← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 136

Sashe 17

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da gangan yake yai magana ya yi shiru yana ta sauraren yadda numfashinta ke fita fuskarsa na yalwantuwa da murmushin da shi kadai ya san sikarsa, bayan ta kashe wayar ya sake kira sallamar da tai masa ta saukar masa da natsuwa da kwnaciyar hankali daman can muryarta kawai yake son ji, domin ba shi da wani abun da zai ce mata, bayan son yai mata jajen ɓarin da tai ta waya, ɓarin kuma ba karamin dadi yai masa ba, domin ya kusanto masa da nesa kusa zuciyarsa na raya nasa a yanzu yana cikin ko wane mataki da zai iya nunawa Halimatu soyayyah, domin bata da auren a yanzu kuma ta cika idda indai har jinin ya tsaya mata. Kansa ya daga sama yana kallon tauraren da sukai ma sararin samaniya ado. Sannan ya maida wayar aljihunsa tare da zuba duk hanneyensa aljihun wandon, Halimatu ba zata so shi ba, ba zata taba amincewa da shi kai tsaye ba, domin yayi kuskuren nuna mata kauna a lokacin da take da igiya uku ta aure akanta har ta koma biyu har da zama daya, shi yake yawan fada mata mijinta yayi kaza ya yi kaza, yana yawan nuna mata Aminu ba irin mijin daya dace ta aura ba ne, ya dade yana jira zuwan wannan ranar ya dade yana addu'ar Allah ya raba auren Aminu da yar'uwarsa Halimatu saboda kawai shi ya aureta, yana ji a ransa kuma yana yawan rayawa a zuciyarsa cewar shi kadai ya dace ya zama mijin Halimatu, domin shi ne mutumen da zai iya nuna mata kauna zallarta ya kare mutuncinta ta martaba, and he know exactly how to lighten the candle of happiness in her life. Tun daga lokacin da ya dawo kasar nan tare da iyalinsa ya kyalle ido ya ga Halima sai Allah ya dauki sonta mai tsanani ya saka masa, har ya zama bashi da sukuni da walwala idan ban ganta ba ko be ji daga gareta ba, tun yana kokarin cire abun a zuciyarsa ya kawarda komai har ya gagareshi, har yake ji da ace ya san lokacin da take budurwa ko kuma yayi arba da ita tabbas da Halimatu bata da wani mijin bayan shi, domin tana da siffar da yake so a jikin mace komai na rayuwarta burge shi yake, the way she dressed, yadda take tafiyarda rayuwarta ga hakuri da kawaici ga magana ma so calmly, even simple makeup din da take burge shi yake.
Daga lokacin da ya gano kalar mijin da take aure kuma sai tausayinta ya samu muhalli a zuciyarsa, kuma ya samu makamin yaki da igiyar aurenta.

Ba abu ne mai sauki Halimatu ta karba tayinsa a yanzu ba, shi kansa ya sani domin haka ba zai yi kuskure nuna mata haka a yanzu ba ko kuma furta mata kalma so ko aure a yanzu ba, duk kuwa da kasancewar ta dade da jin daga gareshi saboda ya fada mata ba daya ba ba biyu ba cewar yana sonta yana kaunarta a lokacij da take da igiyar auren a akanta har take masa kallon mahaukaci ko kuma marar tunani, wannan dalili ya saka Halimatu tsanarsa fiye da kowa a familynsa.
Ba irin wannan lokacin ya kamata ya nuna mata so ba, wata kila ma bata sha'awar auren a yanzu, sai dai ya shirya nuna mata kulawa da kwantar mata da hankali da kuma kaunar yaranta.

“Daddy ba zaka shigo ba?”

Juyowa yai yana kallon yarsa Suhaima fuskarsa dauke da murmushi, ya kai hannunsa ya daga sama.

“Eyyyy ba ki kwanta ba Mamana?”

“Yes mu na ta kallo da Aiman, amman kowa yayi bachi sai ni da kai da Aiman muka rage”

“Okay je ciki ina zuwa”

Ya fada yana sauketa kasa sai ta juya da gudunta ta koma ciki, shi kuma ya sake ciro wayarsa sai dai wannan karon ba Halimatu ya kira ba Hajiyarsa ya kira duk kuwa da bashi da tabbacin cewar zata dauka wata kila ma ta yi bachi. A mamakinsa sai tai picking call din da muryarta radau babu alamun bachi.

“Hajiyata ba ki kwanta ba?”

“Ban kwanta ba Husaini kai me kake a farke?”

Jimmm yai na wani lokacin sannan ya ce.

“To ni ma dai ba zan iya fada ba for now, amman dai na kira na fada miki cewar Halima ta yi miscarriage ya kamata ki dubata gobe inda hali, kin ga ko sakin da akai mata Hajiyata ba ki je kin mata jajaye ba”

Daga dayan bangaren Hajiya tai murmushi mai sauti sannan ta dora da.

“Zanje gobe In-Sha-Allah shikenan? Jikin nata dai da sauki ko?”

“Ban sani ba, amman naje dazun ban tararda ita ba wai tana asibiti ni kuma bana son su fara zargin wani abun ne shiyasa ban je ba, amman ni ma gobe zanje ma dubata”

“To sai ka biyo ka dauke mu mu tafi ai”

“Aa Hajiyata zuwanki dabam na Abdallah dabam”

Ya fada da murmushi a fuskarsa sannan yai mata sallama ya sauke wayar, fira da mahaifiyarsa ko yayansa na daya daga cikin abunda yake saka shi ciki nishadi da farinciki ko da kuwa yana cikin damuwa ne. Juyowa yai ya nufo balcony ya tura kofar falon ya shiga. To His surprise sai ya samu uwargidansa tsaye jikin window dakin tana kallon waje sai dai shigowarsa yasa ta juyo ta da dubanta gurinsa. Ya dan wara ido yana murmushi daya saba yi mata.

“Suhaima ta ce kina bachi”

Ta wani marairaice kamar karamar yarinya marar.

“Taya zan iya bachi Doc be kusa da ni, na yi na dan guntun lokaci sai ya farka bachi ma ba dadi”

Murmushi yai ya katsa kusa da ita yana mai jin son uwargidan har cikin ransa, ya kai hannunsa ya rumgumeta ta baya ya dora kansa saman wuyanta.

“That's right Teema”

Ta yi saurin juyowa ta kalleshi.

“Teema kace fa?”

“Eh ba sunanki ba ne?”

“Amman ai ba haka kake kirana ba sai dai ka ce min Baby ko Madam ko Mom Suhaima”

Dariya yai ya jiyarda ita ya sake rungumeta ta baya.

“To Baby yau yan tsokarna sun motsa ne shiyasa”

“Da wa kake waya?”

“Da Hajiya”

“Amman ka dade a waje fa”

Ya sauke hannayensa daga rikon da yai mata ya saka hannayensa aljihu.

“Ina ta tunanin mutuwa ne, mutuwa kawai ake a yanzu any how abun har tsoro yake ba ni, ina ta tunanin makomarmu ne”

Ya fada yana hade yawun bakinsa domin shi ma yasan karya yai. A take Teema ta bata fuska damuwa ta bayyana a fuskarta jin furuncin daya fito daga bakin mijinta, hakika mutuwa abun tunawa a ko wane dare ko dakika sai dai ba kowa ne ke tunawa da ita ba sai masu imani da tunanin ya goben su zata kasance.

“Allah dai ya saka mun cika da imani, nima abun na taba ni Wallahi”

Ta fada bayan ta sauke ajiyar zuciya. Hannunsa ya kai ya riko hannunta ya nufi hanyar dakinsa da ita.

“Ina Aiman? Suhaima tace sune kawai ba su yi bachi ba”

“Na saka su bachin dole ai, kun zauna gaban tv kamar a gurin za su tabbata”

Hannunta ya saki ya nufi dakin yaransa, a bakin kofar dakin ya tsaya yana kallon Suhaima da Lubna sai kuma yayan Halimatu wato Namra da Aiman da Adnan, a ransa ya rika kwatatta yadda abun zai burge idan da ace shi Halimatu ta haifawa yaran nan gaba daya musamman Aiman da Adnan domin shi Allah be ba shi yaya maza ba, yan mata biyu matarsa ta haifa masa. Zuwa tai ta tsaya bayansa tana kallon yaran.

“Minene?”

“Ba komai”

Ya kai hannu ya janyo kofar dakin sannan ya nufi dakinsa Teema na biye da shi a baya.

HALIMATU POV.

Karfe takwas na safe kofar shiga dakin da Kabir yake tai min, domin na kwana da shi a raina da na farka kuma sai na ji bana bukatar ganin kowa sai shi hakan yasa ban wani tsaya karyawa ba na nufo asibitin daman can abinci be dame ni balle kuma yanzu da damuwa ta zame min ci da sha, kuma ta zame min abokiyar fira.
Ba ni kadai aka hana shiga ba, har da sauran masu ganin marasa lafiya da masu kawo abinci balle kuma ni da ban kawo komai ba. Muna tsaye a gurin har kusan tara da wani abu ba bar mu mum shiga ba sai dai an bar masu dauke da abinci sun shiga, ni kan sai na samu guri kusa da inda kofar take na zauna, na bawa kofar baya zaman jiran gawon shanu domin ban san lokacin da za a bada damar shigar ba, sai dai bana jin a yau zan wuni ban saka Kabir a ido ba ba dan komai ba sai dan damuwa da halin da yake ciki a yanzu wanda silata ne komai ya afko. Ji nai a dabani da wani hannu mai sanyi da alama mamallakin hannun ya taba ruwa mai sanyi ne ko kankara, ashe mamallakin hannu mace ce ba namiji ba ban fahimci hakan ba har sai da na juyo na kalleta na kuma tabbatar da macece ta hanyar sautin muryarta.

“Kamar Haima?”

Gabana ya fadi har na kasa amsa mata da eh ni din ce ko kuma a a ba ni ba ce, domin mutun biyu ne suke kirana da wannan sunan a duk fadin duniyar nan. Daga Abdulhamid sai Kabir, ba kuma zan ce a gurin Abdulhamid ta samu sunan ba, domin be taba kirana a gabab kowa da wannan lakanin ba, mutumen da be yarda na bayyana soyayyarsa ba taya zai fadawa wata ya taba kirana da wannan sunan a lokacin da na ke budurwa.

“Har na wuce ki na dawo saboda kin min kama da Haima, kuma wannan shirun da kikai ya tabbatar min da cewar ke ce Haima! matar da Kabir ya cika wayarsa da hotunanta kuma matar da aka ce ita yaje siyo ma abinci wannan hadarin ya same shi, wani abun mamaki kuma jiya da kika kira wayarsa sunanki yai appearing da Spacial Haima”
Chapter 17 · 0% Book details