Sashe 120
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wasawasa aka kwashe kwana takwas ban saka Ahmad a ido ba hakan kuma ba karamin damuwata yai ba, domin sai na ji kamar na saba da shi a kullum ne, zai kira ni a waya da safe da rana haka ma da dare amman hakan be wadatar ta da ni ba. Ya aiko an karbi list din duk abunda na rubuta an siyo har ma da wanda ban rubuta ba duk an siyo kuma ba kadan ba da yawa aka siyo wanda zai dauke mu tsawon lokaci muma amfani da shi.
A iya sanina yadda Ahmad yake nuna min kauna kamar ba zai iya kwana biyu be saka ni a ido ba balle kuma yanzu da nake matarsa, amman miyasa ya dauke min kafa tun daga wacan ranar? Ko dai shi ma mahaifiyarsa bata so? Ko kuma wani abun ne? Ina tsaka da tunanin nan wayata tai ringing ganin kiransa ne yasa nai hanzarin dauka.
“Hey Babe na ykk”
“Ina lafiya”
“How are my kids?”
“Suna lafiya”
“Na kira na ji muryarki, kuma na miki albishir cewar Kabir yana ta samun sauki ana tunanin end of this month ma su sallame shi, domin an masa tiyata an kwashe jinin daya taba kwakwalwarsa yanzu sun dora shi akan magani ne”
“Ma-sha-Allah Allah ya saka da alheri”
Na fada cikin rashin far'a kamar ba labarin nake son ji ba, ban san abunda ya hana ni jindadi ko murnar samun lafiyar Kabir ba bayan kuma na dade ina fatar samun haka.
“And... I think gobe ko jibi zan je United Kingdom wato London for some works”
Na y shiru ban ce komai ba, domin ban san abunda zan ce ba gaba daya jikina sai ya ba ni kamar ba lafiya ba.
“Idan akwai abunda kike bukata ki fada min”
“Kai nake bukatar gani Ahmad i need to see you”
Daga can cikin wayar ya jiyo sautin murmushinsa mai kama da dariya.
“Wow i got lucky Matata tana so na da yawa haka nan, idan na dawo zan zo In-Sha-Allah”
“Ba zaka zo mu yi sallama ba?”
“Ba zai yiyu ba ne yanzu haka ina Abuja, daga can zan wuce i'm ban fada miki ba, but karki damu next time tare za mu tafi In-Sha-Allah”
Jin na yi shiru yasa shi cewa.
“Kin ji Baby na? Are you there”
“Allah ya tsare”
“Amin i love you”
Na aje wayar ina ta kallon screen din, idan har da gaske wani aikin ne zai kai shi da sai yaje da ni, ko dai shi ma mahaifiyarsa ta masa katanga da ni ne? Ko ba da amincewarta ya aure ni ba? Tun da akai auren ba ban taba gaisawa da ita ba, ni kam dai ina rashin dace da in-laws, but wait miyasa zan zargi mahaifiyarsa? What if ba shi da lafiya? Domin a duk lokacin da nake waya da shi ina jin muryarsa ba a yadda na saba jinta ba. A take gabana ya fadi hankalina yai mugun tashin da sauri na dauki wayar na aika masa da kira amman haka tai ringing har ta katse be dauka ba.....
__________________
Ina yan Team Kabir kun ji ya fara jin sauki 💃
Jiya wata yar Team din Abdallah tana ta min rankwashi a kai 😢😪
To ai ba san maci tuwo ba sai miya ta kare 😥🙄
*Where are are the classy ladies 🤔 mata yan kwalissa ga awwaba scent tazo maku da hadadun turarukan wuta humra body oil turaren jiki na tsuguno da kayan gyaran jiki kaman dilka scrub organic soap 🧼 da sauransu akan farashi daidai aljihu say no karnin da warin damshi na lokacin damina zaaiya samunmu a wannan lqmbobin 09137294470 08034236800*
7/21/21, 11:10 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
5️⃣9️⃣
Kwance take a dakinta tana kallon windows din dakinta da suke bude, pillow na rumgume a kirjinta babu abunda ke fita daga idonta sai hawaye masu zafi.
Mai aikinsu ce Hindatu ta turo kofar dakin ta shigo da sallama.
“Assalamu Alaikum, Siyama Hajiya na nemanki”
“Ki ce zan zo”
Ta amsa ta ba tare da ta juyo ta kalleta ba. After like one hour Hajiya ta turo kofar dakin ta shigo.
“Siyama....”
Sai a lokacin ta fara kokarin yin kamar bachi take, hakan yasa Hajiya ta karasa kusa da gadon ta zauna leken fuskarta da hawaye ya gama yi mata kwalliya.
“Miye abun kuka kuma? Me yake damunki?”
Juyowa tai da kyau ta kalli Hajiya wasu hawayen na cika mata ido.
“Hajiya...”
Sai kuma tai shiru ta tashi zaune tana matsar yatsun hannunta.
“Ba ki fito kin ci abinci ba, ko yau ba kya zuwa makarantar ne?”
“Hajiya bana son na sake rasa kowa”
Ta fada cikin hawaye.
“To wa za ku rasa?”
“Ban sani ba, amman yanzu idan ciwo ya kama wani a cikinmu sai na rika ganin kamar zan rasa shi ne, i don't want to be alone....”
Ta fashe da kuka, tana kwantawa jikin Hajiya.
“Babu abunda zai samu yayanki zai samu sauki In-Sha-Allah, ki daina tada hankalinki kin ga nima kina daga min nawa, da kuzari da karfin zuciya da nake da shi sai ki sa ya karye”
“Hajiya ina jin tsoro”
“Ki daina kawai ki yi masa addu'a, ki tashi ki wanke bakinki ki fito ki yi breakfast”
Ta gyada kai tana share hawayenta Hajiya ma ta yi saurin tashi tana tare hawayen da ke son zubo mata, cikin rashin kuzari ta fita daga dakin ba Siyama kadai ba ita kanta abun ya bata tsoro jin cewar ba a ga komai ba kuma gashi yace yana jin ciwo, tun daga lokacin da ciwon ya same shi baya iya komai daga zaune sai tsaye sai kwance wani lokacin kuma ya kan dan zagaya cikin asibitin amman fa sai idan am masa allurar kashe ciwo, ga shi baya wani iya cin abu mai nauyi daga lemu sai ruwa sai tea shi ma can ba a rasa ba, sai dai tana addu'a kuma tana fatar idan an je check up din nan a gano matsalarsa. A dinning din take zaune amman ta kasa taba komai balle ta ci kamar ba ita ta dafa abun karyawar ba, yadda yake fito daga part dinsa ya zo part dinta su karya ko kuma idan ba shi da lokaci sai ya dauki breakfast din ya tafi da shi ko mug ne abunda yafi tsaya mata a rai, yau kusan 7 days yana asibiti mutumen da bata bari yai nisa da ita, and the most saddest part is aurensa aka daura yana cikin farinciki wannan abun ya same shi.
A hankali ta sauke ajiyar zuciya ta dora hannayenta saman dinning din ta dafe kanta kamin ta kike tsaye ta nufi upstairs dan jin tai bata bukatar cin komai.
HALIMATU POV.
Ba karamin tsoro ne ya kama ni ba, na san ban tana kiran Ahmad ba tun da nake a rayuwata, amman mi zai saka yanzu na kira shi yaki dagawa? Amman ya kamata nai masa uzuri, after like seven minutes a sake gwadawa still be daga ba na sake gwadawa be daga ba haka nai ta yi har kusan 20 miss calls amman be yi picking ba, a lokacin ne fargabana ya karu tsoro ya auri zuciyata na fara sake sake kala kala, ji nai bana da natsuwa kwata kwata a rayuwata jikina ya bani cewar akwai abunda Ahmad yake boye min.
Tashin nai na shiga dakina na canja tufafin jikina na saka wata rigar yadi na dauki medium veil na yafa na saka talkamina na dauki yar purse dita cikin dabara na fice na bar gidan domin na san idan nace zan fadawa Mama zata iya cewa ba zan fita ba tare da izinin mijina ba, tun da ba fada mata zan yi gurinsa zan je ba, ina tafe ina waige waige kar wani dan gidan mu ya gan ni kamar wata marar gaskiya, Allah ko ya bani sa'a har na tari napep na hau ban hadu da kowa ba, zuciyata bata raya min na je ko'ina ba sai gidansu Ahmad, duk kuwa na san hakan be dace ba amman ba ni da wata mafita wacce ta fi wannan ko dan samun natsuwar zuciya dole naje na ga halin da yake ciki, tun da yanzu yamma ta yi ba na san baya kamfaninsa.
Sai da mai napep din ya kai ni har kofar gidan na sallame shi sannan nai knocked din gate din gidan cikin sa'a kuwa mai gadin ya bude min, sai da muka gaisa da shi sannan na tambaye shi ko masu gidan suna ciki, ya amsa min da suna ciki har ma da bude min kofar, sai da na doshi harabar gidan sannan na soma tambayar kaina to idan na shiga ciki me zan fada musu? Idan ma mahaifiyarsa ce tai masa katanga da ni fa? Kuma gashi na shigo har cikin gidan anya shi ma kansa zai jidadi? No wait idan ma babu duk wannan anya ban yi rashin kunya ba na tukari idansu kai tsaye? A take duk na ji wani iri hakan yasa ban karasa ba na juyo na dawo gurin mai gadin.
“Dan Allah Malam ko zaka shiga ciki kace ana sallama da Ahmad?”
“Wai Alhaji... Alhaji ai.... ”
Sai kuma yai shiru ya kalleni.
“To bari a fada musu”
Ya nufi cikin gidan ni kuma na bude gate din daker saboda shegen nauyinsa na fita daga waje na tsaya, kamin ya fito har na matsu bugun zuciyata ya karu ga tsoro ga fargaba da tunanin rashin dacewar zuwana sai suka taru suka tsaya min a rai. A tsammanina Ahmad din zai fito ko mai gadin amman ga mamakina sai kanwarsa ta fito waton Siyama, tana ganina ta saki far'a ta karaso ta rike hannuna.
“Laaaaa In-law shine kika tsaya a waje"
Nima nai mata murmushin daya kasa boye damuwata cike da kunya na ce.
“Bana son shiga ciki ne”
Sai taja hannuna tana fadin.
“Dan Allah shigo ciki magana, sai ku gaisa da Hajiya”
“A a dan Allah ki bari, ba sai na shiga ciki ba amman Ahmad na zo....”
Sai kuma kunya tasa na kasa karasawa, sai tai murmushi.
“Ai baya nan ya tafi jos.....”
Da sauri na kalleta domin ni ba jos yace min ba.
“Jos kuma?”
A iya sanina yadda Ahmad yake nuna min kauna kamar ba zai iya kwana biyu be saka ni a ido ba balle kuma yanzu da nake matarsa, amman miyasa ya dauke min kafa tun daga wacan ranar? Ko dai shi ma mahaifiyarsa bata so? Ko kuma wani abun ne? Ina tsaka da tunanin nan wayata tai ringing ganin kiransa ne yasa nai hanzarin dauka.
“Hey Babe na ykk”
“Ina lafiya”
“How are my kids?”
“Suna lafiya”
“Na kira na ji muryarki, kuma na miki albishir cewar Kabir yana ta samun sauki ana tunanin end of this month ma su sallame shi, domin an masa tiyata an kwashe jinin daya taba kwakwalwarsa yanzu sun dora shi akan magani ne”
“Ma-sha-Allah Allah ya saka da alheri”
Na fada cikin rashin far'a kamar ba labarin nake son ji ba, ban san abunda ya hana ni jindadi ko murnar samun lafiyar Kabir ba bayan kuma na dade ina fatar samun haka.
“And... I think gobe ko jibi zan je United Kingdom wato London for some works”
Na y shiru ban ce komai ba, domin ban san abunda zan ce ba gaba daya jikina sai ya ba ni kamar ba lafiya ba.
“Idan akwai abunda kike bukata ki fada min”
“Kai nake bukatar gani Ahmad i need to see you”
Daga can cikin wayar ya jiyo sautin murmushinsa mai kama da dariya.
“Wow i got lucky Matata tana so na da yawa haka nan, idan na dawo zan zo In-Sha-Allah”
“Ba zaka zo mu yi sallama ba?”
“Ba zai yiyu ba ne yanzu haka ina Abuja, daga can zan wuce i'm ban fada miki ba, but karki damu next time tare za mu tafi In-Sha-Allah”
Jin na yi shiru yasa shi cewa.
“Kin ji Baby na? Are you there”
“Allah ya tsare”
“Amin i love you”
Na aje wayar ina ta kallon screen din, idan har da gaske wani aikin ne zai kai shi da sai yaje da ni, ko dai shi ma mahaifiyarsa ta masa katanga da ni ne? Ko ba da amincewarta ya aure ni ba? Tun da akai auren ba ban taba gaisawa da ita ba, ni kam dai ina rashin dace da in-laws, but wait miyasa zan zargi mahaifiyarsa? What if ba shi da lafiya? Domin a duk lokacin da nake waya da shi ina jin muryarsa ba a yadda na saba jinta ba. A take gabana ya fadi hankalina yai mugun tashin da sauri na dauki wayar na aika masa da kira amman haka tai ringing har ta katse be dauka ba.....
__________________
Ina yan Team Kabir kun ji ya fara jin sauki 💃
Jiya wata yar Team din Abdallah tana ta min rankwashi a kai 😢😪
To ai ba san maci tuwo ba sai miya ta kare 😥🙄
*Where are are the classy ladies 🤔 mata yan kwalissa ga awwaba scent tazo maku da hadadun turarukan wuta humra body oil turaren jiki na tsuguno da kayan gyaran jiki kaman dilka scrub organic soap 🧼 da sauransu akan farashi daidai aljihu say no karnin da warin damshi na lokacin damina zaaiya samunmu a wannan lqmbobin 09137294470 08034236800*
7/21/21, 11:10 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
5️⃣9️⃣
Kwance take a dakinta tana kallon windows din dakinta da suke bude, pillow na rumgume a kirjinta babu abunda ke fita daga idonta sai hawaye masu zafi.
Mai aikinsu ce Hindatu ta turo kofar dakin ta shigo da sallama.
“Assalamu Alaikum, Siyama Hajiya na nemanki”
“Ki ce zan zo”
Ta amsa ta ba tare da ta juyo ta kalleta ba. After like one hour Hajiya ta turo kofar dakin ta shigo.
“Siyama....”
Sai a lokacin ta fara kokarin yin kamar bachi take, hakan yasa Hajiya ta karasa kusa da gadon ta zauna leken fuskarta da hawaye ya gama yi mata kwalliya.
“Miye abun kuka kuma? Me yake damunki?”
Juyowa tai da kyau ta kalli Hajiya wasu hawayen na cika mata ido.
“Hajiya...”
Sai kuma tai shiru ta tashi zaune tana matsar yatsun hannunta.
“Ba ki fito kin ci abinci ba, ko yau ba kya zuwa makarantar ne?”
“Hajiya bana son na sake rasa kowa”
Ta fada cikin hawaye.
“To wa za ku rasa?”
“Ban sani ba, amman yanzu idan ciwo ya kama wani a cikinmu sai na rika ganin kamar zan rasa shi ne, i don't want to be alone....”
Ta fashe da kuka, tana kwantawa jikin Hajiya.
“Babu abunda zai samu yayanki zai samu sauki In-Sha-Allah, ki daina tada hankalinki kin ga nima kina daga min nawa, da kuzari da karfin zuciya da nake da shi sai ki sa ya karye”
“Hajiya ina jin tsoro”
“Ki daina kawai ki yi masa addu'a, ki tashi ki wanke bakinki ki fito ki yi breakfast”
Ta gyada kai tana share hawayenta Hajiya ma ta yi saurin tashi tana tare hawayen da ke son zubo mata, cikin rashin kuzari ta fita daga dakin ba Siyama kadai ba ita kanta abun ya bata tsoro jin cewar ba a ga komai ba kuma gashi yace yana jin ciwo, tun daga lokacin da ciwon ya same shi baya iya komai daga zaune sai tsaye sai kwance wani lokacin kuma ya kan dan zagaya cikin asibitin amman fa sai idan am masa allurar kashe ciwo, ga shi baya wani iya cin abu mai nauyi daga lemu sai ruwa sai tea shi ma can ba a rasa ba, sai dai tana addu'a kuma tana fatar idan an je check up din nan a gano matsalarsa. A dinning din take zaune amman ta kasa taba komai balle ta ci kamar ba ita ta dafa abun karyawar ba, yadda yake fito daga part dinsa ya zo part dinta su karya ko kuma idan ba shi da lokaci sai ya dauki breakfast din ya tafi da shi ko mug ne abunda yafi tsaya mata a rai, yau kusan 7 days yana asibiti mutumen da bata bari yai nisa da ita, and the most saddest part is aurensa aka daura yana cikin farinciki wannan abun ya same shi.
A hankali ta sauke ajiyar zuciya ta dora hannayenta saman dinning din ta dafe kanta kamin ta kike tsaye ta nufi upstairs dan jin tai bata bukatar cin komai.
HALIMATU POV.
Ba karamin tsoro ne ya kama ni ba, na san ban tana kiran Ahmad ba tun da nake a rayuwata, amman mi zai saka yanzu na kira shi yaki dagawa? Amman ya kamata nai masa uzuri, after like seven minutes a sake gwadawa still be daga ba na sake gwadawa be daga ba haka nai ta yi har kusan 20 miss calls amman be yi picking ba, a lokacin ne fargabana ya karu tsoro ya auri zuciyata na fara sake sake kala kala, ji nai bana da natsuwa kwata kwata a rayuwata jikina ya bani cewar akwai abunda Ahmad yake boye min.
Tashin nai na shiga dakina na canja tufafin jikina na saka wata rigar yadi na dauki medium veil na yafa na saka talkamina na dauki yar purse dita cikin dabara na fice na bar gidan domin na san idan nace zan fadawa Mama zata iya cewa ba zan fita ba tare da izinin mijina ba, tun da ba fada mata zan yi gurinsa zan je ba, ina tafe ina waige waige kar wani dan gidan mu ya gan ni kamar wata marar gaskiya, Allah ko ya bani sa'a har na tari napep na hau ban hadu da kowa ba, zuciyata bata raya min na je ko'ina ba sai gidansu Ahmad, duk kuwa na san hakan be dace ba amman ba ni da wata mafita wacce ta fi wannan ko dan samun natsuwar zuciya dole naje na ga halin da yake ciki, tun da yanzu yamma ta yi ba na san baya kamfaninsa.
Sai da mai napep din ya kai ni har kofar gidan na sallame shi sannan nai knocked din gate din gidan cikin sa'a kuwa mai gadin ya bude min, sai da muka gaisa da shi sannan na tambaye shi ko masu gidan suna ciki, ya amsa min da suna ciki har ma da bude min kofar, sai da na doshi harabar gidan sannan na soma tambayar kaina to idan na shiga ciki me zan fada musu? Idan ma mahaifiyarsa ce tai masa katanga da ni fa? Kuma gashi na shigo har cikin gidan anya shi ma kansa zai jidadi? No wait idan ma babu duk wannan anya ban yi rashin kunya ba na tukari idansu kai tsaye? A take duk na ji wani iri hakan yasa ban karasa ba na juyo na dawo gurin mai gadin.
“Dan Allah Malam ko zaka shiga ciki kace ana sallama da Ahmad?”
“Wai Alhaji... Alhaji ai.... ”
Sai kuma yai shiru ya kalleni.
“To bari a fada musu”
Ya nufi cikin gidan ni kuma na bude gate din daker saboda shegen nauyinsa na fita daga waje na tsaya, kamin ya fito har na matsu bugun zuciyata ya karu ga tsoro ga fargaba da tunanin rashin dacewar zuwana sai suka taru suka tsaya min a rai. A tsammanina Ahmad din zai fito ko mai gadin amman ga mamakina sai kanwarsa ta fito waton Siyama, tana ganina ta saki far'a ta karaso ta rike hannuna.
“Laaaaa In-law shine kika tsaya a waje"
Nima nai mata murmushin daya kasa boye damuwata cike da kunya na ce.
“Bana son shiga ciki ne”
Sai taja hannuna tana fadin.
“Dan Allah shigo ciki magana, sai ku gaisa da Hajiya”
“A a dan Allah ki bari, ba sai na shiga ciki ba amman Ahmad na zo....”
Sai kuma kunya tasa na kasa karasawa, sai tai murmushi.
“Ai baya nan ya tafi jos.....”
Da sauri na kalleta domin ni ba jos yace min ba.
“Jos kuma?”