ga ya hade fuska kamar bakin hadari daman can fuskar tashi ba a washe take ba, balle yanzu da ganina yasa ya kara hade ta kamar yaga mala'ikan mutuwa. Hakan kuma be hana na mika masa gaisuwa ba, amman sai yai min banza ya wuce abun shi, a take na ji duk na muzanta domin akwai mutane a kofar kuma na san wasu sun ji gaisuwar da na mika masa. Sai kuma duk na ji haushin kaina, miyasa na gaishe shi tun da farko ma? Miyasa ban kyale shi ba na yi tafiyata? Why na nuna na sanshi ma?
“Miya kawo ki nan?”
Kamar daga sama na ji tambayarsa da wata bakar murya tashi, har daka min tsawa yake kamar wata yarshi.
“Ban sani ba”
Na fada cikin tsiwa ba tare da na kalleshi ba na cigaba da tafiyata ina jin haushin kaina, na gaishe shi ne saboda ina ganin kamar akwai mutunci a tsakani ko dan abokatar da ke tsakanin Baby Namra da Namra, ko da yake daman daga ganinsa ba zai yi mutunci ba sai wani jijji da kai sai kace shi yafi kowa arziki a gari, Allah kadai ya san abunda ya kawo shi kamfani ma wata kila shi ma wata alfamar ya zo nema amman sai son nuna isa.
“Wai miya kawo ki nan”
Na fada a fili ina tsire baki har wani namijin da ke reception din ya dago ya kalleni.
“Na'am....”
Sai na dan saki fuskata nai masa murmushi.
“Sannu dai Malam daman na ji kamar ance kamfanin ku yana neman ma'aikata”
“Eh amman ba zuwa ake ba, ta email ake turo mana sako”
“Minene mail dinku?”
Ya fada min sannan na sake ce masa.
“Sai dai matsalar ban taba zuwa kamfanin ba, ban kuma san tsare tsaren kamfanin ba ban san mi kamfanin yake ba”
“Kamfanin mu yana siye da siyar da zinari tare da narkawar da kuma saffarashi ta hanyar yin abun wuya dan kulleni ko kuma wani abun na kayan ado na jiki ko na riguna”
“Na gode sosai, ta mail din zan tura cv na?”
“Yes idan sun duba suka ga kin cancanta za a kira sai ki zo”
“Na gode”
Na fada masa ina dariya.
“Your welcome.”
Tare da murmushi as respond. Ni kuma na jiyo na fito daga kamfanin, abun ka damai salo sai da nai ma security guard din sallama sannan na kama hanya, ban yi wata tafiya mai nisa ba na hango Kabir zaune a gafen hanya tufafin jikinsa sun yi datti ga surar kansa ta taru gaba daya ya soma canjawa ga wani abun datti da jikinsa yai. Karasa gurinsa nai da sauri ina kiran sunansa sai ya dago kansa da sauri ya kalleni ban san lokacin da na fashe da kuka ba. Hannu na saka a jakata na dauko dubu biyu na mika masa, be karba ba ba kuma yi min alamar zai karba ba, hakan yasa na risina na aje masa kudin na soma tafiya ina hawaye ina waigensa, har na tari napep na shiga be daina kallona ba kuma be kai hannu ya dauki kudin ba.
Gaba daya rayuwarsa ta baya sai ta dawo min sabuwa, Kabir mutum ne mai tsafta ga far'a da son mutane, musamman ni yana kula da ni yana nuna min kauna, duk kuwa da yake haramtacciyar kauna na nemana bayan yasan ina da aure.
Na fi alakanta ganin da nai a haka da rashin mahaifiya a raye domin na tabbatar da ace mahaifiyarsa tana raye ba zata bar danta a haka ba, domin ba duka yake ba balle ace ana gudunsa ba zagi yake ba, kusan sun ta haukar nan ta same shi ko magana baya yi.
Wallahi har na isa gida hawaye ba su daina zubar min ba, sai da zan fitaa napep din sannan na share hawayena na sallame shi na shiga gida, ashe wani kukan zan tarar a gidan mu, na shiga n samu hankalin kowa a tashe, ka rasa wanda zai fada min cewar Amal ta samu hatsari.
“Wai miya faru ne?”
Na tambaya ganin kowa yana ta bina da kallo.
“Amal ta samu hatsari”
Inna ta fada min muryarta a hankali.
“Ko dai ta mutu? Ku fada min?”
“Ba mutuwa tai ba tana asibiti ma”
Hafiza ta amsa min.
“Garin ya ta samu hatsarin?”
“Aisha taje daukarsu daga school sai ta tarar wai Aminu ya dauke su, sai ga kanwarsa ta zo yanzu ta fada mana wai Amal ta samu
Hatsari, so yake ya kashe miki yayan”
“Wace asibiti?”
“Wai Yarima bakura yanzu yanzu ta bar gidan”
Ko jakata ban aje ba na ja kanwata Husna muka nufi asibitin domin an fada min Mama da Aisha suna can sun tafi, haka muka shiga cikin asibitin mukai yawon duniya muka gama ba mu gane inda aka kwantar da Amal ba, daga karshe n yanke shawarar kiran Aminu a kan dole na tambaye shi, shi ma nai ta kiran wayarsa ya ki ya daga har yamma.
Ga shi daga Mama har Aisha babu mai waya balle na kira su, hankali yai mugun tashi, wata zuciyar na ce min naje gidansu Hajiyarsa na tambaya sai kuma na ji kamar ba zan iya zuwa ba, ba hatsarin Amal ne kawai ya daga min hankali ba har da rashin ganin Adnan Aiman Namra da ban yi ba domin ance suna can tare da shi.
“To ko kuma din sun samu hatsarin ne?”
“Waya sanar mishi? Mu dai kar ya kai mana uwa ya halaka”
“Wai ina ka kai min yara ne Aminu.....”
Kamar hadin baki ina rufe baki sai ga kiransa ya shigo a wayata. Da sauri na daga jikin har ba ri yake.
“Ina Amal din ina yarana...”
“Muna nan Royal Hospital tare da su”
Tsakanin akatse kiran wayar da mikewa ta tsaye bana jin ya ci dakika daya ma, cikin sauri na fita cikin gidan na isa titi na hau achaba na nufi asibiti. Sai da na sake kiransa na tambaye shi gurin sannan na karasa, a waje na samu Mama da Hajiyarsa suna zaune kamar abun arziki, Hajiyarsa na ganina ta taso ta tare ni da yar far'arta ni kam ko kula ta ban yi ba na tura dakin na shiga. Daga Aiman har Adnan da Namra da Aminu da kuma Aisha suna cikin dakin, Amal na kwance an saka mata bandeji akai sannan an saka mata wani karfe a baki an kware bakin ga halshenta da dinki.
“Miya same ta me kai mata?”
Na tambaya a tsawace ina kallonsa. Sai ya kalleni a sanyaye ya kasa ce min komai. Sai mahaifiyarsa ce ta amsa min.
“Ya dauko su daga Scul ne yana kokarin tsallaka titi da su sai wani mai Napep ya hade Amal”
“Momi kuma halshenta ya cire yanzu aka dinke mata shi..... ”
Aiman ya karasa mata, ban san lokacin da na kalli Amal ba na sake kallon Aminu ya ce.
“Kaga abunda ka ja min a gurin ya ko? Miya kaika daukar min yara?”
“Mhaifinsu ne ni Halima ki rika tunawa da wannan... ”
Ya fada ido raurau kamar zai fashe da kuka.
“Sai yanzu ka san kai mahaifinsu ne? Sai yanxu kasan su din yayanka ne?....”
“Haba Halimatu”
Mahaifiyarsa ta tari numfashinta sai yai saurin daga mata hannu.
“Barta ta fadi duk abunda take son fada Hajiya...”
Wannan karon nuna shi nai da yatsa.
“Ba fada kawai zan yi ba, gargadin ka zan yi akan yarana? Karka sake kula su ko kallonsu karka sake yi balle har ka dauke zuwa wani gurin karka sake nuna hada jini da ni...”
“Ba zan yi abunda zai jefasu a matsala ba, abunda ya faru kaddara ce wacce ko wane dan'adam be isa ya wuce ta ba, kuma ina son ki rika tunawa cewar har gobe ni mijinki ne domin akwai yaya a tsakanin mu kuma ba a san abunda gaba zata haifar ba..... ”
Sai da suka auna jikina idan bana dauke da bom sannan suka ba ni damar shiga ciki, ba ni kadai suke yi wa haka ba, har masu mota sai sun bude musu bayan mota sun duba sannan su basu damar wuce ciki.
A iya zamana garin gusau ban taba shiga cikin kamfanin ba, to me ma zai kaini tun da ba siye ko siyarwa zan yi ba, a yanzu ma dan ina neman aiki ne kamar yadda nake cewar kamfanin yana neman ma'aikata yan boko wadanda za su iya communicating da wasu mutanen amman da yalshen nasara wato turanci.
Sai dai ban san inda ake bi a shiga kamfanin ba, domin na lura da kofar kamfanin ta kasu gida uku wasu na fita da shiga a ta farkon wasu a ta biyu wasu a ta uku, tsaye nai a gurin ina ta tunanin wacce zan shiga, ta farko haka zuciyata ta raya min dan haka na nufi kofar gadan gadan, a nan ma wasu matsaran ne rike da abun awonsu kamar dai na bakin gate.
Sai dai da alama su basa barin mutum ya shiga sai idan ya nuna musu wata yar takardar wacce nake ganin kowa yana ba su su duba kamin su barshi ya shiga ciki. Hakan yasa ban karasa a gurin ba sai na juyo na nufi kofar tsakiya wacce mutane suka fi fitowa a cikin, wani abun burgewa ma kofar ita take bude kanta sai jujjuyawa take gwanin sha'awa, ina kokarin kutsa kai na shiga cikin kamfanin na Abban Baby Namra ya fito daga ciki yana sanye da shadda mai ruwan madara, ba laifi na dan saki fuskata domin har ga Allah na yi nufin gaisheshi sai kawai na ga ya hade fuska kamar bakin hadari daman can fuskar tashi ba a washe take ba, balle yanzu da ganina yasa ya kara hade ta kamar yaga mala'ikan mutuwa. Hakan kuma be hana na mika masa gaisuwa ba, amman sai yai min banza ya wuce abun shi, a take na ji duk na muzanta domin akwai mutane a kofar kuma na san wasu sun ji gaisuwar da na mika masa. Sai kuma duk na ji haushin kaina, miyasa na gaishe shi tun da farko ma? Miyasa ban kyale shi ba na yi tafiyata? Why na nuna na sanshi ma?
“Miya kawo ki nan?”
Kamar daga sama na ji tambayarsa da wata bakar murya tashi, har daka min tsawa yake kamar wata yarshi.
“Ban sani ba”
Na fada cikin tsiwa ba tare da na kalleshi ba na cigaba da tafiyata ina jin haushin kaina, na gaishe shi ne saboda ina ganin kamar akwai mutunci a tsakani ko dan abokatar da ke tsakanin Baby Namra da Namra, ko da yake daman daga ganinsa ba zai yi mutunci ba sai wani jijji da kai sai kace shi yafi kowa arziki a gari, Allah kadai ya san abunda ya kawo shi kamfani ma wata kila shi ma wata alfamar ya zo nema amman sai son nuna isa.
“Wai miya kawo ki nan”
Na fada a fili ina tsire baki har wani namijin da ke reception din ya dago ya kalleni.
“Na'am....”
Sai na dan saki fuskata nai masa murmushi.
“Sannu dai Malam daman na ji kamar ance kamfanin ku yana neman ma'aikata”
“Eh amman ba zuwa ake ba, ta email ake turo mana sako”
“Minene mail dinku?”
Ya fada min sannan na sake ce masa.
“Sai dai matsalar ban taba zuwa kamfanin ba, ban kuma san tsare tsaren kamfanin ba ban san mi kamfanin yake ba”
“Kamfanin mu yana siye da siyar da zinari tare da narkawar da kuma saffarashi ta hanyar yin abun wuya dan kulleni ko kuma wani abun na kayan ado na jiki ko na riguna”
“Na gode sosai, ta mail din zan tura cv na?”
“Yes idan sun duba suka ga kin cancanta za a kira sai ki zo”
“Na gode”
Na fada masa ina dariya.
“Your welcome.”
Tare da murmushi as respond. Ni kuma na jiyo na fito daga kamfanin, abun ka damai salo sai da nai ma security guard din sallama sannan na kama hanya, ban yi wata tafiya mai nisa ba na hango Kabir zaune a gafen hanya tufafin jikinsa sun yi datti ga surar kansa ta taru gaba daya ya soma canjawa ga wani abun datti da jikinsa yai. Karasa gurinsa nai da sauri ina kiran sunansa sai ya dago kansa da sauri ya kalleni ban san lokacin da na fashe da kuka ba. Hannu na saka a jakata na dauko dubu biyu na mika masa, be karba ba ba kuma yi min alamar zai karba ba, hakan yasa na risina na aje masa kudin na soma tafiya ina hawaye ina waigensa, har na tari napep na shiga be daina kallona ba kuma be kai hannu ya dauki kudin ba.
Gaba daya rayuwarsa ta baya sai ta dawo min sabuwa, Kabir mutum ne mai tsafta ga far'a da son mutane, musamman ni yana kula da ni yana nuna min kauna, duk kuwa da yake haramtacciyar kauna na nemana bayan yasan ina da aure.
Na fi alakanta ganin da nai a haka da rashin mahaifiya a raye domin na tabbatar da ace mahaifiyarsa tana raye ba zata bar danta a haka ba, domin ba duka yake ba balle ace ana gudunsa ba zagi yake ba, kusan sun ta haukar nan ta same shi ko magana baya yi.
Wallahi har na isa gida hawaye ba su daina zubar min ba, sai da zan fitaa napep din sannan na share hawayena na sallame shi na shiga gida, ashe wani kukan zan tarar a gidan mu, na shiga n samu hankalin kowa a tashe, ka rasa wanda zai fada min cewar Amal ta samu hatsari.
“Wai miya faru ne?”
Na tambaya ganin kowa yana ta bina da kallo.
“Amal ta samu hatsari”
Inna ta fada min muryarta a hankali.
“Ko dai ta mutu? Ku fada min?”
“Ba mutuwa tai ba tana asibiti ma”
Hafiza ta amsa min.
“Garin ya ta samu hatsarin?”
“Aisha taje daukarsu daga school sai ta tarar wai Aminu ya dauke su, sai ga kanwarsa ta zo yanzu ta fada mana wai Amal ta samu
Hatsari, so yake ya kashe miki yayan”
“Wace asibiti?”
“Wai Yarima bakura yanzu yanzu ta bar gidan”
Ko jakata ban aje ba na ja kanwata Husna muka nufi asibitin domin an fada min Mama da Aisha suna can sun tafi, haka muka shiga cikin asibitin mukai yawon duniya muka gama ba mu gane inda aka kwantar da Amal ba, daga karshe n yanke shawarar kiran Aminu a kan dole na tambaye shi, shi ma nai ta kiran wayarsa ya ki ya daga har yamma.
Ga shi daga Mama har Aisha babu mai waya balle na kira su, hankali yai mugun tashi, wata zuciyar na ce min naje gidansu Hajiyarsa na tambaya sai kuma na ji kamar ba zan iya zuwa ba, ba hatsarin Amal ne kawai ya daga min hankali ba har da rashin ganin Adnan Aiman Namra da ban yi ba domin ance suna can tare da shi.
“To ko kuma din sun samu hatsarin ne?”
“Waya sanar mishi? Mu dai kar ya kai mana uwa ya halaka”
“Wai ina ka kai min yara ne Aminu.....”
Kamar hadin baki ina rufe baki sai ga kiransa ya shigo a wayata. Da sauri na daga jikin har ba ri yake.
“Ina Amal din ina yarana...”
“Muna nan Royal Hospital tare da su”
Tsakanin akatse kiran wayar da mikewa ta tsaye bana jin ya ci dakika daya ma, cikin sauri na fita cikin gidan na isa titi na hau achaba na nufi asibiti. Sai da na sake kiransa na tambaye shi gurin sannan na karasa, a waje na samu Mama da Hajiyarsa suna zaune kamar abun arziki, Hajiyarsa na ganina ta taso ta tare ni da yar far'arta ni kam ko kula ta ban yi ba na tura dakin na shiga. Daga Aiman har Adnan da Namra da Aminu da kuma Aisha suna cikin dakin, Amal na kwance an saka mata bandeji akai sannan an saka mata wani karfe a baki an kware bakin ga halshenta da dinki.
“Miya same ta me kai mata?”
Na tambaya a tsawace ina kallonsa. Sai ya kalleni a sanyaye ya kasa ce min komai. Sai mahaifiyarsa ce ta amsa min.
“Ya dauko su daga Scul ne yana kokarin tsallaka titi da su sai wani mai Napep ya hade Amal”
“Momi kuma halshenta ya cire yanzu aka dinke mata shi..... ”
Aiman ya karasa mata, ban san lokacin da na kalli Amal ba na sake kallon Aminu ya ce.
“Kaga abunda ka ja min a gurin ya ko? Miya kaika daukar min yara?”
“Mhaifinsu ne ni Halima ki rika tunawa da wannan... ”
Ya fada ido raurau kamar zai fashe da kuka.
“Sai yanzu ka san kai mahaifinsu ne? Sai yanxu kasan su din yayanka ne?....”
“Haba Halimatu”
Mahaifiyarsa ta tari numfashinta sai yai saurin daga mata hannu.
“Barta ta fadi duk abunda take son fada Hajiya...”
Wannan karon nuna shi nai da yatsa.
“Ba fada kawai zan yi ba, gargadin ka zan yi akan yarana? Karka sake kula su ko kallonsu karka sake yi balle har ka dauke zuwa wani gurin karka sake nuna hada jini da ni...”
“Ba zan yi abunda zai jefasu a matsala ba, abunda ya faru kaddara ce wacce ko wane dan'adam be isa ya wuce ta ba, kuma ina son ki rika tunawa cewar har gobe ni mijinki ne domin akwai yaya a tsakanin mu kuma ba a san abunda gaba zata haifar ba..... ”