← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 136

Sashe 1

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read



*⚠️ Ban yarda a canja min ko da harafi daya na littafin nan ba, balle kuma har a saffara shi a dora a Youtube ba tare da izinina ba, yin haka kan iya janyo wa mamallakin Channel din babbar matsala dan haka a kiyaye!*

_Hasbunallahu Wa Nimal Wakeel_

*GOBE NA...*
_My Tomorrow_

By Khadeeja Candy

Free Page 1️⃣

*GUSAU ZAMFARA STATE NIGERIA.*
*Gusau Rd/Sokoto Rd*

*_Jifatu Shopping Mall_*
  *_3:16pm_*

Madara ta fi komai yawa a cikin abubuwan da na siya, ba dan komai ba sai dan sanin cewa mahaifina ya fi bukatar tea fiye da komai a yanzu. Gwando daya na cika da siyayyar kayan ciye-ciye da tande tande sannan na dauki wani kwando na cika shi da da wasu abubuwa na bukatun yau da kullum kamar sabulun wanka da wanki da turare sai kuma omo.
Bakar abaya ce a jikina sai dan karamin mayafinta wanda hakan ya bani damar rika duka kwandunan na nufi gurin biya Amal na bayana rike da biscuit dinta. A saman dan teburin da suka tana dan lissafa kaya na dora kwandunan sannan na saka hannuna a jaka na ciro atm dina na rike a hannu ina jiran ya gama da wadanda suka gabana ya fara da ni sai na biya da pos din da yake gurin, domin na saba indai ban ciro albashi gaba daya idan na siye abu ina biya ne da atm.
Sai da ya gama da mutum biyu sannan ya fara da nawa, sai da ya gama lissafa komai kamin na mika masa kudin ya fara dauko leda yana sakawa, ni kuma a iya sanina idan kai siyayya a jifatu sai ka biya suke saka maka a leda su sallameka.

“Nawa ne?”

“Hajiya an biya”

Ya fada min yana ga aikin harhada min kayan a leda. A take gabana ya yanke ya fadi har sai da na dauki yan awanin sannan na sake tambayarsa.

“Waya biya?”

“Gashi can a waje”

Juyawa nai na kallin wajen sai n hango Abdallah tsaye jikin motarsa idonsa akan wayar da yake dannawa. Dauke kai nai na cigaba da kallonsa har ya gama saka kayan a leda sannan na mika hannu na karba.

“Thank you”

“No mune da godiya Hajiya”

Da duka hannayena na riko ledodin na nufo kofar fita Amal na rike da gefen rigata muka fito, ko da wasa ban kalli inda Abdallah yake tsaye ba balle har ya ga fuskata duk kuwa da na san hakan ba zai hana shi yi min magana ba idanya tashi.
Bakin titin na nufo ina ta tafiya ina sai jin maganarsa nai bayana.

“Ban biya kudin dan ki min godiya ba, kuma na san ba zaki min godiyar ba, amman ai ko kallona kya yi na dan ji sanyi ko?”

Tsayawa nai cak na juyo na watsa masa wata banzar harara fuskata a hade kamar bakin hadari. Sai dai da alama harar tawa dadi take masa domin murmushi ne ya cika masa fuska har ya cire farin gilashin idonsa yana kallona. Dauke kai nai na cigaba da tafiya sai jin nai ya riko hannun Amal wanda hakan yasa na juyo da sauri sai ganinsa nai yana danka mata kudi a hannu.

“Ku hau napep da wannan kin ji Amal nasan ko na ce na kai stubborn mother dinki a mota ba zata je ba”

Amal bata ce masa komai ba ta karbi kudin daman haka take indai kudi ne da biscuit bata kin karba ko a hannun waye, jan hannunta nai muka cigaba da tafiya.

“Yanzu na baro mijinki a can gurin damba area tare da abokansa da wasu mata”

Sake juyowa nai karo na biyu na dubeshi da duba na bakincikin jin kalaminsa da kuma na tsanar ganin fuskarsa.

“Miye ribar da zaka samu idan ka labarta min wannan? Kana tunanin zan yarda da kai? Mi zai saka mijina neman wasu matan banza a waje?”

“To ni ma dai shi na gani, namijin da zai aje mace kamarki mi zai saka ya nemi wasu a waje?”

“Baka tsoron Allah Abdallah saboda baka gudun taka dokarsa, kana isgili da ganganci ga dokokin aure da kumana Allah, shin zaka jidadi idan wani namijin ya kula matarka? Wani namijin ya iya furta wata mummunar kalma akanka gurin matarka? Kai baka kishin kanka? Daga yau karka sake yi min wata magana da ta shafi mijina ni mijina ba mazinaci ba ne, na lura kai baka san darajar aure ba kuma baka san kimar kanka ba balle har ka iya tsare mutuncin iyalanka”

“Na san darajar Aure Halimatu, na san martabar aure, kuma ina mutunta aure da duk wani mai aure, kawai dai ina son ki ne, ina son ki san kamanni da hallita suna canjawa amman zuciya bata taba canjawa, alakar da ke tsakanina da ke ba zata taba yankewa ba, ko bayan so ai ni dan'uwanki ne ko?”

“Ajinabi ba, kuma ina fatar ka san da hakan”

Ya gyada min kai yana murmushi. Ni kuma na juya na cigaba da tafiyata.

“Da ni nake da mace kamar ke ba zan bari ko tawaye na ya kalleta ba, balle kuma har wani namijin ya tsaya magana da ita, zan yi duk abunda zan yi na kare mutuncinta da martabarta”

Ban sake kulashi ba balle har na tsaya sake ce masa wani abun, na yi sa'a ina kaiwa titin na samu napep a take na daga mata hannu ta tsaya na shiga.

“Yan mangurora zaka kai ni”

“Dari biyu”

“Zan dai baka dari da hansi”

“To muje”

Sai da na fara saka ledodin hannuna na shigar da yana ta hudu wato Amal sannan shiga na zauna.

“Momy ga kudin”

Amal ta fada tana miko min kudin da Abdallah ya bata, karba nai na saka a jakata ina hade yawu, kamar hadin baki ina saka kudin karamar wayata tai ringing sai na fiddo hannuna tare da wayar ganin number surukata yasa ni saurin dauka.

“Assalamu Alaikum Hajiya”

“Na'am Halimatu kina lafiya?”

“Lafiya kalau Hajiya ya jikin?”

“Al-hamdulillah, na ce kin fadawa Aminu maganar kudin nan kuwa?”

“Eh Hajiya na fada masa”

“Idan ma baki fada masa ba ya kamata dai ki fada masa, har yanzu na ji shiru be ce komai ba ban sani ba ko baki fada masa ba, idan ma baki fada masa ba ya kamata dai ki fada masa yanzu, kuma izuwa yanzu ya kamata ace kina fahimtar cewar uwar miji ma kamar uwa ce, duk abunda ya shafe ni ya kamata ace kina daukarsa da muhimmanci”

“Wallahi na fada masa Hajiya, amman zan sake masa magana”

Bata ko bari mun yi sallama ba ta katse wayar, hakan kuma alamune da ke nuna cewar yau a fusace ta kirani. Haka na ke da yan'uwansa idan suna bukatar abu sai dai su kira su ce nai masa magana bayan ni kuma ba magana ta hake ji ba, mahaifiyarsa ma ta fi kusa da shi amman ita ma kanta sai dai tace na fada masa tana bukatar abu kaza da kaza, saboda gani suke komai na kame na mallake shi sai abunda na ce yake yi. Ko da yake shi ya nuna musu hakan domin a duk lokacin da suka bukaci abu ko da naira biyar ne sai yace balle nai magana da Halima, ganin hakan yasa suka dauki ido da baki suka dora min wai na mallake shi, ni kuwa nasan da zan samu mallakar kamar yadda suke zato da ba haka ba.
Har kofar gida mai napep din ya kai mu na fita na ciro kudinsa na mika masa sannan Amal ta fito tana bata fuska wai rana sai kace a kafa muka zo. Ganin motar Abdulhamit wato tawayen Abdallah fake gefen icen da ke kofar gidanmu ya tabbatar min da zuwansa, daman can ya kan zo jifa jifa ya gaishe da su Mama.
Ina gaba Amal na bayana tana kukan rana, gidanmu gidane mai yan mata da samari ina shiga yan matan gidanmu wato kanne waenda muke uwa daya uba daya da kuma waenda muke uba daya suka hau ihu da murna ganina.

“Oyoyo Anty Halima”

Da sauri kananna suka zo suka rika ledar hannuna, dayar kuma ta dauke Amal tai sama da ita tana dariya, daman haka gidan mu yake yana da wahala ka iya banbance yan dakin mu da waenda muke uba daya domin mu ba musan wani abu wai ubanci ba ko kuma yayan kishiya. Sai da na fara shiga dakin Inna na gaisheta sannan na nufi dakin mahaifiyata

“Maraba da Sadiya”

Cewar Mama da murmushi a fuskarta, ni kuma na zauna saman kujera ina mika mata gaisuwa tare da gaisawa da Abdulhamid.

“Yau kuma nan aka zo?”

“Eh Wallahi ya gida ya yaran?”

“Lafiya kalau”

“Yanzu ko na ke tambayarki aka ce kin kwana biyu ba ki zo ba”

“Wallahi yanzu na rage fitar nan sosai saboda abubuwan sun yi yawa ga hidimar yara ga zuwa gurin aiki idan na dawo kuma nai aikin gida, ba ni da hutu ne Wallahi”

“To Allah ya taimaka ni zan wuce”

“Tun yanzu”

“Tun dazu na zo fa, nan na ci abincin rana ma”

“To a gaishe da su Hajiya”

“Za su ji”

Ya mike tsaye yana ciro makullinsa a aljihu, banbancinsa da Abdallah kadan ne ta wajen hakoransa na gaba dayan ya dan kare kadan sai kuma yanayinsa da ba na Abdallah ba, amman kama iri daya ni kaina ba dan banbanci tufafi ba da motar da na gani a waje idan har na shigo be bude baki ya min magana ba zan iya cewa Abdallah ne.

Sai da Mama ta raka shi har gurin motarsa ta dawo, sannan take labarta min shinkafa ce ya kawo musu yar gobnati, daman haka familyn Baba suke suna da son zumuncin da son yi ma wanda ba shi da karfi a cikinsu, musamman ma Baba da suke ganin baya aikin komai kuma ga ciwon kafar da yake fama da shi, ga kuma iyali rututu mashallah, domin yan matan dakinmu kadai su hudu ne, idan aka cire ni da nake ta biyu da kuma yayana Maimunatu wace ke aure Kano da yaranta, ga kuma yayan Inna su ma su bakwai duka mata sa dai ita ta aurarda matanta hudu saura uku.

“Kai shinkafar nan mai tsada, Allah ya saka musu da alheri”

“Amin”
Chapter 1 · 0% Book details