Sashe 82
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da hannu daya yake tuka motar yayinda dayan hannunsa yake dafe da idonsa, wani zafin bala'i idon yake masa ga ruwan da ake kama da bakin kwarya, har baya iya gani da kyau saboda karfinsu.
A dole ya faka motarsa gafen titi, slowly ya dauke hannunsa daga idon da ke masa wani mugun zugi, ji yai idaniyar ta cika da abu mai kauri shi ba hawaye ba kuma ba ya san jini ne har sai da ya duba hannunsa. Jini a ciki kuma shine yake cika masa idon har baya gani da idon daya.
Lumshe idanuwan yai duka biyu yana sauraren yadda zugin yake shigar masa har cikin kansa, a rufe da idon ya saka hannun aljihu ya dauko wayarsa sai a lokacin yai kokarin bude idon daya yana duba iPhone dinsa wacce ta gama daukewa dip, sakamakon ruwan da ta sha, ba wayar kadai ba tufafin jikinsa ma sun gama jika seat dinsa balle kuma wayarsa.
Iskar bakinsa ya bushar yanzu be san yadda zai yi ya kira Doc Nura ba balle yaji idan ma yana gari ko yana asibitin ko gida, daman can a tsarinsa be yarda wani likitan ya duba shi ba sai family doc su, domin ya yarda da aikinsa hundred percent.
“Ba ma ita ce mahaukaciyar ba ni ne mahaukacin, taya zan shigar mata fada? Fadan ma da mahaukaci dan'uwanta? Matar da ta kashe min yarinyar? What's is wrong with me?”
Ya fada yana jin haushin abunda ya aika..
“Bata ma tsaya ta dubani ba fa sai kawai ta gudu, idan ma kashe ni zai yi ita dai ta tsira, mahaukaciyar banza i hate her”
Ya sake fada cikin fusata yana cizon bakinsa. A gurin ya tsaya har sai da ruwan suka dauke gaba daya sannan ya karasa tukin zuwa gida kamin ya isa har wani jiri yake ji cikin kansa.
“Ai I'm human being be kamata ina gani ayi kisan kai ba, shiyasa na taimake ta, amman yanzu na gano matar nan bakincikina take so take ta illatani bayan ta kashe min ya, be m kamata na barta tana aiki a kamfani na ba ai”
Shi kadai yake ta magana da kansa har ya faka motarsa a harabar gidan, yana kokarin bude motar ya fita ya tambayi kansa.
“Ko ma miya kai ni fada da mahaukaci? Da mahaukaci da mahaukaciya suna fada ni mai hankali miya kai ni ciki?”
After ya fito daga motar ya bawa kansa amsa.
“Kaddara.... ”
Part dinsa ya wuce, yana shiga ya fara ziyartar bandakin ya wanke fuskarsa, ya saka tissue yana tare jinin a hankali sannan ya dawo dakinsa ya dauko dayar wayarsa da ke gida yana kokarin kiran Doc Nura.
“Hasara nawa ga saka ni a yau? Ta saka na jika tufafina ga idona daya ga phone dina.....”
Wani irin haushinta ne ya kara cika msa zuciya. Sai da ya tabbatar Doc Nura na aibitin sannan ya canj tufafin jikinsa ya dauko key din wata motar ya fice ba tare da ya leka part din Hajiya ba, domin baya son ya tashi hankalinta.
A asibiti babu kalar dariyar da Doc Nura be msa ba.
“To kai yanzu miya kaika raba fada da mahaukaci? Ai gashi an bak tukuici”
“You make me hate her more”
“Wai wacece wannan?”
“Wata mahaukaciya ce mai ruwan masu hankali”
Ya hada fuska babu annuri can kuma yai murmushi.
“Ita ma fa taji wuya, ba da wasa ya moreta ba”
Dadi yaji tun da ita ma ta ji wuya, but maganar Allah shi yafi kowa shan wuya tunda shi be shi yaja mahaukacin ba.
Bayan Doc ya duba idon ya bashi maganin na sha da shafawa a idon ya kuma fada msa yadda zai kula da ido. After ya dawo gida ya kira shiga part dinsa ya kiran Yunus.
“Yu akwai wani mahaukaci da ke kusa da kamfanin mu, daga hannun dama gurin wani shagon kwano, za ka iya gane shi?”
Sai da Yunus yai tunani sosai sannan ya amsa masa da.
“Yes na gane shi kullum nn yke zama”
“Ka sa a dauke shi a kai shi gidan mahaukata”
“Why?”
“Why? Ya zan baka umarni ka tambayeni why?”
Ya amsa a fusace, kamar Yunus din ba abokinsa ba ne, saboda yau yana cikin zafin kai. Bayan ya kashe wayar yaje gaban madubi yan duba idon, idonsa daya yayi kwancin jini a ciki gaba daya gefen idon ya kumbura, abunka da farin mutun har wani ja gurin yai.
“Ina zaman zamana ta ja min masifa.....”
Ya karasa maganar ta tari sai jini ya biyo baya, daman haka yake yanzu da ransa ya bace sai ya fada tarin jinin sai ciwon kirji.
Toilet ya nufa aman jini yai ba kadan ba, shi kanshi sai da abun ya dan tsorata shi, har yana zargin wata kila saboda ya sha ruwan sama ne abun ya kara hade masa, wanka yai sannan ya dawo dakinsa ya sha maganinsa ha kwanta.
Sai 4:21 ya farka, sallah ce abunda ya fara gabatarwa sannan ya duba idon nasa kamin ya nufi part din Hajiya. Tana ganinsa hankalinta yai mugun tashin musamman idon nasa wanda ta hango jan jini a ciki.
“Miya same ka Gwarzo?”
“Hadarin nan ne da ya taso ina kokarin shiga, mota sai kasa ya shigar min ido”
“Wannan ba kasa ba ne, hannu ne ga kwancin shi nan a idonka, kaga ni ko shiyasa bana son kana zuwa kana dadewa a waje, na sha fada maka da kun gama aiki ka rika dawowa gida, na san halinka da zuciya wata kila kaje ka bugu wani ya rama”
Hannu ya kama yana kokarin zaunawa da murmushi a fuskarsa.
“Haba Hajiya ai na girmi wannan, Wallahi kaddara ce kawai amman In-Sha-Allah ba zai sake faruwa ba”
“Bari na kira Doc Nura”
“Naje gurinsa ya bani magani ya duba idon”
Sam bata yarda ba har sai da ta kira shi da kanta tai magana da shi ya tabbtar mata da cewar ya dubashi sannan hankalinta ya kwanta.
“And daga yau ba zaka je aiki ba sai nan da one week”
Da sauri ya kalli Hajiyarsa yana sakin baki.
“Amman Hajiya kin san idan ba da ni ba wani abun ba zai yiyu ba”
“Doka ta ce wannan”
Ta fada fuskarta babu alamun wasa.
“Yaro ba san ciwon kansa ba, sai idan ana nuna maka abu kace kai ba yaro ba ne”
Rasa yai abunda zai ce mata, ba zai iya karya dokarta ba, kuma ba zai so fashin zuwa aiki ba, zai iya amfani da bakin gilashi ya rufe idonsa.
“Idan an yi magariba ka kwanta karka tashi sai an yi isha'i, zan dafa maka carrot da allayau da wake yanzu suma suna gyara ido”
A dolen dolensa ya amsa mata da okay, ta tashi ta shiga kitchen da zimmar dora masa girkin, shi kuma ya bita da kallo yana ta tunanin randa Hajiya zata yarda da cewar ya girma san ciwon kanshi.
HALIMATU POV.
A hankali na kalleshi, fuskarsa a hade take sam babu alamar wasa a umarninsa. Na sani ba lallai ne su yarda su canja min aiki ba, balle kuma har su yarda na rika saka wasu tufafin na dabam, Ahmad ba zai min wannan lamanin ba, ko a da balle a yanzu da ba san yadda na baro shi da karfi ba, ba laifi ya nuna kulawarsa tun da har ya taimaka min ba dan shi ba wata kila da yanzu na zama gawa, domin ba kadan Kabir ya makure ni ba.
Tunanin nake ta yi ni kadai ina shafa wuyana da har yanzu ciwon yake min.
“Amman za su iya cewa ba za su yarda na daina saka kayan ba”
“Sai ki daina aikin”
“Idan na daina aikin da me zan kula da kaina? Kamin na samu wani aikin abu mai wahala, kuma ka san bana da mai taimakona a yanzu sai Allah”
“To sai ki samu miji ki yi aure, ki rike Namra da Amal Aiman da Adnan kuma ki maidasu gurin Babansu.....”
Kai tsaye ya fada min maganar nan ba tare da ya kalleni ba. Wani irin kallon mamaki nai masa, ban yarda daga bakinsa kalaman nan suke fitowa ba, sam ban yarda Abdallah na ne ba, taya zai min wannan maganar me yake nufi da ni? To sai ki fitar da miji ki yi aure...... Kalmarsa na ta maimaita min kanta a cikin kaina.
“Kalmar ka ta min nauyi Abdallah, tana kokarin rikecewa, ban gane komai ba”
Ajiyar zuciya ya sauke ba tareda ya kalleni ba ya ce.
“Har gobe ina sonki, har gobe ina kishinki, har gobe ina tausayinki ki saka wannan a zuciyarki, kuma wannan kaddara ta ce zan mutu da sonki.... Na sani kuskure ne na so matar yayana bayan ya rabu da ita, sai dai sonki ya dade a zuciyata tun kamin ki auri dan uwana, kin riga kin lalata komai Halima, Hajiya ta min katanga tsakanina da ke....”
“Har da aurena....?”
Na tambaya murya na rawa, idanuwana kuma suka soma aikinsu.
“Taya kike tunanin samun farinciki a auren da uwa bata so? Dan'uwa baya so? Da wane irin ido za mu kalli al'ummarmu? Zan mutu da kaunarki Halimatu wannan ita ce kaddarata.....”
Ban taba jin abu marar dadi irin na yau ba, Abdallah be taba fada min wata bakar magana ba irin yau, gaba daya sai na nemi farincikina da kuzarina na rasa, wani irin bakinciki ya cika min zuciya.
“Sauke ni a nan”
Na fada ina kawarda fuskata, ba musu ya faka motarsa gefen titi ni kuma na bude na fita, ina jikin babu kwari kamar na fadi. Key yai ma motarsa ya kara gaba ya bar ni a gurin tsaye ina hawaye.
“Shiyasa ya daina kula ni? Miyasa na auri Abdulhamid tun farko? Miyasa tunani be bani Abdallah ba sai a yanzu? Miyasa kaddara take min haka? A lokacin da ya kamata ba jidadi sai wata matsalar ta saka ni a gaban? Gaba daya ban san jindadi a rayuwata ba....”
A dole ya faka motarsa gafen titi, slowly ya dauke hannunsa daga idon da ke masa wani mugun zugi, ji yai idaniyar ta cika da abu mai kauri shi ba hawaye ba kuma ba ya san jini ne har sai da ya duba hannunsa. Jini a ciki kuma shine yake cika masa idon har baya gani da idon daya.
Lumshe idanuwan yai duka biyu yana sauraren yadda zugin yake shigar masa har cikin kansa, a rufe da idon ya saka hannun aljihu ya dauko wayarsa sai a lokacin yai kokarin bude idon daya yana duba iPhone dinsa wacce ta gama daukewa dip, sakamakon ruwan da ta sha, ba wayar kadai ba tufafin jikinsa ma sun gama jika seat dinsa balle kuma wayarsa.
Iskar bakinsa ya bushar yanzu be san yadda zai yi ya kira Doc Nura ba balle yaji idan ma yana gari ko yana asibitin ko gida, daman can a tsarinsa be yarda wani likitan ya duba shi ba sai family doc su, domin ya yarda da aikinsa hundred percent.
“Ba ma ita ce mahaukaciyar ba ni ne mahaukacin, taya zan shigar mata fada? Fadan ma da mahaukaci dan'uwanta? Matar da ta kashe min yarinyar? What's is wrong with me?”
Ya fada yana jin haushin abunda ya aika..
“Bata ma tsaya ta dubani ba fa sai kawai ta gudu, idan ma kashe ni zai yi ita dai ta tsira, mahaukaciyar banza i hate her”
Ya sake fada cikin fusata yana cizon bakinsa. A gurin ya tsaya har sai da ruwan suka dauke gaba daya sannan ya karasa tukin zuwa gida kamin ya isa har wani jiri yake ji cikin kansa.
“Ai I'm human being be kamata ina gani ayi kisan kai ba, shiyasa na taimake ta, amman yanzu na gano matar nan bakincikina take so take ta illatani bayan ta kashe min ya, be m kamata na barta tana aiki a kamfani na ba ai”
Shi kadai yake ta magana da kansa har ya faka motarsa a harabar gidan, yana kokarin bude motar ya fita ya tambayi kansa.
“Ko ma miya kai ni fada da mahaukaci? Da mahaukaci da mahaukaciya suna fada ni mai hankali miya kai ni ciki?”
After ya fito daga motar ya bawa kansa amsa.
“Kaddara.... ”
Part dinsa ya wuce, yana shiga ya fara ziyartar bandakin ya wanke fuskarsa, ya saka tissue yana tare jinin a hankali sannan ya dawo dakinsa ya dauko dayar wayarsa da ke gida yana kokarin kiran Doc Nura.
“Hasara nawa ga saka ni a yau? Ta saka na jika tufafina ga idona daya ga phone dina.....”
Wani irin haushinta ne ya kara cika msa zuciya. Sai da ya tabbatar Doc Nura na aibitin sannan ya canj tufafin jikinsa ya dauko key din wata motar ya fice ba tare da ya leka part din Hajiya ba, domin baya son ya tashi hankalinta.
A asibiti babu kalar dariyar da Doc Nura be msa ba.
“To kai yanzu miya kaika raba fada da mahaukaci? Ai gashi an bak tukuici”
“You make me hate her more”
“Wai wacece wannan?”
“Wata mahaukaciya ce mai ruwan masu hankali”
Ya hada fuska babu annuri can kuma yai murmushi.
“Ita ma fa taji wuya, ba da wasa ya moreta ba”
Dadi yaji tun da ita ma ta ji wuya, but maganar Allah shi yafi kowa shan wuya tunda shi be shi yaja mahaukacin ba.
Bayan Doc ya duba idon ya bashi maganin na sha da shafawa a idon ya kuma fada msa yadda zai kula da ido. After ya dawo gida ya kira shiga part dinsa ya kiran Yunus.
“Yu akwai wani mahaukaci da ke kusa da kamfanin mu, daga hannun dama gurin wani shagon kwano, za ka iya gane shi?”
Sai da Yunus yai tunani sosai sannan ya amsa masa da.
“Yes na gane shi kullum nn yke zama”
“Ka sa a dauke shi a kai shi gidan mahaukata”
“Why?”
“Why? Ya zan baka umarni ka tambayeni why?”
Ya amsa a fusace, kamar Yunus din ba abokinsa ba ne, saboda yau yana cikin zafin kai. Bayan ya kashe wayar yaje gaban madubi yan duba idon, idonsa daya yayi kwancin jini a ciki gaba daya gefen idon ya kumbura, abunka da farin mutun har wani ja gurin yai.
“Ina zaman zamana ta ja min masifa.....”
Ya karasa maganar ta tari sai jini ya biyo baya, daman haka yake yanzu da ransa ya bace sai ya fada tarin jinin sai ciwon kirji.
Toilet ya nufa aman jini yai ba kadan ba, shi kanshi sai da abun ya dan tsorata shi, har yana zargin wata kila saboda ya sha ruwan sama ne abun ya kara hade masa, wanka yai sannan ya dawo dakinsa ya sha maganinsa ha kwanta.
Sai 4:21 ya farka, sallah ce abunda ya fara gabatarwa sannan ya duba idon nasa kamin ya nufi part din Hajiya. Tana ganinsa hankalinta yai mugun tashin musamman idon nasa wanda ta hango jan jini a ciki.
“Miya same ka Gwarzo?”
“Hadarin nan ne da ya taso ina kokarin shiga, mota sai kasa ya shigar min ido”
“Wannan ba kasa ba ne, hannu ne ga kwancin shi nan a idonka, kaga ni ko shiyasa bana son kana zuwa kana dadewa a waje, na sha fada maka da kun gama aiki ka rika dawowa gida, na san halinka da zuciya wata kila kaje ka bugu wani ya rama”
Hannu ya kama yana kokarin zaunawa da murmushi a fuskarsa.
“Haba Hajiya ai na girmi wannan, Wallahi kaddara ce kawai amman In-Sha-Allah ba zai sake faruwa ba”
“Bari na kira Doc Nura”
“Naje gurinsa ya bani magani ya duba idon”
Sam bata yarda ba har sai da ta kira shi da kanta tai magana da shi ya tabbtar mata da cewar ya dubashi sannan hankalinta ya kwanta.
“And daga yau ba zaka je aiki ba sai nan da one week”
Da sauri ya kalli Hajiyarsa yana sakin baki.
“Amman Hajiya kin san idan ba da ni ba wani abun ba zai yiyu ba”
“Doka ta ce wannan”
Ta fada fuskarta babu alamun wasa.
“Yaro ba san ciwon kansa ba, sai idan ana nuna maka abu kace kai ba yaro ba ne”
Rasa yai abunda zai ce mata, ba zai iya karya dokarta ba, kuma ba zai so fashin zuwa aiki ba, zai iya amfani da bakin gilashi ya rufe idonsa.
“Idan an yi magariba ka kwanta karka tashi sai an yi isha'i, zan dafa maka carrot da allayau da wake yanzu suma suna gyara ido”
A dolen dolensa ya amsa mata da okay, ta tashi ta shiga kitchen da zimmar dora masa girkin, shi kuma ya bita da kallo yana ta tunanin randa Hajiya zata yarda da cewar ya girma san ciwon kanshi.
HALIMATU POV.
A hankali na kalleshi, fuskarsa a hade take sam babu alamar wasa a umarninsa. Na sani ba lallai ne su yarda su canja min aiki ba, balle kuma har su yarda na rika saka wasu tufafin na dabam, Ahmad ba zai min wannan lamanin ba, ko a da balle a yanzu da ba san yadda na baro shi da karfi ba, ba laifi ya nuna kulawarsa tun da har ya taimaka min ba dan shi ba wata kila da yanzu na zama gawa, domin ba kadan Kabir ya makure ni ba.
Tunanin nake ta yi ni kadai ina shafa wuyana da har yanzu ciwon yake min.
“Amman za su iya cewa ba za su yarda na daina saka kayan ba”
“Sai ki daina aikin”
“Idan na daina aikin da me zan kula da kaina? Kamin na samu wani aikin abu mai wahala, kuma ka san bana da mai taimakona a yanzu sai Allah”
“To sai ki samu miji ki yi aure, ki rike Namra da Amal Aiman da Adnan kuma ki maidasu gurin Babansu.....”
Kai tsaye ya fada min maganar nan ba tare da ya kalleni ba. Wani irin kallon mamaki nai masa, ban yarda daga bakinsa kalaman nan suke fitowa ba, sam ban yarda Abdallah na ne ba, taya zai min wannan maganar me yake nufi da ni? To sai ki fitar da miji ki yi aure...... Kalmarsa na ta maimaita min kanta a cikin kaina.
“Kalmar ka ta min nauyi Abdallah, tana kokarin rikecewa, ban gane komai ba”
Ajiyar zuciya ya sauke ba tareda ya kalleni ba ya ce.
“Har gobe ina sonki, har gobe ina kishinki, har gobe ina tausayinki ki saka wannan a zuciyarki, kuma wannan kaddara ta ce zan mutu da sonki.... Na sani kuskure ne na so matar yayana bayan ya rabu da ita, sai dai sonki ya dade a zuciyata tun kamin ki auri dan uwana, kin riga kin lalata komai Halima, Hajiya ta min katanga tsakanina da ke....”
“Har da aurena....?”
Na tambaya murya na rawa, idanuwana kuma suka soma aikinsu.
“Taya kike tunanin samun farinciki a auren da uwa bata so? Dan'uwa baya so? Da wane irin ido za mu kalli al'ummarmu? Zan mutu da kaunarki Halimatu wannan ita ce kaddarata.....”
Ban taba jin abu marar dadi irin na yau ba, Abdallah be taba fada min wata bakar magana ba irin yau, gaba daya sai na nemi farincikina da kuzarina na rasa, wani irin bakinciki ya cika min zuciya.
“Sauke ni a nan”
Na fada ina kawarda fuskata, ba musu ya faka motarsa gefen titi ni kuma na bude na fita, ina jikin babu kwari kamar na fadi. Key yai ma motarsa ya kara gaba ya bar ni a gurin tsaye ina hawaye.
“Shiyasa ya daina kula ni? Miyasa na auri Abdulhamid tun farko? Miyasa tunani be bani Abdallah ba sai a yanzu? Miyasa kaddara take min haka? A lokacin da ya kamata ba jidadi sai wata matsalar ta saka ni a gaban? Gaba daya ban san jindadi a rayuwata ba....”