Sashe 5
Yarena Addinina Part Complete Hausa Novel · about 4 min read
A yau da yamma Najib ne ya dira a garin Doko daga Kano, ya iske Suhaif a dakinsa yana zaune kan katifarsa ya jingina a jikin filon daya jingina a jikin bango. Tunanin Iman ne yake damunsa ya saka wannan ya cire, ya saka wancan. Sallamar Najib ce ta katse masa tunani ya amsa a sanyaye yayin da hankalinsa gaba daya ya tattara ga kallon mai shigowa. Kasancewar yamma tayi ga babu wuta, dakin ya fara duhu. Suhaif bai gane fuskar mai shigowa ba duk da yaso ya dauki muryar amma yana kokonto anya kuwa Najib ne zai zo da yammar nan. Kuma a yadda suka yi da Najib ba zaizo yau ba, ya ce zai je Bauchi ya dawo tukunna. Najib ya karaso kan katifar da Suhaif ke zaune ya kama masa hannu suka gaisa sannan Suhaif ya gane ko wanene. Cikin mamaki Suhaif ya ce "Malam Najib kaine, kasan kuwa ban ganeka ba? Gaskiya mutumin nan kayi min zuwan bazata. Najib yayi dariya ya sami waje ya zauna a kusa da Suhaif ya ce "Haba dai, ba dai tun shigowata baka gane ni ba. Na dauka zaka gane muryar? Suhaif ya ce "Naso in dau muryar saina ce kai ba kai bane yaushe ka dawo daga Bauchi? Ko dai *yar Bauchin za'a samo mana ne? Ka cika yawan zuwa Bauchi. Su duka suka tuntsire da dariya. Naji ya ce "Kai wallahi ka cika rudu, bana gaya maka bikin Aliyu Bauchi course mate dina muke ba? Kasan ni ai sai Samira Tukur, bayan har yanzu yarinyar nan garani take ban samu shiga ba ina ni ina jijjibo wata kuma? Samira ta cika yanga da yawa. Suhaif ya fada yayin da yake tabe baki.. Najib ya kwashe da dariya ya ce "To meye kake tabe baki? Suhaif ya ce "Ai haka take idan zata yi magana a wani tabe baki a yatsune fuska kafin ta gaishe da mutum shi yasa ban cika rakaka ba wajenta.
Yanzu a label nawa take ne? Najib ya ce "Lebel two ta shiga tana Micro-biology anan B.U.K Old Side.
Najib ya gyara zama ya ce "Daman labari na kawo maka da dimi-dimi, da sai gobe zanzo naga kai gara in zo yau in fesa maka wannan abun farin cikin. Kasan kamar akan kaya nake Allah-Allah nake su turamu bautar kasa nan muje muyi mu dawo mu sami aiki mu ma a dama damu a gwamnati, Babana yana da abokai a kusoshin gwamnati. Last week ma ya kirani falonsa ya dubeni ya ce, "Wai kai da dan uwanka Suhaif yaushe zaku je bautar kasa ku fara aiki har na yiwa abokaina maganarku fa. Na ce "Mun kusa tafiya Baba. Suhaif ya harareshi ya ce "Kai mayen kudi ne wallahi baza ka iya aikin banki ba. Ni har yanzu baka fada mun labarin da ka kawo min da dimi-diminsa ba. Najib ya ce "Ina dawowa daga Bauchi na shiga School na tarar an kafe sunayenmu kowa da garin da zaije bautar kasa. Suhaif ya zabura ya dafe kirji ya ce "Kaga nawa? Najib ya ce "Ba dole ba ai kafin in tsaya in duba nawa naka na fara dubawa an turani Kaduna kai kuma Ogun.
Suhaif ya daka tsalle ya mike tsaye ya ce "Bazai yuwu ba, danme za'a turani kasar inyamurai? Ai nafadawa Baba, indai kudu ne ba inda zani don haka kayi shiru karma ka bari su Baba su sani dan ba zanje ba. Najib ya mike ya nufi kofar fita yana cewa "Kai wallahi dan yawa ne, bari in fadawa Baban da kaina dole ma kaje. Suhaif ya damko Najib ya rike shi, Najib kuma na kokarin fisgewa. Baba ya zo wucewa ya gansu suna kiciniya. Ya daka tsawa ya ce "Meye hakan, kamar wasu *yan yara kuke wasan kunce? Najib ya kyalkyale da dariya ya durkusa ya gaishe da Baba sannan ya gaya masa abunda yake faruwa. Suhaif kuwa sai bata rai yake yana tsaye yana hararar Najib. Baba ya fusata ya sharba masa Carbin dake hannunsa ya rufe shi da fada fafafafa "Sai kaje wallahi. Ko na mutu na bar wasiyya a tura ka. Yaro ka gama karatu bautar kasa ta gagareka wai kai sai arewa, kudun zaka je dole ne ai. Najib ya yiwa Baba sallama ya ce ba kwana zai yi ba.
Reedwan [[f9.heart]] Iman [[f9.heart]] Matawata ....... Mai mace daya aminin Gwauro.
Su wa'e a dage ai aure..
SAI GOBE IDAN ALLAH YA KAIMU
Reedwan Suraj Isma'il
08098715332 @watsapp
_____________________ YARENA ADDININA
CI GABAN LABARIN
Yanzu a label nawa take ne? Najib ya ce "Lebel two ta shiga tana Micro-biology anan B.U.K Old Side.
Najib ya gyara zama ya ce "Daman labari na kawo maka da dimi-dimi, da sai gobe zanzo naga kai gara in zo yau in fesa maka wannan abun farin cikin. Kasan kamar akan kaya nake Allah-Allah nake su turamu bautar kasa nan muje muyi mu dawo mu sami aiki mu ma a dama damu a gwamnati, Babana yana da abokai a kusoshin gwamnati. Last week ma ya kirani falonsa ya dubeni ya ce, "Wai kai da dan uwanka Suhaif yaushe zaku je bautar kasa ku fara aiki har na yiwa abokaina maganarku fa. Na ce "Mun kusa tafiya Baba. Suhaif ya harareshi ya ce "Kai mayen kudi ne wallahi baza ka iya aikin banki ba. Ni har yanzu baka fada mun labarin da ka kawo min da dimi-diminsa ba. Najib ya ce "Ina dawowa daga Bauchi na shiga School na tarar an kafe sunayenmu kowa da garin da zaije bautar kasa. Suhaif ya zabura ya dafe kirji ya ce "Kaga nawa? Najib ya ce "Ba dole ba ai kafin in tsaya in duba nawa naka na fara dubawa an turani Kaduna kai kuma Ogun.
Suhaif ya daka tsalle ya mike tsaye ya ce "Bazai yuwu ba, danme za'a turani kasar inyamurai? Ai nafadawa Baba, indai kudu ne ba inda zani don haka kayi shiru karma ka bari su Baba su sani dan ba zanje ba. Najib ya mike ya nufi kofar fita yana cewa "Kai wallahi dan yawa ne, bari in fadawa Baban da kaina dole ma kaje. Suhaif ya damko Najib ya rike shi, Najib kuma na kokarin fisgewa. Baba ya zo wucewa ya gansu suna kiciniya. Ya daka tsawa ya ce "Meye hakan, kamar wasu *yan yara kuke wasan kunce? Najib ya kyalkyale da dariya ya durkusa ya gaishe da Baba sannan ya gaya masa abunda yake faruwa. Suhaif kuwa sai bata rai yake yana tsaye yana hararar Najib. Baba ya fusata ya sharba masa Carbin dake hannunsa ya rufe shi da fada fafafafa "Sai kaje wallahi. Ko na mutu na bar wasiyya a tura ka. Yaro ka gama karatu bautar kasa ta gagareka wai kai sai arewa, kudun zaka je dole ne ai. Najib ya yiwa Baba sallama ya ce ba kwana zai yi ba.
Reedwan [[f9.heart]] Iman [[f9.heart]] Matawata ....... Mai mace daya aminin Gwauro.
Su wa'e a dage ai aure..
SAI GOBE IDAN ALLAH YA KAIMU
Reedwan Suraj Isma'il
08098715332 @watsapp
_____________________ YARENA ADDININA
CI GABAN LABARIN