Sashe 106
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Wannan ba abun wasa ba ne, Wallahi zai iya cutar da kai, duk mutunen da zai iya keta haddin aure ya lalata rayuwar wata to zai iya komai, ban san adadin abunda ya aikata ba, ban san iya abunda yai ma wasu ba, wata kila ya tana kisa, ban sani ba, zai iya cutar da kai, kana tunanin idan wani abun ya same ka ni zan jidadi? Zan iya walwala?”
“Duk wannan hawayen saboda ni? Mi kake nai?”
Ya tambaya yana faka motarsa gefen titi.
“Ka kwarara tsaro a gidan da kamfani, kuma ka fadawa police halin da kake ciki”
“Police ba za su iya ba ni tsaro ba, kuma ki kwantar da hankalinki babu abunda zai same ni”
Ya miko min ruwa.
“How ta yaya zaka ce babu abunda zai same ka bayan Abdulhamid ya bata kuma....”
“Abdulhamid yana hannun DSS”
“What....?”
Na masa wani irin kallo na mamaki.
“Yes su suka kama shi yana Abuja”
“Ho.. How.... Do you know kai kasa aka kama shi?”
Na nuna shi da yatsana.
“No bincike yasa aka kama shi, har Abraham din suna can tare”
“Miya faru? Fada min?”
“Nima ban sani ba”
“Then taya ka san an kama su?”
“Mataimakin DSS na jihar nan he's my friend, shi ya fada min”
“Miyasa aka kama su? Kai ka saka aka kamasu?”
“Saboda me? Idan ma zan saka a kama wani ai Abraham zan saka a kama ba Abdulhamid ba, na fada masa matsalar Abraham ne kawai ana cikin bibiyar sa ana bincike ta masa, sai ga wannan ya faru da Abdulhamid din, shi ya fadi Abraham aka kama su”
“Amman miyasa aka kama su din?”
“Kin san sana'ar da Abdulhamid din yake yi?”
“Yana saida mota kuma yana aiki”
“Ya taba baki labarin Abraham, ko kuma shi Abraham din ya taba baki labarin Abdulhamid”
“A'a”
“Shiyasana fada miki, Abraham din ba son gaskiya yake miki ba, ba zai bar abunda yake saboda ke ba, ba kuma zai fallasa miki sirrinsa ba, da dawo gareki ne kawai saboda yana son haihuwa, kamar yadda ya fada miki zai iya mutuwa a ko yaushe idan asirinsa ya tonu, ya taba fada miki cewar yana da mata?”
Na girgiza kai da sauri.
“A a”
“To yana da mata tana can garinsu enugu, dukansu su biyu suna wani business, kuma babu mai sanin alakarsu sai su i think basa yawan ziyarta juna ne saboda gudun kar a zarge su”
Bude motar nai na fita ina shakar iskar waje. Sai shi ma ya bude gefensa ya fito ya zagayo inda nake.
“Hakan na nufi Abdulhamid ya san cewa shi yai min fyade kenan?”
“Be zama lallai ya sani ba, domin ba kowa zai yarda abokinsa ya keta haddin matarsa ba, zai kuma iya yiyuwa ma shi ya saka shi, ko ma dai minene gaskiya zata bayyana”
Dana lumshe idona sai hawaye suka sauko min. Ina jin lokacin da Ahmad yaja dogon numfashi ya sauke.
“Sometimes, Allah yana jarrabar bawanaa ba dan baya son bawan ba, daga baya kuma sai ya kawo masa sauki, a yanzu ne zaki gane ba karamin taimakinki Allah yai ba da ya raba ki da Abdulhamid, shi kan shi uban yayanki da za ki bibiya tahirinsa wata kila za ki samu wani abun ya same shi, ko kuma zai same shi a gaba, shi kansa Abraham din da kin yi kuskuren aminta da shi kin aureshi da kin jefa kanki a cikin wata matsalar, trust me Allah yana son ki, and i think lokacin kukanki ya kare, wani jindadin nesa, wani za ki ga sai ya tsufa ta hanyar yaya zai samu, wani kuma sai ya sha wahala, wani kuma ya jidadin farko daga baya wahalar ta zo, ki gode Allah Allah ya kawo miki sauki tun a yanzu”
Bude idona nai na kalleshi, sai na ji ya kara kwanta min a rai, yana da gaskiya wani jindadin nesa yake, wani kuma ba za a taba jindadin ba har abada.
“Bana son ki saka kanki a damuwa, bana da tashin hankali a yanzu kamar damuwarki, Doc Nura ya fada min cewar idan zuciyarki ta sake bugawa zan a iya rasa ki, so bana tafar haka, kina bukatar ki rayu ko dan saboda yayanki da ni, ina ji a raina cewar ni kadai ne namijin da zan juya duniyarki ki jidadi, na baki abubuwan da kika rasa, na ranta ran mahaifiyarki da yan'uwanki, ba alfahari nake ba, ba kuma ina fada da wata manufa ba, dukan abunda zan yi a yanzu dan na saka ki cikin farinciki ne na mantar da ke damuwarki, a yanzu kam bana jin zan iya bari ko kuda ya cutar da ke lims, wahalarki ta yanke da izinin Allah”
Ji nai kamar ya daure ni, indai jin kalamai ne na sha jinsu daga bakin maza, amman baka gane gaskiyar kowa sai ka zauna da shi, sai dai idan na kalli Ahmad sai na ga kamar be yi kama da mutanen da za su iya wannan ba. Sai dai idan har kalamansa suna nufin soyayya ko aure to ban shirya ba a yanzu, bana jin akwai namijin da ya cancance ni a yanzu sama da Abdallah.
“Zamu iya komawa Gurin Aikin?”
“No na fito da ke nan waje ne saboda ki samu natsuwa and fresh air, yanzu kuma ki zan kai ki gida ki huta just for today daman yau birthday ki ne you're princess”
Na juya na shiga motar, shi ma ya zagaya ya shiga yai mata key.
“Kamin na hadu da ke, idan na tuna babu matata babu Baby Namra babu Mahaifina sai na ji duniya ta ta koma upside down, ammn daga lokacin kaddarar rayuwarki ta same ni sai komai ya canja, na zama jarumi na ji cewar nima zan sake samun farinciki, a duk lokacin da na tuna da yata sai na tuna ki sai na ji bakincikin rashinta ya tafi”
Kallonsa nai sai ya sakar min irin murmushin nan da ake cewa ya fi kuka ciwo.
“Ya isa a nan zan sauka sai na hau napep”
“Ba ki son a gan ki da ni ne ko? Fine”
“No bana son ina shiga motar mutane ne, yanzu sai ka ji ana magana”
“That's why na baki mota ai dan na dauke miki wahalar hawan napep, kuma tsakani da Allah ina jin bakincikin hawan Napep da kike saboda namiji ne zai tuka ki”
“Idan ka bani motar ka bude hanyar da za su kara zargina, a fara magana akai”
“To shikenan zan aje miki har lokacin da za ki bukata”
Har na bude motar da zimmar fita sai kuma na kalleshi.
“Baka fada min wani irin business suke ba?”
“Nima ban sani ba, amman ko minane idan sun gama bincike ai kowa zai ji”
Na fita daga motar sannan na rufe mishi motar sai ganin nai ya sauke gilashin motar.
“Ki kula min da kanki”
Ya fada sannan yai ma motar key ya hau titi, ba ni da abunda ya wuce na bi motarsa da kallo har sai da na daina hangota.
7/21/21, 10:48 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
5️⃣3️⃣
ABDALLAH POV.
Misalin tara da yan mintuna ya shigo gurin Hajiyarsa kana kallonsa kasan yana cikin damuwa. Yayyen Hajiya ya tarar a falon wato Hajiya Altine da Hajiya Rukaiya, sai da ya gaishe su sannan ya wuce dakin mahaifiyarsa, yadda ya same ta zaune saman carpet rike da carbe fuskarta da damuwa sai ya kara jefashi a cikin nasa damuwar. Kusa da ita ya zauna bakin gado yana kallonta da Fuskarsa da ke bayyana damuwarsa karara.
“Hajiya barka da dare”
Ta dago ta kalleshi kana ganin idonta ka san ta sha kuka.
“Barka dai Husaini, ya aikin”
“Alhamdulillah, Hajiya ki rage saka kanki a damuwa, In-Sha-Allah za a ga Abdulhamid”
“To Allah yasa ni abun yanzu har tsoro yake ba ni, jikina yayi sanyi sosai, idan na duba sai na rasa abunda Abdulhamid zai yi wa wani da zai cutar da shi mutumen da magana ma bata sha masa kai ba, Allah yasa ba yan fillar kai ya hadu da su ba, domin na san masu neman kudi fansa da su suka kama shi da yanzu sun kira sun fadi abunda suke bukata”
Jimmmm Abdallah yai kamin ya kalleta a natse ya ce.
“Hajiya zaki iya tuna lokacin da akai yi Halima fyade?”
“Na sani”
“Mutumen da yai mata fyade wani kirista ne, kuma abokin Abdulhamid ne, ban san miya kai shi gidan ba har yai ma Halima fyade, a yanzu kuma ina kyautata zaton kamar da sa hannunsa gurin dauke Abdulhamid”
Cikin tashin hankali Hajiya ta kalleshi.
“Kamar kai ya akai ka sani?”
“Halima ta fada min mutumen ya dawo yana sonta, saboda cikin da tai shi kuma haihuwa yake nema, bata aminta da shi ba amman ya dage yana son ta aure shi, shiyasa na fada mata gaskiyar cewar shi yai mata fyade, sai dai ita bata san yana da alaka da Abdulhamid ba, ni kai dai na sani nima kuma saboda na taba ganinsu tare har hotuna sun yi tare, shi mutumen police”
“To me zai saka ya dauke Hassan?”
“Saboda ni na fadawa Abdulhamid gaskiyar daya kasa yarda da Halima a lokacin da abun ya same ta, ke da shi kuna ganin kamar ta aikata zina ne, yayi ta bakinciki yana fadar cewar shi Abraham zai ciwa amana, wata kila yai masa magana ko yai masa wata barazana shi kuma Abraham din ya dauke shi”
“Amman miyasa baka fadi wannan ba? Sai yan sanda su bincike shi mutunen?”
“Hajiya idan baka iya kama barawo ba, sai barawo ya kama ka, shi Abraham din police ne kuma da na bincika sai na samu labarin cewar baya cikin garin nan a office dinsa ma har an saka wani, amman mu saurara na kwana biyu tukuna tun da mun kai report din gurin Police kuma ana Addu'a, ko minene zai bayyana In-Sha-Allah”
“Amman irin wannan ai kama shi za ayi a bincike shi ko kuma ita Halimar, waya sani ko ma ita ta saka shi ya sace shi saboda ta dauki fansa balle ta ji zai yi aure, kuma ta ga shi Abraham din yan sonta”
“Haba Hajiya wane irin Halima kuma?”
“Duk wannan hawayen saboda ni? Mi kake nai?”
Ya tambaya yana faka motarsa gefen titi.
“Ka kwarara tsaro a gidan da kamfani, kuma ka fadawa police halin da kake ciki”
“Police ba za su iya ba ni tsaro ba, kuma ki kwantar da hankalinki babu abunda zai same ni”
Ya miko min ruwa.
“How ta yaya zaka ce babu abunda zai same ka bayan Abdulhamid ya bata kuma....”
“Abdulhamid yana hannun DSS”
“What....?”
Na masa wani irin kallo na mamaki.
“Yes su suka kama shi yana Abuja”
“Ho.. How.... Do you know kai kasa aka kama shi?”
Na nuna shi da yatsana.
“No bincike yasa aka kama shi, har Abraham din suna can tare”
“Miya faru? Fada min?”
“Nima ban sani ba”
“Then taya ka san an kama su?”
“Mataimakin DSS na jihar nan he's my friend, shi ya fada min”
“Miyasa aka kama su? Kai ka saka aka kamasu?”
“Saboda me? Idan ma zan saka a kama wani ai Abraham zan saka a kama ba Abdulhamid ba, na fada masa matsalar Abraham ne kawai ana cikin bibiyar sa ana bincike ta masa, sai ga wannan ya faru da Abdulhamid din, shi ya fadi Abraham aka kama su”
“Amman miyasa aka kama su din?”
“Kin san sana'ar da Abdulhamid din yake yi?”
“Yana saida mota kuma yana aiki”
“Ya taba baki labarin Abraham, ko kuma shi Abraham din ya taba baki labarin Abdulhamid”
“A'a”
“Shiyasana fada miki, Abraham din ba son gaskiya yake miki ba, ba zai bar abunda yake saboda ke ba, ba kuma zai fallasa miki sirrinsa ba, da dawo gareki ne kawai saboda yana son haihuwa, kamar yadda ya fada miki zai iya mutuwa a ko yaushe idan asirinsa ya tonu, ya taba fada miki cewar yana da mata?”
Na girgiza kai da sauri.
“A a”
“To yana da mata tana can garinsu enugu, dukansu su biyu suna wani business, kuma babu mai sanin alakarsu sai su i think basa yawan ziyarta juna ne saboda gudun kar a zarge su”
Bude motar nai na fita ina shakar iskar waje. Sai shi ma ya bude gefensa ya fito ya zagayo inda nake.
“Hakan na nufi Abdulhamid ya san cewa shi yai min fyade kenan?”
“Be zama lallai ya sani ba, domin ba kowa zai yarda abokinsa ya keta haddin matarsa ba, zai kuma iya yiyuwa ma shi ya saka shi, ko ma dai minene gaskiya zata bayyana”
Dana lumshe idona sai hawaye suka sauko min. Ina jin lokacin da Ahmad yaja dogon numfashi ya sauke.
“Sometimes, Allah yana jarrabar bawanaa ba dan baya son bawan ba, daga baya kuma sai ya kawo masa sauki, a yanzu ne zaki gane ba karamin taimakinki Allah yai ba da ya raba ki da Abdulhamid, shi kan shi uban yayanki da za ki bibiya tahirinsa wata kila za ki samu wani abun ya same shi, ko kuma zai same shi a gaba, shi kansa Abraham din da kin yi kuskuren aminta da shi kin aureshi da kin jefa kanki a cikin wata matsalar, trust me Allah yana son ki, and i think lokacin kukanki ya kare, wani jindadin nesa, wani za ki ga sai ya tsufa ta hanyar yaya zai samu, wani kuma sai ya sha wahala, wani kuma ya jidadin farko daga baya wahalar ta zo, ki gode Allah Allah ya kawo miki sauki tun a yanzu”
Bude idona nai na kalleshi, sai na ji ya kara kwanta min a rai, yana da gaskiya wani jindadin nesa yake, wani kuma ba za a taba jindadin ba har abada.
“Bana son ki saka kanki a damuwa, bana da tashin hankali a yanzu kamar damuwarki, Doc Nura ya fada min cewar idan zuciyarki ta sake bugawa zan a iya rasa ki, so bana tafar haka, kina bukatar ki rayu ko dan saboda yayanki da ni, ina ji a raina cewar ni kadai ne namijin da zan juya duniyarki ki jidadi, na baki abubuwan da kika rasa, na ranta ran mahaifiyarki da yan'uwanki, ba alfahari nake ba, ba kuma ina fada da wata manufa ba, dukan abunda zan yi a yanzu dan na saka ki cikin farinciki ne na mantar da ke damuwarki, a yanzu kam bana jin zan iya bari ko kuda ya cutar da ke lims, wahalarki ta yanke da izinin Allah”
Ji nai kamar ya daure ni, indai jin kalamai ne na sha jinsu daga bakin maza, amman baka gane gaskiyar kowa sai ka zauna da shi, sai dai idan na kalli Ahmad sai na ga kamar be yi kama da mutanen da za su iya wannan ba. Sai dai idan har kalamansa suna nufin soyayya ko aure to ban shirya ba a yanzu, bana jin akwai namijin da ya cancance ni a yanzu sama da Abdallah.
“Zamu iya komawa Gurin Aikin?”
“No na fito da ke nan waje ne saboda ki samu natsuwa and fresh air, yanzu kuma ki zan kai ki gida ki huta just for today daman yau birthday ki ne you're princess”
Na juya na shiga motar, shi ma ya zagaya ya shiga yai mata key.
“Kamin na hadu da ke, idan na tuna babu matata babu Baby Namra babu Mahaifina sai na ji duniya ta ta koma upside down, ammn daga lokacin kaddarar rayuwarki ta same ni sai komai ya canja, na zama jarumi na ji cewar nima zan sake samun farinciki, a duk lokacin da na tuna da yata sai na tuna ki sai na ji bakincikin rashinta ya tafi”
Kallonsa nai sai ya sakar min irin murmushin nan da ake cewa ya fi kuka ciwo.
“Ya isa a nan zan sauka sai na hau napep”
“Ba ki son a gan ki da ni ne ko? Fine”
“No bana son ina shiga motar mutane ne, yanzu sai ka ji ana magana”
“That's why na baki mota ai dan na dauke miki wahalar hawan napep, kuma tsakani da Allah ina jin bakincikin hawan Napep da kike saboda namiji ne zai tuka ki”
“Idan ka bani motar ka bude hanyar da za su kara zargina, a fara magana akai”
“To shikenan zan aje miki har lokacin da za ki bukata”
Har na bude motar da zimmar fita sai kuma na kalleshi.
“Baka fada min wani irin business suke ba?”
“Nima ban sani ba, amman ko minane idan sun gama bincike ai kowa zai ji”
Na fita daga motar sannan na rufe mishi motar sai ganin nai ya sauke gilashin motar.
“Ki kula min da kanki”
Ya fada sannan yai ma motar key ya hau titi, ba ni da abunda ya wuce na bi motarsa da kallo har sai da na daina hangota.
7/21/21, 10:48 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
5️⃣3️⃣
ABDALLAH POV.
Misalin tara da yan mintuna ya shigo gurin Hajiyarsa kana kallonsa kasan yana cikin damuwa. Yayyen Hajiya ya tarar a falon wato Hajiya Altine da Hajiya Rukaiya, sai da ya gaishe su sannan ya wuce dakin mahaifiyarsa, yadda ya same ta zaune saman carpet rike da carbe fuskarta da damuwa sai ya kara jefashi a cikin nasa damuwar. Kusa da ita ya zauna bakin gado yana kallonta da Fuskarsa da ke bayyana damuwarsa karara.
“Hajiya barka da dare”
Ta dago ta kalleshi kana ganin idonta ka san ta sha kuka.
“Barka dai Husaini, ya aikin”
“Alhamdulillah, Hajiya ki rage saka kanki a damuwa, In-Sha-Allah za a ga Abdulhamid”
“To Allah yasa ni abun yanzu har tsoro yake ba ni, jikina yayi sanyi sosai, idan na duba sai na rasa abunda Abdulhamid zai yi wa wani da zai cutar da shi mutumen da magana ma bata sha masa kai ba, Allah yasa ba yan fillar kai ya hadu da su ba, domin na san masu neman kudi fansa da su suka kama shi da yanzu sun kira sun fadi abunda suke bukata”
Jimmmm Abdallah yai kamin ya kalleta a natse ya ce.
“Hajiya zaki iya tuna lokacin da akai yi Halima fyade?”
“Na sani”
“Mutumen da yai mata fyade wani kirista ne, kuma abokin Abdulhamid ne, ban san miya kai shi gidan ba har yai ma Halima fyade, a yanzu kuma ina kyautata zaton kamar da sa hannunsa gurin dauke Abdulhamid”
Cikin tashin hankali Hajiya ta kalleshi.
“Kamar kai ya akai ka sani?”
“Halima ta fada min mutumen ya dawo yana sonta, saboda cikin da tai shi kuma haihuwa yake nema, bata aminta da shi ba amman ya dage yana son ta aure shi, shiyasa na fada mata gaskiyar cewar shi yai mata fyade, sai dai ita bata san yana da alaka da Abdulhamid ba, ni kai dai na sani nima kuma saboda na taba ganinsu tare har hotuna sun yi tare, shi mutumen police”
“To me zai saka ya dauke Hassan?”
“Saboda ni na fadawa Abdulhamid gaskiyar daya kasa yarda da Halima a lokacin da abun ya same ta, ke da shi kuna ganin kamar ta aikata zina ne, yayi ta bakinciki yana fadar cewar shi Abraham zai ciwa amana, wata kila yai masa magana ko yai masa wata barazana shi kuma Abraham din ya dauke shi”
“Amman miyasa baka fadi wannan ba? Sai yan sanda su bincike shi mutunen?”
“Hajiya idan baka iya kama barawo ba, sai barawo ya kama ka, shi Abraham din police ne kuma da na bincika sai na samu labarin cewar baya cikin garin nan a office dinsa ma har an saka wani, amman mu saurara na kwana biyu tukuna tun da mun kai report din gurin Police kuma ana Addu'a, ko minene zai bayyana In-Sha-Allah”
“Amman irin wannan ai kama shi za ayi a bincike shi ko kuma ita Halimar, waya sani ko ma ita ta saka shi ya sace shi saboda ta dauki fansa balle ta ji zai yi aure, kuma ta ga shi Abraham din yan sonta”
“Haba Hajiya wane irin Halima kuma?”