Sashe 35
Yarena Addinina Part Complete Hausa Novel · about 9 min read
Iman tayi shiru tsabar yin kuka tayi magana ta gaji, gashi babu koshi a tare da ita. Suhaif ya aika wani gida kusa da inda suke ya ce a debo mata ruwa ta sha. Idanuwanta sunyi luhu-luhu tasha kuka ta godewa Allah. Abun tausayi, da aka kawo mata ruwa kurba daya tayi da kyar ta hadiye saboda tsananin rayuwar da ta shiga. Suhaif yayi-yayi ta sake shan ruwan ta ce ba zata iya shaba, ta dauki lokaci mai dan tsawo kafin ta sake cewa wani abu.
Ta ci gaba da cewa "A tunanina iya sanina bana zaton akwai yarinya mai irin shekaruna, da ta taba shiga irin kuncin rayuwar dana shisshiga. Amma na sa a raina Allah Ya na sane dani kuma baya bacci. Kowanne bawa akwai yadda Allah Ya ke jarrabarsa, ni kuma ta haka Allah Ya ke jarrabata. Nasha wuya a wannan lokacin saboda kula da jaririn bana samun bacci da daddare kuma dole in bar dakin Mama Tabita saboda mijinta ranar zai kwana a gida domin wani yana canjarsa. Ni kadai a dakin da aka ware mun, tun bansan yadda zan lallashi yaro ba nar na fara sabawa, shima kuma ya saba da jagwalgwalon da nake masa har yayi shiru ya koma bacci. Yana rungume a hannuna, ni kuma ina zaune ina gyangyadi har sai na tabbatar barcin nasa yayi nisa sannan nake kwantar dashi in kwanta. Ana jimawa zai farka in sake katse baccina in bashi madara, idan yaki komawa bacci saina goya shi ina jijjigashi. Ni kadai a zaune cikin dare yayin da duk bil'adama suna bacci. Idan na gaji sai in ta kuka ni da jaririn a rasa mai lallashin wani. Kar kuce da safe zai barni inyi bacci, a'a garin Allah na wayewa zan shiga kacaniyar hada ruwan wanka Mama Tabita tayi masa, ana jimawa in dama masa madara in bashi, a jima yayi kashi, ajima yayi tunbudi, ajima inyi wankin kayansa. Haka dai muka kasance babu hutu ni da Tabita kuma ga aikin gidanmu.
A lokacin na sawa raina Mahaifana basa sona ko kadan don ina bukatar taimakonsu da kulawarsu basa mun, ina takaicin wannan al'amarin musamman idan naga kallon da Mahifina yake min, hankalina yana tashi kamar ba shine mai sona ba, yayi hira da ni, yayi wasa dani, yau gashi idan na gaishe shi dakyar zai amsa min a cicciki. Mahaifiyata kuwa daman can ta saba yimin haka tun ina yarinya, kullum muna rigima da ita saboda bana zuwa wajan bautarsu, ta fuskanci bana yin addininta, tayi dukan tayi zagin ta gaji. Ina tsananin jin takaici idan naga Mahaifina tare da Mahaifiyata da kannena sun dunguma za su tafi wajan bauta duk ranar bauta. Nakan gigice inyi kuka saboda takaicin Mahaifina ya bar addininsa na Musulunci. Babu wanda yake cemin in shirya in biyo su wajen bauta. Kamar yadda suka san Tabita da addininta nima sunsan dole da addinina daban ba nasu ba.
Jaririn ya fara warwarewa yana girma watanninsa uku a duniya. Mahaifiyata tasa kanwata Rabecca ta kira ni a gidan Mama Tabita, ina yi masa wanka. Mama Tabita ta karbe shi ta ce in je kiran da ake min, ina zuwa na duka na gaishe da Mahaifiyata cikin harshen Igbo. Ta amsa a shelake ta nuna min wata katuwar jaka a makare da kaya ta ce "Ki dauki jakar nan sako ne daga Micheal ya aiko jiya da daddare hade da wasika, wasikar kuma gata na karanta, ya ce ranar asabar mai zuwa yana nan tafe da Mahaifiyarsa da *yan uwansa akan zancen aurenku. Kada ki sake bamu kunya, kada ki kuskura ki bude baki ki fadi wannan bayanin naki na rashin hankali cewar bake ce kika haifi yaron ba, daga karshe kuma kada ki sake ki fito min da wata tsirfar wani addini idan ba irin namu ba. Ni da Micheal da Mahaifinki addininmu daya don haka dole addinin da muke shi zaki bi, haka danki ma. Ranar lahadi zamu dunguma dasu Micheal dukka aje wajan bauta, saura ki ki zuwa ko kuma kije ki faki idanuwanmu ki gudo kamar yadda kika saba tun kina yarinya. Idan ki ka kunyatamu, ki ka ki auransa to fa ke da danki zamanku ya kare a gidan nan, don babu wanda ya ce ki je kiyi ciki ki haihu dole ki aure shi ku tarkata ku tafi. Baza ki jawo mana abun kunya ba, abun fada, ana ganin girmanmu ana mana biyayya kisa girmanmu da mutucinmu ya zube a idon jama'a. Yanzu ma Allah ne Ya dubi zuciyata ya rufa mana asiri Micheal ya zo da kansa yayi zancen aure da bansan me zan fadawa mutane ba *yata ta haifi da marar uba.
Jinta kawai nake amma tuntuni tasan bana cikin haiyacina nayi sharkaf da hawaye. Wata uwar tsawa da ta daka min ina tsugune sai da ni mike tsaye ta ce "Kukan me kike yi? Rufe min baki ko in tashi in tattakaki. Mama Tabita ce ta katsemu ta shigo da gudu a gigice dauke da Jaririn a hannunta, zanin jikinta ya fadi a hanya bata sani ba, daga ita sai dan siket da riga. Karkarwa take ta nufo wajen da Mahaifiyata ke zaune tana cewa "Madam ki taimakamin ina sawa yaro riga idanuwansa sun kakkafe sama, babu numfashi, babu motsi. Subhanallahi! Irin bugun da zuciyata tayi a lokacin inda yazo da karar kwana, zuciyata ta fashe na fadi na mutu. Na karaso da gudu na karbe shi ina jijjigashi hakika ko ba'a fadamin ba nasan yaron ya rasu. Mahaifiyata ta gigice gaba dayanmu ihu muke. Mahaifina na kwance a dakinsa yayi wuf ya fito, ya karbi yaron ya jujjuya, sai ya girgiza kai alamar babu. Nayi kuka nayi kururuwa, babu lallashin da basu yimin ba naki yin shiru. Na rike yaron tsam a hannuna, suka yi juyin duniyar nan su karbe shi naki basu. Abun mamaki sai suka ga na sabashi a baya. Suka tambayeni ina zanje cikin kuka na ce "Asibiti Mama Tabita ta rikeni tana cewa ya mutu me za'ayi miki a asibiti, na fisge na shiga dakina da gudu na dauko jakata na fito, kuka nake, tana rokona in hakura in sauke dan, idan mutum ya mutu babu abin da *yan asibiti zasu iya yi. Na ki fur nace ni dai asibiti zan kai shi. Mahaifiyata ta ce da Tabita ta barni inje asibitin in na je ma zan dawo, likitoci suna farfado da matacce ne? Haukar banza da yarinta, manya sun fadamin ya mutu ni na san mutuwa ne da zance asibiti zani. Mahaifina yana ta kwallamin kira na fice da gudu na nufi titi ina kururuwar kuka tamkar tababbiya. *Yan unguwarmu suka firfito suna tambaya "Meya sami Pretty? Aka sanar musu dana ne ya mutu na goya shi na ce asibiti zan kai shi. Sai suyi dariya suce "Yarinta ke damuna ban san mutuwa ba ne, lallai da ban je asibiti ba. Na hau dan achaba ina karkarwa na ce ya kaini asibiti.
Daidai get din shiga asibiti naji yaron yana tamin mutsu-mutsu a baya, wani dadi marar misaltuwa ya lullubeni, nan da nan na cewa dan acaba ya sauke ni a nan. Yana tsayawa na diro da sauri daga kan babur na kwance goyon da sauri yayin da nayi ajiyar zuciya gami da ambaton alhamdulillahi a lokacin da nayi ido hudu da dan jaririna. Saboda tsabar gigicewa gami da jin dadi, mantawa nayi ban biya mai achaba kudin babur dinsa ba, na ruga cikin asibitin da gudu. Ina shiga ba tare da na yanki kati ba, haka ba tare da na tuna ana bin layin ganin likita ba, haka na tsallake dandazon matan dana iske a zaune akan bencina suna bin layin ganin likita, sai kawai na tsallakesu na rufta dakin likita, kowa ya bude baki yana kallona cike da mamaki. Ma'aikaciyar jinya (nurse) din dake aiki tare da likitan ta biyoni cikin dakin da sauri tana tambayata "Ke baiwar Allah lafiya kika zo kika iske mutane a layi, wasu a ciki suna ganin likita kika shigo? Nayi guru-guru da ido in kalleta in kalli likita in kalli matan dana iske a gaban teburin likita yana dubasu. Haka shima likita ya zura min ido gaba dayansu suna sauraran bayanin da zai fito daga bakina.
Nurs din ta sake tambayata "Ina katinki na ganin likita ko shima baki je kin yanka ba? Na gyada kai alamar eh ban yanka ba. Sai haushina ya rufeta ta hau fada tana cewa in fito kar in bata musu lokaci in likita zan gani inje in yanki kati in bi layi irin na kowa, akwai mutane a gabana saman da talatin. Na rushe da kuka ina rokarsa ya taimakeni yarona suma yake yi yanzu ya farfado. Cike da tausayi likitan ya dubeni sai ya cewa nurse din ta rabu da ni bari ya dubani bata ganin ni yarinya ce watakila bansan yadda ake yi ba. Nurse ta fita ta jawo mana kofar ta rufe. Ya juya ya dubi matan guda biyu da suke zazzaune a kujerun dake gaban teburinsa suma rungume da yaransu ya ce suyi hakuri bari ya duba min yaron. Ya mika hannu ya karbeshi ya fara duba shi yana bude bakinsa, hancinsa, cikinsa da kirjinsa, ya zabura ya mike da sauri ya nufi kan wani gado dake ofishin na kwantar da mara lafiya domin dubawa. Na ji gabana ya fadi na dafa kirji cike da fargaba nake tambayar likita "Meke damunsa? Bai bani amsa ba yaci gaba da aikinsa. Ya dauko wani abun gwaje-gwaje yana auna numfashin yaron, ya sake daukar yaron da sauri ya nufi kofar fita, yayin da kuka ya kece min ina binsu a baya, na tabbatar akwai matsala mai yawa ganin likitan hankalinsa a tashe. Muka fito muka nufi wani daki. "Malama me kike nufi ne kin ruga da gudu baki biyani kudin achabana ba? Dan achabar da ya kawo ni ne yake tambayata a cikin kakkausar murya. Na juya inda sautin maganar ke fitowa naga dan achaban ne ransa a bace. Hannuna yana rawa na bude jakata na dauko naira ashirin na mika masa gami da bashi hakuri na ce mantawa nayi. Na sake runtumawa da gudu na bi bayan likita a lokacin harya shiga dakin. Muna shiga likitan ya cirewa yaron kayansa, ya daga kafafuwansa sama kansa a kasa yana jijjiga shi, yayin da yaron ya shide yana kuka, amai ya fara diddikowa ta hanci ta baki, ya mayar da yaron ya kwanta ya kafa masa wani inji mai doguwar roba ya sakala masa ta hanci da baki. Kukan da nake ina tambayar likita meya same shi? Ya tunzura likitan yayi fushi ya ce in fita waje in jira na barshi yayi aikinsa.
Ta ci gaba da cewa "A tunanina iya sanina bana zaton akwai yarinya mai irin shekaruna, da ta taba shiga irin kuncin rayuwar dana shisshiga. Amma na sa a raina Allah Ya na sane dani kuma baya bacci. Kowanne bawa akwai yadda Allah Ya ke jarrabarsa, ni kuma ta haka Allah Ya ke jarrabata. Nasha wuya a wannan lokacin saboda kula da jaririn bana samun bacci da daddare kuma dole in bar dakin Mama Tabita saboda mijinta ranar zai kwana a gida domin wani yana canjarsa. Ni kadai a dakin da aka ware mun, tun bansan yadda zan lallashi yaro ba nar na fara sabawa, shima kuma ya saba da jagwalgwalon da nake masa har yayi shiru ya koma bacci. Yana rungume a hannuna, ni kuma ina zaune ina gyangyadi har sai na tabbatar barcin nasa yayi nisa sannan nake kwantar dashi in kwanta. Ana jimawa zai farka in sake katse baccina in bashi madara, idan yaki komawa bacci saina goya shi ina jijjigashi. Ni kadai a zaune cikin dare yayin da duk bil'adama suna bacci. Idan na gaji sai in ta kuka ni da jaririn a rasa mai lallashin wani. Kar kuce da safe zai barni inyi bacci, a'a garin Allah na wayewa zan shiga kacaniyar hada ruwan wanka Mama Tabita tayi masa, ana jimawa in dama masa madara in bashi, a jima yayi kashi, ajima yayi tunbudi, ajima inyi wankin kayansa. Haka dai muka kasance babu hutu ni da Tabita kuma ga aikin gidanmu.
A lokacin na sawa raina Mahaifana basa sona ko kadan don ina bukatar taimakonsu da kulawarsu basa mun, ina takaicin wannan al'amarin musamman idan naga kallon da Mahifina yake min, hankalina yana tashi kamar ba shine mai sona ba, yayi hira da ni, yayi wasa dani, yau gashi idan na gaishe shi dakyar zai amsa min a cicciki. Mahaifiyata kuwa daman can ta saba yimin haka tun ina yarinya, kullum muna rigima da ita saboda bana zuwa wajan bautarsu, ta fuskanci bana yin addininta, tayi dukan tayi zagin ta gaji. Ina tsananin jin takaici idan naga Mahaifina tare da Mahaifiyata da kannena sun dunguma za su tafi wajan bauta duk ranar bauta. Nakan gigice inyi kuka saboda takaicin Mahaifina ya bar addininsa na Musulunci. Babu wanda yake cemin in shirya in biyo su wajen bauta. Kamar yadda suka san Tabita da addininta nima sunsan dole da addinina daban ba nasu ba.
Jaririn ya fara warwarewa yana girma watanninsa uku a duniya. Mahaifiyata tasa kanwata Rabecca ta kira ni a gidan Mama Tabita, ina yi masa wanka. Mama Tabita ta karbe shi ta ce in je kiran da ake min, ina zuwa na duka na gaishe da Mahaifiyata cikin harshen Igbo. Ta amsa a shelake ta nuna min wata katuwar jaka a makare da kaya ta ce "Ki dauki jakar nan sako ne daga Micheal ya aiko jiya da daddare hade da wasika, wasikar kuma gata na karanta, ya ce ranar asabar mai zuwa yana nan tafe da Mahaifiyarsa da *yan uwansa akan zancen aurenku. Kada ki sake bamu kunya, kada ki kuskura ki bude baki ki fadi wannan bayanin naki na rashin hankali cewar bake ce kika haifi yaron ba, daga karshe kuma kada ki sake ki fito min da wata tsirfar wani addini idan ba irin namu ba. Ni da Micheal da Mahaifinki addininmu daya don haka dole addinin da muke shi zaki bi, haka danki ma. Ranar lahadi zamu dunguma dasu Micheal dukka aje wajan bauta, saura ki ki zuwa ko kuma kije ki faki idanuwanmu ki gudo kamar yadda kika saba tun kina yarinya. Idan ki ka kunyatamu, ki ka ki auransa to fa ke da danki zamanku ya kare a gidan nan, don babu wanda ya ce ki je kiyi ciki ki haihu dole ki aure shi ku tarkata ku tafi. Baza ki jawo mana abun kunya ba, abun fada, ana ganin girmanmu ana mana biyayya kisa girmanmu da mutucinmu ya zube a idon jama'a. Yanzu ma Allah ne Ya dubi zuciyata ya rufa mana asiri Micheal ya zo da kansa yayi zancen aure da bansan me zan fadawa mutane ba *yata ta haifi da marar uba.
Jinta kawai nake amma tuntuni tasan bana cikin haiyacina nayi sharkaf da hawaye. Wata uwar tsawa da ta daka min ina tsugune sai da ni mike tsaye ta ce "Kukan me kike yi? Rufe min baki ko in tashi in tattakaki. Mama Tabita ce ta katsemu ta shigo da gudu a gigice dauke da Jaririn a hannunta, zanin jikinta ya fadi a hanya bata sani ba, daga ita sai dan siket da riga. Karkarwa take ta nufo wajen da Mahaifiyata ke zaune tana cewa "Madam ki taimakamin ina sawa yaro riga idanuwansa sun kakkafe sama, babu numfashi, babu motsi. Subhanallahi! Irin bugun da zuciyata tayi a lokacin inda yazo da karar kwana, zuciyata ta fashe na fadi na mutu. Na karaso da gudu na karbe shi ina jijjigashi hakika ko ba'a fadamin ba nasan yaron ya rasu. Mahaifiyata ta gigice gaba dayanmu ihu muke. Mahaifina na kwance a dakinsa yayi wuf ya fito, ya karbi yaron ya jujjuya, sai ya girgiza kai alamar babu. Nayi kuka nayi kururuwa, babu lallashin da basu yimin ba naki yin shiru. Na rike yaron tsam a hannuna, suka yi juyin duniyar nan su karbe shi naki basu. Abun mamaki sai suka ga na sabashi a baya. Suka tambayeni ina zanje cikin kuka na ce "Asibiti Mama Tabita ta rikeni tana cewa ya mutu me za'ayi miki a asibiti, na fisge na shiga dakina da gudu na dauko jakata na fito, kuka nake, tana rokona in hakura in sauke dan, idan mutum ya mutu babu abin da *yan asibiti zasu iya yi. Na ki fur nace ni dai asibiti zan kai shi. Mahaifiyata ta ce da Tabita ta barni inje asibitin in na je ma zan dawo, likitoci suna farfado da matacce ne? Haukar banza da yarinta, manya sun fadamin ya mutu ni na san mutuwa ne da zance asibiti zani. Mahaifina yana ta kwallamin kira na fice da gudu na nufi titi ina kururuwar kuka tamkar tababbiya. *Yan unguwarmu suka firfito suna tambaya "Meya sami Pretty? Aka sanar musu dana ne ya mutu na goya shi na ce asibiti zan kai shi. Sai suyi dariya suce "Yarinta ke damuna ban san mutuwa ba ne, lallai da ban je asibiti ba. Na hau dan achaba ina karkarwa na ce ya kaini asibiti.
Daidai get din shiga asibiti naji yaron yana tamin mutsu-mutsu a baya, wani dadi marar misaltuwa ya lullubeni, nan da nan na cewa dan acaba ya sauke ni a nan. Yana tsayawa na diro da sauri daga kan babur na kwance goyon da sauri yayin da nayi ajiyar zuciya gami da ambaton alhamdulillahi a lokacin da nayi ido hudu da dan jaririna. Saboda tsabar gigicewa gami da jin dadi, mantawa nayi ban biya mai achaba kudin babur dinsa ba, na ruga cikin asibitin da gudu. Ina shiga ba tare da na yanki kati ba, haka ba tare da na tuna ana bin layin ganin likita ba, haka na tsallake dandazon matan dana iske a zaune akan bencina suna bin layin ganin likita, sai kawai na tsallakesu na rufta dakin likita, kowa ya bude baki yana kallona cike da mamaki. Ma'aikaciyar jinya (nurse) din dake aiki tare da likitan ta biyoni cikin dakin da sauri tana tambayata "Ke baiwar Allah lafiya kika zo kika iske mutane a layi, wasu a ciki suna ganin likita kika shigo? Nayi guru-guru da ido in kalleta in kalli likita in kalli matan dana iske a gaban teburin likita yana dubasu. Haka shima likita ya zura min ido gaba dayansu suna sauraran bayanin da zai fito daga bakina.
Nurs din ta sake tambayata "Ina katinki na ganin likita ko shima baki je kin yanka ba? Na gyada kai alamar eh ban yanka ba. Sai haushina ya rufeta ta hau fada tana cewa in fito kar in bata musu lokaci in likita zan gani inje in yanki kati in bi layi irin na kowa, akwai mutane a gabana saman da talatin. Na rushe da kuka ina rokarsa ya taimakeni yarona suma yake yi yanzu ya farfado. Cike da tausayi likitan ya dubeni sai ya cewa nurse din ta rabu da ni bari ya dubani bata ganin ni yarinya ce watakila bansan yadda ake yi ba. Nurse ta fita ta jawo mana kofar ta rufe. Ya juya ya dubi matan guda biyu da suke zazzaune a kujerun dake gaban teburinsa suma rungume da yaransu ya ce suyi hakuri bari ya duba min yaron. Ya mika hannu ya karbeshi ya fara duba shi yana bude bakinsa, hancinsa, cikinsa da kirjinsa, ya zabura ya mike da sauri ya nufi kan wani gado dake ofishin na kwantar da mara lafiya domin dubawa. Na ji gabana ya fadi na dafa kirji cike da fargaba nake tambayar likita "Meke damunsa? Bai bani amsa ba yaci gaba da aikinsa. Ya dauko wani abun gwaje-gwaje yana auna numfashin yaron, ya sake daukar yaron da sauri ya nufi kofar fita, yayin da kuka ya kece min ina binsu a baya, na tabbatar akwai matsala mai yawa ganin likitan hankalinsa a tashe. Muka fito muka nufi wani daki. "Malama me kike nufi ne kin ruga da gudu baki biyani kudin achabana ba? Dan achabar da ya kawo ni ne yake tambayata a cikin kakkausar murya. Na juya inda sautin maganar ke fitowa naga dan achaban ne ransa a bace. Hannuna yana rawa na bude jakata na dauko naira ashirin na mika masa gami da bashi hakuri na ce mantawa nayi. Na sake runtumawa da gudu na bi bayan likita a lokacin harya shiga dakin. Muna shiga likitan ya cirewa yaron kayansa, ya daga kafafuwansa sama kansa a kasa yana jijjiga shi, yayin da yaron ya shide yana kuka, amai ya fara diddikowa ta hanci ta baki, ya mayar da yaron ya kwanta ya kafa masa wani inji mai doguwar roba ya sakala masa ta hanci da baki. Kukan da nake ina tambayar likita meya same shi? Ya tunzura likitan yayi fushi ya ce in fita waje in jira na barshi yayi aikinsa.