Sashe 75
Yarena Addinina Part Complete Hausa Novel · about 9 min read
Nima ya gina min gida na mu ni da sweety Matawata.... Lolxx..
Reedwan Suraj Isma'il
YARENA ADDININA
CI GABAN LABARI
Sun isa Jalingo Iman ta sauka a gidansu shi kuwa Suhaif a Hotel ya sauka. Nan ma yasha alwashin wataran zai yi gini a garin saboda idan suka zo su dinga sauka. Bayan sun huta gajiyar hanya sai Iman ta shaidawa Iyayenta gaskiyar magana akan jaririn Harriet cewa bai mutu ba don haka yanzu zata bazama nemansa har sai ta samo shi. Suhaif ke tukata suka nufi gidan da aka ce mata marikan nasa nan suka koma. A bakin get din gidan Suhaif yayi parkin. Ya ce zai raka Iman ciki ta ce "A'a ya bari ta shiga ita kadai tunda gidan matan aure ne. Iman ta shiga cikin get bayan ta gaishe da mai gadin ta tambayeshi "Matar gidan tana ciki kuwa? Ya amsa mata "Eh tana ciki" ta tambaye shi "Yaran fa? Ya ce "Sun tafi Islamiyya. Iman ta ce "Su duka ukun? Ya ce "A'a su biyar dai. Iman ta ce a ranta "Su biyar? Anya kuwa gidan ne Abubakar da Aisha ne kawai ai sai Muhammad suka zama su uku, to ko Mamar tasu ta kara haihuwa tayi? Haka Iman take tunani har ta isa kofar falon gidan. Tayi sallama matar gidan mai suna Salma ta amsa gami da yin izini ga mai sallamar ta shigo. Iman ta shiga, tana shiga ta gane fuskar matar Mahaifiyar su Aisha ce domin taganta lokacin da ta haye kan bishiya, ita kuwa matar bata taba ganin Iman ba. Iman sai fara'a take yiwa Salma kamar ta santa, Salma cike da mamaki take kallon Iman tana tunanin anya ta san wannan matar kuwa? Ta gama tunanin duniyar nan taga bata taba ganin Iman ba. Ta nunawa Iman kujera ta zauna suka gaisa. Ta kwallawa mai aikinta kira ta ce ta kawowa bakuwa ruwa da lemo. Iman ta gyara zama tayi murmushi cikin yaren fulatanci ta ce "Baki sanni ba ko? Salma tayi murmushi ta ce "Gaskiya ban gane ki ba. Iman tayi gyaran murya ta ce "Ba zaki gane ni ba amma ni na gane ki. Shekarun baya nazo mai gadinku ya ce min kun tafi Umara ku duka gidan harda yaranki. Salma ta ce "Oh daman kece kika zo? Ya fada min wai nayi bakuwa ya ce wata fara tas. Ya ce ta tambayeni ta tambayi Muhammad . Ya ce har kina tambayarsa Muhammada ya girma, yana tafiya yanzu? Na dinga mamaki sai na zata ko ma Mahaifiyarsa ce ta zo, ta fada a hankali.
Iman tayi shiru can ta dago ta kalli Salma ta ce "Haka aka yi nice na zo. Da Aisha da Abubakar sun ganni me yiwuwa su gane ni amma ba lallai bane su gane ni saboda tun suna kanana. Salma ta gyara zama ta tsurawa Iman ido tana sauraranta cike da mamaki.
Iman ta ci gaba da cewa "Yanzu ma na zo ne mu gaisa tunda na zo garin. Salma ta ce "Ko zaki min dalla-dalla don in gane ki sosai? Iman ta ce "Maganar gaskiya nice na ajiye muku Muhammad, amma nasan nayi muku laifi ku yafe min, babu yadda zanyi a lokacin. Salma ta zabura ta tashi tsaye ta dafe kirji ta ce "Ke ce? Iman ta nisa ta ce "Labarine mai tsawo. Salma ta ce "To bari na taso mai gidana Ibrahim, yana bacci a daki wannan lamarin babba ne. Ta shiga daki bayan *yan mintina suka fito tare, a zabure ya fito.
Iman ta gaishe shi sai taga ya na mata kallon tara saura kwata ya amsa da kyar. Ta nisa ta ce "Dan Allah idan baza ku damu ba zan iya shigowa da mijina shima ayi maganar a gabansa? Matar ta ce "Kwarai kuwa ya shigo. Ibrahim ya ce "Bari na aika a kira su Malam Shehu tunda suna nan aka tsinci yaron duk a hadu aji labarin. Tunda sune shaidu. Iman da mijinta, haka ga Salma ga mijinta Ibrahim sannan ga Malam Shehu da sauran Jama'ar da suke nan ranar da aka tsinci dan. Aka cika falon ana sauraran Iman. Ta fara basu labari tun daga farkon yadda Harriet ta haifi yaron har ranar data yarda shi. Babu shakka duk yadda ta kwatanto yadda ta yar da dan haka ne babu karya. Sai suka tambayeta yanzu meke tafe da ita, da kuma dalilin zuwanta yanzu. Iman ta ce ta zo ta ganshi ne ta tabbatar da inda yake sannan ta nemi izini su yarde masa ta dinga zuwa ganinsa. Sai tausayinta ya rufe marikan yaron da sun dauka cewa zata yi zata dauke shi.
Iman taci gaba da cewa idan da hali tana son ta sami wasu su rakata a je wajen Mahaifin yaron a Baucji yaga Babansa saboda watarana. Suka amsa mata da "Haka ne gaskiya ne. Duk ba abun damuwa bane. Yata *yan makaranta sun taso sai surutunsu ake ji kafin su karaso. Iman ta baza idanuwanta gaba daya tana duban kofar shigowa tana so taga Muhammad dinta. Suka shigo kofar sai suka durkusa suka gaishe su dukkansu. Daga gani babu tambaya, babu wanda ya nuna mata shi ta gane shi. Kamar kaki Micheal yayi, kamarsu daya da Ubansa. Ya girma sosai gashi da tsaho kamar ubansa. Iman ta fashe da kuka, ta ce ya je wajenta su gaisa. Ya tsaya yana kallonta bai santa ba. Sai da Mamarsa Salma ta ce masa "Muhammad jeka ku gaisa da Aunty. Sanna ya je wajen Iman, ta rungume shi tana kuka. Iman ta tambaye shi da turanci ajinsa nawa a makarantar boko? Ya amsa mata ya ce "Primary 2. Ta tambaye shi shekarunsa nawa ya ce bakwai. Tayi masa larabci ta ce Islamiyya fa ajinsa nawa? Ya ce uku. Ta ce kur'ani izunsa nawa? Ya ce izufi biyar. Iman tayi dariya ta fada da Fulatanci "Kai Muhammad har ka yi izufi biyar? Malamin ajinsu yana wajen ya ce "Ai ma har ya rage yanzu a izufi goma yake. Muhammad yaro ne mai hazaka har tsallaken aji ake yi masa saboda kokarinsa. Kafin ya gama primary zai iya sauke Alkur'ani. Iman taji dadi ya rufeta.
Aisha da Abubakar sun girma ga kannensa nan kanana da aka haifa dukka maza. Iman ta dinga tunawa su Aisha tana cewa "Yanzu kun manta ni Mamar Muhammad da ku kace in ajiye muku shi kuna son kani. Aisha ta tuno amma Abubakar bai tuna ba saboda bashi da wayo a lokacin. Daga karshe Iman ta dauko musu kayan da ta kawo musu, alawa da biskit kala-kala na kasa shen waje da ta dawo. Suka hadu aka tsayar da shawarar gobe da sassafe su zasu zo su dauki Ibrahim, Malam shehu da shi Muhammad dina a tafi Bauchi wajen Micheal.
Washe gari da sassafe Iman da Suhaif suka shirya suka fito tafiya Bauchi. Suka biyo daukar su Muhammad. Iman na shiga gidan ta tarar an shirya su kawai suke jira. Suka dungumo suka fito wajen mota. Salma tayi musu rakiya duk jikinta yayi sanyi, hankalinta ya tashi gani take idan Mahaifin Muhammad ya ganshi zai dauke shi ya hana a dawo da shi. Iman ta lura da halin da Salma ke ciki sai ta shiga kwantar mata da hankali cewar babu matsala yadda suka dauki Muhammad yanzu haka in anjima zasu dawo mata da danta Insha-Allah. Sannan Salma ta saki ranta tayi murmushi ta ce "Allah Ya kiyaye hanya.
Suhaif ne yake tukawa, Iman a gaba. Ibrahim da Malam Shehu a baya Muhammad a tsakiyarsu a kujerun baya. Suka tafi, Salma da *ya*yanta suna daga musu hannu har suka yi nisa. Babu in da suka tsaya tunda suka fara tafiya sai a garin Bauchi. Bauchin Yakubu! Inji masu kirari. Iman ta shiga tunani ina zata fara neman Micheal a cikin garin nan, shi me gidaje kala-kala. Sai ta ce su fara zuwa gidansa na G.R.A kusa da gidan Gwamna. Tana nunawa Suhaif hanya har bakin get din gidan.
Iman ta fito daga mota tace su jira bari ta tambaya. Ta kwankwasa get, mai gadi ya fito da sauri ta karamar kofa dan yaga ko waye. Iman tayi murmushi ta gaishe shi ta ce "Dan Allah maigidan yana ciki? Ya ce "A'a ya tafi kasar waje da sabuwar amaryarsa yawon shakatawa, uwar gidansa ce kawai a ciki ita kuwa bama iya tunkararta saboda yanzu tana tsakiyar kishi sai ta huce a kanka. Kamar zata mare mu haka take mana, sai kace mu muka sa Alhaji yayi mata amarya. Iman ta ce Alhaji? Yaya sunan Alhajin ya ce "Alhaji Musa! Waye a garin nan baisan shi ba, ko dai batan kai kika yi? Iman ta ce "Ina mai ainihin gidan Micheal? Ya ce "Oh Micheal wannan tantirin yaron? Ai tuni ya tashi, ya sayar da gidan ko ince hukuma ta kwace gidan daya dunguma wani fashi aka kwace kadarorinsa. Iman ya ce "Yanzu a ina kake ganin zan iya ganinsa? Ya ce "Ke kuwa Hajiya ina kike neman kungurmin dan fashi, kina Musulma nai mutunci ko wani abu ya dunguma muku? Koda yake ba ruwana. Gaskiya idan na ce ga inda zaki ganshi nayi karya, don nima labarinsa nake ji ban sanshi ba. Iman tayi godiya ta shiga mota. Ta ce da Suhaif su tafi daya gidan nasa baya nan. Suna tafiya Iman tana hawaye idan ta waiga ta kalli dansa Muhammad, sai hawaye yayi ta zuba daga idanuwanta saboda tausayinsa. Suhaif yana kallonta ya rasa kalmar da zai fada mata da zata daina kuka. Yasan tausayin yaron take ji idan ta tuna da yadda aka same shi amma haka Allah Ya rubuto, uban wani baya haihuwar dan wani.
Duk in da Iman tasan gidan Micheal ne ta je sai su tarar an sayar da gidan wasu ne a ciki. Sun je gidajen abokansa gaba daya, suma ba sune a ciki ba. Daga karshe ta ce suje zaranda Hotel ko har yanzu yana zaman Hotel. Suka je, ma'aikatan Hotel suka duba sunayen Jama'ar dake ciki da lamabar dakunan da suke babu mai suna Micheal.
Hankalin Iman ya tashi kwarai, ita dama ace ta sami wanda ya sanshi ma ya bata labarin idan mutuwa yayi hankalinta zai fi kwanciya. Idan yaron ya girma a shaida masa Uwarsa da Ubansa sun mutu yafi sauki. Suna shiga mota zasu fita daga Hotel din sai ga wani wanda ta sani abokin Micheal ne sunansa Mansir. Yana tafe yana kallon Iman harda tuntube yana yi mata kallon sani. Iman ta fito daga mota da sauri ta kira sunansa. Nan da nan ya dawo wajen da take tsaye jikin mota. Ta ce "Mansir ne ko? Cike da mamaki ya ce "Ni ne kamar preety ce ko? Iman tayi murmushi ta ce "Ni ce. Sai ya girgiza kai yayi shiru hawaye yana zuba daga idanuwansa. Ya ce "Preety kinga yadda rayuwa ta zamar mana ko? Wato duk abokan mu da kika sani an harbesu. *Yan matanmu su Janet duk sun mutu. Irina da ba'a kamamu ba, mun tuba da fashi mun zama abun tausayi. Yanzu haka sana'ata haka rijiya da yasar masai ko kwata. Iman ta tambaye shi cike da fargaba ta ce "An kashe Micheal ma? Ya ce "Micheal ba'a kashe shi ba, amma wadanda aka kashe sun fishi kwanciyar hankali duk da ban san halinda suke ciki a can ba amma duk karshen mutum mutuwa kowa sai ya mutu. Gara ni dinnan da kika ganni da tsumma akan Micheal. Ni ina haka ana biyana shi ba zai iya ba saboda ya nakashe, ga shi ya tsiyace komai nasa ya kare. Kin sanshi mafadacine shine ya je Lagos ya yo tsokanar wasu gungun *yan fashi ko kudin da suka yi fashi ne ya kwashe ya hanasu? Ban dai sani ba shine suka biyo shi Bauchi zasu kashe shi basu same shi ba suka je suka kashe Mahaifiyarsa. Da yaga haka shima ya je yayi musu barna shine suka biyo shi suka sare masa kafa.
Reedwan Suraj Isma'il
YARENA ADDININA
CI GABAN LABARI
Sun isa Jalingo Iman ta sauka a gidansu shi kuwa Suhaif a Hotel ya sauka. Nan ma yasha alwashin wataran zai yi gini a garin saboda idan suka zo su dinga sauka. Bayan sun huta gajiyar hanya sai Iman ta shaidawa Iyayenta gaskiyar magana akan jaririn Harriet cewa bai mutu ba don haka yanzu zata bazama nemansa har sai ta samo shi. Suhaif ke tukata suka nufi gidan da aka ce mata marikan nasa nan suka koma. A bakin get din gidan Suhaif yayi parkin. Ya ce zai raka Iman ciki ta ce "A'a ya bari ta shiga ita kadai tunda gidan matan aure ne. Iman ta shiga cikin get bayan ta gaishe da mai gadin ta tambayeshi "Matar gidan tana ciki kuwa? Ya amsa mata "Eh tana ciki" ta tambaye shi "Yaran fa? Ya ce "Sun tafi Islamiyya. Iman ta ce "Su duka ukun? Ya ce "A'a su biyar dai. Iman ta ce a ranta "Su biyar? Anya kuwa gidan ne Abubakar da Aisha ne kawai ai sai Muhammad suka zama su uku, to ko Mamar tasu ta kara haihuwa tayi? Haka Iman take tunani har ta isa kofar falon gidan. Tayi sallama matar gidan mai suna Salma ta amsa gami da yin izini ga mai sallamar ta shigo. Iman ta shiga, tana shiga ta gane fuskar matar Mahaifiyar su Aisha ce domin taganta lokacin da ta haye kan bishiya, ita kuwa matar bata taba ganin Iman ba. Iman sai fara'a take yiwa Salma kamar ta santa, Salma cike da mamaki take kallon Iman tana tunanin anya ta san wannan matar kuwa? Ta gama tunanin duniyar nan taga bata taba ganin Iman ba. Ta nunawa Iman kujera ta zauna suka gaisa. Ta kwallawa mai aikinta kira ta ce ta kawowa bakuwa ruwa da lemo. Iman ta gyara zama tayi murmushi cikin yaren fulatanci ta ce "Baki sanni ba ko? Salma tayi murmushi ta ce "Gaskiya ban gane ki ba. Iman tayi gyaran murya ta ce "Ba zaki gane ni ba amma ni na gane ki. Shekarun baya nazo mai gadinku ya ce min kun tafi Umara ku duka gidan harda yaranki. Salma ta ce "Oh daman kece kika zo? Ya fada min wai nayi bakuwa ya ce wata fara tas. Ya ce ta tambayeni ta tambayi Muhammad . Ya ce har kina tambayarsa Muhammada ya girma, yana tafiya yanzu? Na dinga mamaki sai na zata ko ma Mahaifiyarsa ce ta zo, ta fada a hankali.
Iman tayi shiru can ta dago ta kalli Salma ta ce "Haka aka yi nice na zo. Da Aisha da Abubakar sun ganni me yiwuwa su gane ni amma ba lallai bane su gane ni saboda tun suna kanana. Salma ta gyara zama ta tsurawa Iman ido tana sauraranta cike da mamaki.
Iman ta ci gaba da cewa "Yanzu ma na zo ne mu gaisa tunda na zo garin. Salma ta ce "Ko zaki min dalla-dalla don in gane ki sosai? Iman ta ce "Maganar gaskiya nice na ajiye muku Muhammad, amma nasan nayi muku laifi ku yafe min, babu yadda zanyi a lokacin. Salma ta zabura ta tashi tsaye ta dafe kirji ta ce "Ke ce? Iman ta nisa ta ce "Labarine mai tsawo. Salma ta ce "To bari na taso mai gidana Ibrahim, yana bacci a daki wannan lamarin babba ne. Ta shiga daki bayan *yan mintina suka fito tare, a zabure ya fito.
Iman ta gaishe shi sai taga ya na mata kallon tara saura kwata ya amsa da kyar. Ta nisa ta ce "Dan Allah idan baza ku damu ba zan iya shigowa da mijina shima ayi maganar a gabansa? Matar ta ce "Kwarai kuwa ya shigo. Ibrahim ya ce "Bari na aika a kira su Malam Shehu tunda suna nan aka tsinci yaron duk a hadu aji labarin. Tunda sune shaidu. Iman da mijinta, haka ga Salma ga mijinta Ibrahim sannan ga Malam Shehu da sauran Jama'ar da suke nan ranar da aka tsinci dan. Aka cika falon ana sauraran Iman. Ta fara basu labari tun daga farkon yadda Harriet ta haifi yaron har ranar data yarda shi. Babu shakka duk yadda ta kwatanto yadda ta yar da dan haka ne babu karya. Sai suka tambayeta yanzu meke tafe da ita, da kuma dalilin zuwanta yanzu. Iman ta ce ta zo ta ganshi ne ta tabbatar da inda yake sannan ta nemi izini su yarde masa ta dinga zuwa ganinsa. Sai tausayinta ya rufe marikan yaron da sun dauka cewa zata yi zata dauke shi.
Iman taci gaba da cewa idan da hali tana son ta sami wasu su rakata a je wajen Mahaifin yaron a Baucji yaga Babansa saboda watarana. Suka amsa mata da "Haka ne gaskiya ne. Duk ba abun damuwa bane. Yata *yan makaranta sun taso sai surutunsu ake ji kafin su karaso. Iman ta baza idanuwanta gaba daya tana duban kofar shigowa tana so taga Muhammad dinta. Suka shigo kofar sai suka durkusa suka gaishe su dukkansu. Daga gani babu tambaya, babu wanda ya nuna mata shi ta gane shi. Kamar kaki Micheal yayi, kamarsu daya da Ubansa. Ya girma sosai gashi da tsaho kamar ubansa. Iman ta fashe da kuka, ta ce ya je wajenta su gaisa. Ya tsaya yana kallonta bai santa ba. Sai da Mamarsa Salma ta ce masa "Muhammad jeka ku gaisa da Aunty. Sanna ya je wajen Iman, ta rungume shi tana kuka. Iman ta tambaye shi da turanci ajinsa nawa a makarantar boko? Ya amsa mata ya ce "Primary 2. Ta tambaye shi shekarunsa nawa ya ce bakwai. Tayi masa larabci ta ce Islamiyya fa ajinsa nawa? Ya ce uku. Ta ce kur'ani izunsa nawa? Ya ce izufi biyar. Iman tayi dariya ta fada da Fulatanci "Kai Muhammad har ka yi izufi biyar? Malamin ajinsu yana wajen ya ce "Ai ma har ya rage yanzu a izufi goma yake. Muhammad yaro ne mai hazaka har tsallaken aji ake yi masa saboda kokarinsa. Kafin ya gama primary zai iya sauke Alkur'ani. Iman taji dadi ya rufeta.
Aisha da Abubakar sun girma ga kannensa nan kanana da aka haifa dukka maza. Iman ta dinga tunawa su Aisha tana cewa "Yanzu kun manta ni Mamar Muhammad da ku kace in ajiye muku shi kuna son kani. Aisha ta tuno amma Abubakar bai tuna ba saboda bashi da wayo a lokacin. Daga karshe Iman ta dauko musu kayan da ta kawo musu, alawa da biskit kala-kala na kasa shen waje da ta dawo. Suka hadu aka tsayar da shawarar gobe da sassafe su zasu zo su dauki Ibrahim, Malam shehu da shi Muhammad dina a tafi Bauchi wajen Micheal.
Washe gari da sassafe Iman da Suhaif suka shirya suka fito tafiya Bauchi. Suka biyo daukar su Muhammad. Iman na shiga gidan ta tarar an shirya su kawai suke jira. Suka dungumo suka fito wajen mota. Salma tayi musu rakiya duk jikinta yayi sanyi, hankalinta ya tashi gani take idan Mahaifin Muhammad ya ganshi zai dauke shi ya hana a dawo da shi. Iman ta lura da halin da Salma ke ciki sai ta shiga kwantar mata da hankali cewar babu matsala yadda suka dauki Muhammad yanzu haka in anjima zasu dawo mata da danta Insha-Allah. Sannan Salma ta saki ranta tayi murmushi ta ce "Allah Ya kiyaye hanya.
Suhaif ne yake tukawa, Iman a gaba. Ibrahim da Malam Shehu a baya Muhammad a tsakiyarsu a kujerun baya. Suka tafi, Salma da *ya*yanta suna daga musu hannu har suka yi nisa. Babu in da suka tsaya tunda suka fara tafiya sai a garin Bauchi. Bauchin Yakubu! Inji masu kirari. Iman ta shiga tunani ina zata fara neman Micheal a cikin garin nan, shi me gidaje kala-kala. Sai ta ce su fara zuwa gidansa na G.R.A kusa da gidan Gwamna. Tana nunawa Suhaif hanya har bakin get din gidan.
Iman ta fito daga mota tace su jira bari ta tambaya. Ta kwankwasa get, mai gadi ya fito da sauri ta karamar kofa dan yaga ko waye. Iman tayi murmushi ta gaishe shi ta ce "Dan Allah maigidan yana ciki? Ya ce "A'a ya tafi kasar waje da sabuwar amaryarsa yawon shakatawa, uwar gidansa ce kawai a ciki ita kuwa bama iya tunkararta saboda yanzu tana tsakiyar kishi sai ta huce a kanka. Kamar zata mare mu haka take mana, sai kace mu muka sa Alhaji yayi mata amarya. Iman ta ce Alhaji? Yaya sunan Alhajin ya ce "Alhaji Musa! Waye a garin nan baisan shi ba, ko dai batan kai kika yi? Iman ta ce "Ina mai ainihin gidan Micheal? Ya ce "Oh Micheal wannan tantirin yaron? Ai tuni ya tashi, ya sayar da gidan ko ince hukuma ta kwace gidan daya dunguma wani fashi aka kwace kadarorinsa. Iman ya ce "Yanzu a ina kake ganin zan iya ganinsa? Ya ce "Ke kuwa Hajiya ina kike neman kungurmin dan fashi, kina Musulma nai mutunci ko wani abu ya dunguma muku? Koda yake ba ruwana. Gaskiya idan na ce ga inda zaki ganshi nayi karya, don nima labarinsa nake ji ban sanshi ba. Iman tayi godiya ta shiga mota. Ta ce da Suhaif su tafi daya gidan nasa baya nan. Suna tafiya Iman tana hawaye idan ta waiga ta kalli dansa Muhammad, sai hawaye yayi ta zuba daga idanuwanta saboda tausayinsa. Suhaif yana kallonta ya rasa kalmar da zai fada mata da zata daina kuka. Yasan tausayin yaron take ji idan ta tuna da yadda aka same shi amma haka Allah Ya rubuto, uban wani baya haihuwar dan wani.
Duk in da Iman tasan gidan Micheal ne ta je sai su tarar an sayar da gidan wasu ne a ciki. Sun je gidajen abokansa gaba daya, suma ba sune a ciki ba. Daga karshe ta ce suje zaranda Hotel ko har yanzu yana zaman Hotel. Suka je, ma'aikatan Hotel suka duba sunayen Jama'ar dake ciki da lamabar dakunan da suke babu mai suna Micheal.
Hankalin Iman ya tashi kwarai, ita dama ace ta sami wanda ya sanshi ma ya bata labarin idan mutuwa yayi hankalinta zai fi kwanciya. Idan yaron ya girma a shaida masa Uwarsa da Ubansa sun mutu yafi sauki. Suna shiga mota zasu fita daga Hotel din sai ga wani wanda ta sani abokin Micheal ne sunansa Mansir. Yana tafe yana kallon Iman harda tuntube yana yi mata kallon sani. Iman ta fito daga mota da sauri ta kira sunansa. Nan da nan ya dawo wajen da take tsaye jikin mota. Ta ce "Mansir ne ko? Cike da mamaki ya ce "Ni ne kamar preety ce ko? Iman tayi murmushi ta ce "Ni ce. Sai ya girgiza kai yayi shiru hawaye yana zuba daga idanuwansa. Ya ce "Preety kinga yadda rayuwa ta zamar mana ko? Wato duk abokan mu da kika sani an harbesu. *Yan matanmu su Janet duk sun mutu. Irina da ba'a kamamu ba, mun tuba da fashi mun zama abun tausayi. Yanzu haka sana'ata haka rijiya da yasar masai ko kwata. Iman ta tambaye shi cike da fargaba ta ce "An kashe Micheal ma? Ya ce "Micheal ba'a kashe shi ba, amma wadanda aka kashe sun fishi kwanciyar hankali duk da ban san halinda suke ciki a can ba amma duk karshen mutum mutuwa kowa sai ya mutu. Gara ni dinnan da kika ganni da tsumma akan Micheal. Ni ina haka ana biyana shi ba zai iya ba saboda ya nakashe, ga shi ya tsiyace komai nasa ya kare. Kin sanshi mafadacine shine ya je Lagos ya yo tsokanar wasu gungun *yan fashi ko kudin da suka yi fashi ne ya kwashe ya hanasu? Ban dai sani ba shine suka biyo shi Bauchi zasu kashe shi basu same shi ba suka je suka kashe Mahaifiyarsa. Da yaga haka shima ya je yayi musu barna shine suka biyo shi suka sare masa kafa.