Sashe 101
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kamar ko yaushe yau ma na shirya shirin zuwa aikina, cikin bakar abaya kusan abaya tafi yawa a cikin tufafi domin ina jin sakewa sosai idan na saka ta gashi babu ruwanka da wani rike hijab ko gyara gyale.
Ban yi kwalliya ba, hoda ce kawai na shafa bayan mai sai dan turaren da na saka, sannan na shafa dan mai a bakina na dauki bakar jakata na rayata na nufi dakin Mama nai mata sallama, a tsakar gida na samu Inna ita mai mata sai na dawo na kama hanyar zuwa office din rai na fes.
Na samu napep daf da kofar gidanmu ya sauke wasu sai kawai na tsayar da shi na fada masa inda zai kai ni sannan na shiga.
Misalin tara da yan mintuna na isa office din, ko da na shiga na samu komai tsaf kamar kullum, wato masu gyara office din sun gyara shi sai kamshi yake. Jaka na aje a inda na saba ajewa na nufi window ya bude abun mamaki yau Ahmad ya shigo da wuri na hango shi jikin windows sa tsaye hannunsa daya rike da mug dayan kuma a aljihunsa har yana dago min mai kofin alamar gaisuwa. Ni kuma na daga masa hannu ina murmushi sannan na juyo na zauna a kujera na fara aikina.
Knocked akai kamin na ce komai Yunus ya turo kofar office din ya shigo.
“Good morning”
“Morning how are you sir”
“Fine, hope dai baki gaji da ni ba”
Ya fada yana murmushi kamar yadda nima nake mayar masa da murmushin.
“No haba dai Bismillah”
Na fada ina nuna masa gurin da system din take. Yau kusan kwana biyu kenan a office dina yake aikinsa saboda system din da ke office dinsa ta samu matsala kamar yadda ya fada min.
“Yau ma dai kin yi kyau kamar jiya, wai kiye sirrin”
Ya fada yana nufar gurin da System din take yana aje kayan dake hannunsa. Ni kuma sai nai dariya mai sauti.
“Na gode, sirrin aikin kamfaninku ne ka san yana karawa ma'aikatanku kyau da natsuwa”
He was laughing so hard kamar na fadi masa wani abun dariya sosai.
“Oh wow okay zan fadawa mutanen kamfaninku haka kuwa, so that kowa ya rike aikinsa da kyau kar yai laifin da zai saka a koreshi”
Nima dariyar nai.
“Gaskiya ya kamata kam, ko ma an koresu ku makale kar su je”
“Hahaha Haima kenan”
Ya fada yana cigaba da dariyar, wani abu na ji marar dadi ya ratsa zuciyata sakamakon kirana da yai da sunan da Abdulhamid ke kirana da shi. ban sake cewa komai ba na cigaba da aikina, sai jin nai wayata ta yi kara alamar sako, a zato na mtn ne hakan yasa na share wayar ban duba.
“I think this week zan je Abuja In-Sha-Allah”
Na kalleshi.
“Gurin me?”
“Wani aiki ne, kin san can din ma muna da branch, so idan mai gida be je ba dole ni zan je”
“Okay kace zaka leka garin manya kenan”
Dariya yai.
“Kin tana zuwa Abuja?”
“No ni ai ban taba wuce Gusau ba”
“Oh duk wayewar nan taki? Ya kamata ace kin zagaya manyan birane ai”
“To ai ban san kowa ba, kaga ko ai ba zan tashi naje garin da ba dangi ba na zauna”
“Ba dole sai kana da dangi zaka ziyarci gari ba, idan kina da friends ko ma a karan kanki zaki iya zuwa ki huta”
“Hm da dai ace ni namiji ce zanje amman ina mace ai be kamata ba”
“Believe me akwai matan da suke zuwa garin da ba su san kowa ba, wasu idan za su yi birthday haka ko suje bikin friends dinsu”
“Tab ni kam ba zan iya ba, na je garin da ban san kowa ba? Amman masu zuwa birthday a wani garin basa celebration ko? Dan na san ba za su samu masu binsu ba”
“Irin yaran manya haka, ko manyan mata wasu ma ba su tsayawa kansu ba, so suna zuwa da friends dinsu sai a hadu can ayi ta abubuwa wasu har kasar suke bari fa, kuma kin san ba kowa ke celebration din birthday ba, like me ni ma bana bikin birthday amman a ranar zan ci na sha na yi duk abunda na so”
“Nima haka nake yi gaskiya, ban tana bikin birthday ba, ko cake ban tana ci a ranar birthday na ba sai dai na gode Allah nai saka a status shikenan”
“Ni ina ciye ciye gaskiya, kuma zan iya ma mutane abu albarka birthday na, my is 22 December”
“Mine is 4 October”
Ya kalleni.
“O really? That's mean gobe kike birthday kenan?”
Na yi dariya ina gyada masa kai.
“Wow ki ce ke princess ce kenan”
Dariya na sake yi, a raina ina fadin princess sai kace wata yarinya. Wayata ce tai ringing sai da na dauke kaina daga computer sannan na kai hannuna na dauko wayar ganin bakuwar ce yasa ban damu na dauka ba sai kawai na aje wayar a saman tana ringing.
“Ah gaskiya ya kamata ki yi mana celebration”
“Haba wannan kuma ai sai yara”
Na fada ina kallon number kiranta ya sake shigowa. Hannuna kai na dauka na danna picking nakara a kunne.
“Hello Sallamu alaikum”
“Zo office dina yanzu nan”
Yana fadar hakan ya kashe wayar, ko ba a fada min ba na san mai murya, kuma na san duk a kamfanin nan shi kadai ne zai kira haka kai tsaye ya bani umarni, duk da be taba ba, be ma taba kiran wayata ba, and the way da yai maganar kamar yana cikin fushi. Hakan yasa na dan tsorata, a take na fara tunanin abunda nai wanda ba daidai tsakanin jiya zuwa yau, domin hausawa na cewa karka ji tsoron kira ka ji tsoron laifin da kai, but if i can remember ai dazun da na shigo mun gaisa da shi idan fushi yake da ni ba zai daga min hannu ba, oh maybe wani abun nai ba daidai ba, a take na fara duba sakkwanin mail din wai ko akwai wanda ya kamata na aika masa kuma ban aika ba.
“Ko a kamfanin nan ne ya kamata ki yi mana celebration”
Yunus ya fada yana danna computer dake gabansa yana murmushi, nima murmushin nai na mike tsaye rike da wayata da sai a lokacin na ke ganin sakon da ya turo min.
“Same ni office yanzu”
Oh ashe ba mtn ba ne kenan dazun, na fada a raina sannan na nufi kofar fita ina fadin.
“Ina zuwa Sir”
“Okay”
Ya amsa hankalinsa na gurin abunda yake, cikin faduwar gaba da fargaba na nufi office din kuwa da nasan ban yi wani abun ba, kuma a yadda nake da shi a yanzu bana tunanin akwai wata matsala a tsakaninku, sai muryarsa ta tabbatar min da ba lafiya ba.
Na tura office din na farko na shiga har na gaisa da mutumen dake ciki, haka a na biyu har na kai a nasa office din na tura na shiga bayan na yi knocked.
Ina shiga ya watsa min wata uwar harara, har sai da gabana ya fadi.
“Sai yanzu kika ga damar zuwa?”
“Ban ga sakon ba ne sai yanzu, ina zaki gan shi hankalinki yana can wani guri, me Yunus yake yi a office dinki?”
“Aiki”
“Shi office dinsa kwantarsa ake a ciki?”
“System dinsa ce ta lalace”
“Kuma ba zai iya magana a gyara ba, sai dai ya zo office dinki ya zauna shi tsohon dan iska, ke kuma kin saki jiki sai dariya kike kin kebe da shi kamar wani muharraminki”
The way da yai maganar sai naga kamar ba shi ba, to miye laifi dan Yunus ya zauna a a office dina? Naga dai idan wani abu zamu aikata ai ba za mu bar windows a bude ba, kuma yana maganar Yunus din ba muharramina ba ne shi din muharramina ne da na kebe da shi a nan? I was so so confused.
“Zauna nan”
Ya nuna min kujera, na yi zaton wani abun zan masa dan haka na nufi kujerar na zauna.
“Look at you kuna da exchanging words, mi kuke cewa”
Kallon mamaki nai masa.
“Magana kawai muke”
“Mi yace miki?”
Na yi shiru ina ta tunanin ta inda zan fara, ni kam yaushe rabon da ayi min haka wai a tsareni ana son na fadi wani abu da na fada ko kuma wani ya fada min.
“Maganar zuwa Abuja ne da yai min, sai maganar Birthday, sai.... At first dai cewa yai na yi kyau sai..... Maganganu dai haka... ”
Sama sama na tsakuro abunda zan iya fada na fada masa, domin na lura ba da wasa yake tambaya ba.
“Ji dan Allah kin saki baki kina ta magana da shi har da zancen zuwa Abuja, cewa yai ki bishi ku tafi?”
Na zaro ido ina bude baki.
“A a Wallahi ya za ayi yace haka? Na fada masa ban taba zuwa ba ne, shine muke zancen”
Kamar hadin baki sai ga Yunus din yayi knocked.
“Yes”
Ahmad na bada umarni ya shigo rike da wasu files a hannu, kallo yai ya sakar min murmushi kamin ya karasa gurin Ahmad din yana fadin.
“Tace gobe ne birthday ta shine nace ya kamata tai mana celebration, kuma tace bata taba zuwa Abuja ba, gaskiya ya kamata a turata ko ta hanyar aiki ne taje ta gano Abuja”
It's normal for a friend like Yunus yai magana da friend dinsa like that kamar Ahmad, kuma ban ga wani illa a ciki ba, amman sai Ahmad yai masa banza ya karbi files din kawai ya aje.
“Miya samu System dinka?”
“Wallahi ta tsaya ne gaba daya, ban san abunda ya same ta”
“Kuma ba kai magana ba”
“No na yi magana da Tukur yace min baya gari shiyasa”
“Kuma Tukur ne kawai yake mana gyara a kamfanin nan?”
“No na dai fi yarda da aikinsa”
“Ka dauko wata ka kai office dinka”
“Okay”
Ban yi kwalliya ba, hoda ce kawai na shafa bayan mai sai dan turaren da na saka, sannan na shafa dan mai a bakina na dauki bakar jakata na rayata na nufi dakin Mama nai mata sallama, a tsakar gida na samu Inna ita mai mata sai na dawo na kama hanyar zuwa office din rai na fes.
Na samu napep daf da kofar gidanmu ya sauke wasu sai kawai na tsayar da shi na fada masa inda zai kai ni sannan na shiga.
Misalin tara da yan mintuna na isa office din, ko da na shiga na samu komai tsaf kamar kullum, wato masu gyara office din sun gyara shi sai kamshi yake. Jaka na aje a inda na saba ajewa na nufi window ya bude abun mamaki yau Ahmad ya shigo da wuri na hango shi jikin windows sa tsaye hannunsa daya rike da mug dayan kuma a aljihunsa har yana dago min mai kofin alamar gaisuwa. Ni kuma na daga masa hannu ina murmushi sannan na juyo na zauna a kujera na fara aikina.
Knocked akai kamin na ce komai Yunus ya turo kofar office din ya shigo.
“Good morning”
“Morning how are you sir”
“Fine, hope dai baki gaji da ni ba”
Ya fada yana murmushi kamar yadda nima nake mayar masa da murmushin.
“No haba dai Bismillah”
Na fada ina nuna masa gurin da system din take. Yau kusan kwana biyu kenan a office dina yake aikinsa saboda system din da ke office dinsa ta samu matsala kamar yadda ya fada min.
“Yau ma dai kin yi kyau kamar jiya, wai kiye sirrin”
Ya fada yana nufar gurin da System din take yana aje kayan dake hannunsa. Ni kuma sai nai dariya mai sauti.
“Na gode, sirrin aikin kamfaninku ne ka san yana karawa ma'aikatanku kyau da natsuwa”
He was laughing so hard kamar na fadi masa wani abun dariya sosai.
“Oh wow okay zan fadawa mutanen kamfaninku haka kuwa, so that kowa ya rike aikinsa da kyau kar yai laifin da zai saka a koreshi”
Nima dariyar nai.
“Gaskiya ya kamata kam, ko ma an koresu ku makale kar su je”
“Hahaha Haima kenan”
Ya fada yana cigaba da dariyar, wani abu na ji marar dadi ya ratsa zuciyata sakamakon kirana da yai da sunan da Abdulhamid ke kirana da shi. ban sake cewa komai ba na cigaba da aikina, sai jin nai wayata ta yi kara alamar sako, a zato na mtn ne hakan yasa na share wayar ban duba.
“I think this week zan je Abuja In-Sha-Allah”
Na kalleshi.
“Gurin me?”
“Wani aiki ne, kin san can din ma muna da branch, so idan mai gida be je ba dole ni zan je”
“Okay kace zaka leka garin manya kenan”
Dariya yai.
“Kin tana zuwa Abuja?”
“No ni ai ban taba wuce Gusau ba”
“Oh duk wayewar nan taki? Ya kamata ace kin zagaya manyan birane ai”
“To ai ban san kowa ba, kaga ko ai ba zan tashi naje garin da ba dangi ba na zauna”
“Ba dole sai kana da dangi zaka ziyarci gari ba, idan kina da friends ko ma a karan kanki zaki iya zuwa ki huta”
“Hm da dai ace ni namiji ce zanje amman ina mace ai be kamata ba”
“Believe me akwai matan da suke zuwa garin da ba su san kowa ba, wasu idan za su yi birthday haka ko suje bikin friends dinsu”
“Tab ni kam ba zan iya ba, na je garin da ban san kowa ba? Amman masu zuwa birthday a wani garin basa celebration ko? Dan na san ba za su samu masu binsu ba”
“Irin yaran manya haka, ko manyan mata wasu ma ba su tsayawa kansu ba, so suna zuwa da friends dinsu sai a hadu can ayi ta abubuwa wasu har kasar suke bari fa, kuma kin san ba kowa ke celebration din birthday ba, like me ni ma bana bikin birthday amman a ranar zan ci na sha na yi duk abunda na so”
“Nima haka nake yi gaskiya, ban tana bikin birthday ba, ko cake ban tana ci a ranar birthday na ba sai dai na gode Allah nai saka a status shikenan”
“Ni ina ciye ciye gaskiya, kuma zan iya ma mutane abu albarka birthday na, my is 22 December”
“Mine is 4 October”
Ya kalleni.
“O really? That's mean gobe kike birthday kenan?”
Na yi dariya ina gyada masa kai.
“Wow ki ce ke princess ce kenan”
Dariya na sake yi, a raina ina fadin princess sai kace wata yarinya. Wayata ce tai ringing sai da na dauke kaina daga computer sannan na kai hannuna na dauko wayar ganin bakuwar ce yasa ban damu na dauka ba sai kawai na aje wayar a saman tana ringing.
“Ah gaskiya ya kamata ki yi mana celebration”
“Haba wannan kuma ai sai yara”
Na fada ina kallon number kiranta ya sake shigowa. Hannuna kai na dauka na danna picking nakara a kunne.
“Hello Sallamu alaikum”
“Zo office dina yanzu nan”
Yana fadar hakan ya kashe wayar, ko ba a fada min ba na san mai murya, kuma na san duk a kamfanin nan shi kadai ne zai kira haka kai tsaye ya bani umarni, duk da be taba ba, be ma taba kiran wayata ba, and the way da yai maganar kamar yana cikin fushi. Hakan yasa na dan tsorata, a take na fara tunanin abunda nai wanda ba daidai tsakanin jiya zuwa yau, domin hausawa na cewa karka ji tsoron kira ka ji tsoron laifin da kai, but if i can remember ai dazun da na shigo mun gaisa da shi idan fushi yake da ni ba zai daga min hannu ba, oh maybe wani abun nai ba daidai ba, a take na fara duba sakkwanin mail din wai ko akwai wanda ya kamata na aika masa kuma ban aika ba.
“Ko a kamfanin nan ne ya kamata ki yi mana celebration”
Yunus ya fada yana danna computer dake gabansa yana murmushi, nima murmushin nai na mike tsaye rike da wayata da sai a lokacin na ke ganin sakon da ya turo min.
“Same ni office yanzu”
Oh ashe ba mtn ba ne kenan dazun, na fada a raina sannan na nufi kofar fita ina fadin.
“Ina zuwa Sir”
“Okay”
Ya amsa hankalinsa na gurin abunda yake, cikin faduwar gaba da fargaba na nufi office din kuwa da nasan ban yi wani abun ba, kuma a yadda nake da shi a yanzu bana tunanin akwai wata matsala a tsakaninku, sai muryarsa ta tabbatar min da ba lafiya ba.
Na tura office din na farko na shiga har na gaisa da mutumen dake ciki, haka a na biyu har na kai a nasa office din na tura na shiga bayan na yi knocked.
Ina shiga ya watsa min wata uwar harara, har sai da gabana ya fadi.
“Sai yanzu kika ga damar zuwa?”
“Ban ga sakon ba ne sai yanzu, ina zaki gan shi hankalinki yana can wani guri, me Yunus yake yi a office dinki?”
“Aiki”
“Shi office dinsa kwantarsa ake a ciki?”
“System dinsa ce ta lalace”
“Kuma ba zai iya magana a gyara ba, sai dai ya zo office dinki ya zauna shi tsohon dan iska, ke kuma kin saki jiki sai dariya kike kin kebe da shi kamar wani muharraminki”
The way da yai maganar sai naga kamar ba shi ba, to miye laifi dan Yunus ya zauna a a office dina? Naga dai idan wani abu zamu aikata ai ba za mu bar windows a bude ba, kuma yana maganar Yunus din ba muharramina ba ne shi din muharramina ne da na kebe da shi a nan? I was so so confused.
“Zauna nan”
Ya nuna min kujera, na yi zaton wani abun zan masa dan haka na nufi kujerar na zauna.
“Look at you kuna da exchanging words, mi kuke cewa”
Kallon mamaki nai masa.
“Magana kawai muke”
“Mi yace miki?”
Na yi shiru ina ta tunanin ta inda zan fara, ni kam yaushe rabon da ayi min haka wai a tsareni ana son na fadi wani abu da na fada ko kuma wani ya fada min.
“Maganar zuwa Abuja ne da yai min, sai maganar Birthday, sai.... At first dai cewa yai na yi kyau sai..... Maganganu dai haka... ”
Sama sama na tsakuro abunda zan iya fada na fada masa, domin na lura ba da wasa yake tambaya ba.
“Ji dan Allah kin saki baki kina ta magana da shi har da zancen zuwa Abuja, cewa yai ki bishi ku tafi?”
Na zaro ido ina bude baki.
“A a Wallahi ya za ayi yace haka? Na fada masa ban taba zuwa ba ne, shine muke zancen”
Kamar hadin baki sai ga Yunus din yayi knocked.
“Yes”
Ahmad na bada umarni ya shigo rike da wasu files a hannu, kallo yai ya sakar min murmushi kamin ya karasa gurin Ahmad din yana fadin.
“Tace gobe ne birthday ta shine nace ya kamata tai mana celebration, kuma tace bata taba zuwa Abuja ba, gaskiya ya kamata a turata ko ta hanyar aiki ne taje ta gano Abuja”
It's normal for a friend like Yunus yai magana da friend dinsa like that kamar Ahmad, kuma ban ga wani illa a ciki ba, amman sai Ahmad yai masa banza ya karbi files din kawai ya aje.
“Miya samu System dinka?”
“Wallahi ta tsaya ne gaba daya, ban san abunda ya same ta”
“Kuma ba kai magana ba”
“No na yi magana da Tukur yace min baya gari shiyasa”
“Kuma Tukur ne kawai yake mana gyara a kamfanin nan?”
“No na dai fi yarda da aikinsa”
“Ka dauko wata ka kai office dinka”
“Okay”