Sashe 39
Yarena Addinina Part Complete Hausa Novel · about 6 min read
Yakaini kofar gidan Hajiya mai sayar da gwal, saina kafe a bayan babur naki sauka, na ce sai dai in bashi ya shiga ciki ya sayar mun idan ta ganni yarinya zata ki saya ta ce na sata ne, shi kuwa babba ne zata siya. Bai yi musu ba ya kashe babur na debo su daga jakata na hada da zoben dake hannuna na mika masa. Ya aika yaro cikin gidan akayi masa sallama da ita suka tsaya a zaure suka yi ciniki ta shiga gida ta dauko masa kudin. Ina kallonsa bayan matar ta shiga cikin gida sai ya debi wasu kudin ya zuba a aljihunsa ya fito daga zauren ya nufo inda nake, ban nuna na ganshi ba ya mikomin kudin na karba nayi godiya. Ban damu da cutar da yayi mun ba ganin kudin cunkus ya bani. Ya buga babur muka tafi. Na sake mamaita masa "Ka kaini tashar Kano yace "An gama *yan mata.
Muka isa tasha na sauko daga kan babur na dauko kudi mai yawa na bashi, ya sani, nima nasan yafi kudin aikin da yayi mun. Yana ta godiya muka yi sallama na nufi wajan motoci shi kuma ya buga babur dinsa yana mai matukar farin ciki shikam ranar kamar danshi na sayar da gwal dinnan, saboda kudin da ya samu.
Nayi tambaya ina zanje in hau motar Kano? Aka nuna mun, kwarai kuwa gaskiya ne, Kano garine na Musulmai da Musulunci. Domin matan dana iske a layin yankar tikitin shiga mota sun burgeni gaba dayansu sanye suke da hijabai har kasa wasu harda abun lullube fuska wato (nikaf) nabi layi nima a bayansu. Kamar yadda naga suna yi duk wacce ta mika kudinta aka yankar mata tikiti sai ta dauki jakar kayanta ta shiga cikin zungureriyar mota. Layi yazo kaina na tambayeshi nawa ne? Ya fada mun na zaro kudin na bashi ya bani tikiti saina dauki jakata na shiga mota. Na shiga cikin mota ina ta baza ido ina neman wajan da zan zauna, kasancewar motar tana da kujerun zaman mutane bibbiyu ne a layi-layi. Kowanne layi ya cika da mutane. Hankalina ya tashi ganin zan rasa wajen zama kuma kowa abokin tafiyarsa yake tanadarwa kusa dashi, ni kuwa ni kadaice bansan kowa ba. Amma zuciyata tayi sanyi hankalina ya kwanta ganin kowacce na hada ido da ita sai tayi mun murmushi tace mun "Salamu alaikim. Na wuce can karshen motar saina iske wata mata ita kadai, koda taga na tunkaro wajenta nan da nan ta dauke jakarta ta nuna mun kusa da ita ta ce in zo in zauna. Ina zama a kusa da ita saita mikomun hannu gami da cemun "Salamu alaikim". Muka gaisa. Nayi ajiyar zuciya na ce a zuciyata "Addinin Musulunci kenan, Musulmi suna son *yan uwansu Musulmai.
Mota ta cika aka rufe kofar mota, direba ya shiga ya kunna mota ya ja muka fara tafiya, yayin da hawaye ya kece mun. Matar da ta ke kusa dani ta lura da kuka nake sai ta shiga yimun tambayoyi meya sameni nake kuka? Duk ta damu ta rikice tana tambayata. Na rasa amsar da zan bata na goge hawayena na hau murmushin dole. Ta fara mun nasiha tana jawomin aya tana bani musalai da rayuwar da sahabbai suka yi, daman duniya kurkukun mumini ce sai lahira zaiji dadi dan haka duk yawancin masu holewa a duniya su sha giya, suyi zina, suyi sata, su suke jin dadin duniya lahirarsu kuwa tamkar kurkukunsu ne. Nan ma naji na karu da abunda ta fadamun na rike a zuciyata. Sai na fara tambayarta ita *yar Kano ce ko *yar Jalingo ce? Ko da yake naji ta iya Hausa sosai daga dukkan alamu *yar Kano ce. Sai ta ce mun ita *yar Kano ce aure ya kawota Jalingo, amma duk shekara tana zuwa Kano. Na sake tambayarta ganin gida take zuwa. Sai ta ce "Bama ganin gida kawai ba, kinsan wannan watan Azumi ne duk gomar karshe muna shiga Ittikafi a Masallaci har sai ranar sallah muke fitowa muna Masallaci muna ibada. Nayi shiru na kasa magana tunda bansan har an fara azumi ba an yi kusan ashirin. Sai dai duk sanda na shiga gidansu Huzaifa sai suce min suna azumi, bansan Ramadan bane koma na sani ai ba damar inyi a gidanmu. Ina mata tambayoyi tana amsamin duk yadda suke yi. Ta nuna min sauran tawagar tafiyarta ta ce haka suke yi duk shekara a Masallacin BUK old site suke zama har kwana goma suna sallah cikin dare suna addu'o'i. Nan danan na ce mata nima zan bita inje mu kwana goma. Ta dube ni cike da mamaki sai ta tambayeni "Kin fadawa iyayenki sun yadda? Na Marairaice na fara hawaye na ce "Ai ni marainiya ce, aikin wanke-wanke da shara nake a Jalingo suka koreni, shine zan taho Kano ko zan samu wani aikin. Sai naga ta kuramin ido tana min kallon kurilla daga ni har kayan jikina. Da alama taga babu wahala a tare dani, sai ta shiga wani tunani mai zurfi. Dana ga haka dan karta gane ni sai na hau tsarata yadda zata yadda da ni na ce "Sun rike ni amana a gidan aikin tamkar *yar gida tun ina karama, sun saka ni a makaranta, to tun lokacin da mai gidan ya ce yana sona matar gidan ta tsaneni ta kore ni. Nan da nan matar ta gaskata abunda nake fada mata ta ce "Eh kwarai dole ta kore ki karki aure mata miji, to Allah Ya kyauta. Ta yi shiru bata sake cewa komai ba muka ci gaba da tafiya, Jalingo da Kano akwai nisa. Duk inda muka tsaya salla sai matar ta siya mana abubuwan ciye-ciye kona roketa ta bari in siya da kudina sai ta ki. Ganin duk suna azumi nima sai in ajiye in ki ci ina jiran sai an sha ruwa. Amma ta lura bana azumi sai ta ce min "Zan iya ajiye azumin saboda ni matafiya ce bayan sallah sai na rama azumin. Na ce "A'a azumi nake nima. Sai daf da zamu shiga Kano aka kira sallar Magaruba, dukkan mu muka yi buda baki da abubuwan da muka siya. Mun isa Masallacin BUK ana kiran sallar isha'i.
Mun iske mata da yawa masu zaman Ittifaki, haka wasu da yawa sun zo bayanmu. Na sha mamaki dana ga wasu harda kayan abincinsu danye da rusho din dahuwa kamar a gida. Sunan matar da muke tare da ita Maman Aisha. Tana da kirki sosai kamar yadda ya kamata, tana kaunata tamkar jininta, naji dadin zama da ita kamar yadda taji dadin zama dani. Ta bani hijab dogo har kasa haka duk wasu ayyuka da suka taso da rawar jiki zan tashi inyi bana barinta ta wanke ko cokali. Muna zaman lafiya da kowa, *yan uwa Musulmi masu neman ladan ciyarwa a cikin wannan watan mai girma na azumi suna ta tururuwar kawo abinci sadaka cikin Masallaci, don haka akwai wadatar abinci kuma idan wasu daga cikinmu suka dafa suna kiran kowa da kowa a taru aci saboda Allah.
Muna yini ibada, mu kwana ibada, bayan sallolin farilla da muke bin jam'i, daga karfe sha biyun dare mata suke tururuwa su taru a Masallacinmu ana cika taf har wasu a waje saboda cika. Maza kuma a bangaransu babu mai ganin wani idan aka fara salla har asuba. Allahu Akbar! Lallai Musulmi su suke ibada tukuru da jikinsu kuma duk mulkinka da kudinka. Na sha wuya kafin in saba dare da rana sallah, ga yunwar azumi amma zuciyata a dake take na sawa raina son Musulunci, kafin kwana gomar nan harna saba na daina gajiya. Ba shakka wannan shine mafarkin da nayi, sahun sallah sahu-sahu sannan ayi karatun kur'ani. Ina nacewa Maman Amina tana biyamin karatun kur'ani na kuwa fara koya yadda ya kamata.
RANAR SALLAH. !!!
ALLAH YA KARA DAUKAKA MUSULUNCI DA MUSULMAI AMEEN
Reedwan Suraj Isma'il
*************** YAREANA ADDININA
___CIGABAN LABARI
Muka isa tasha na sauko daga kan babur na dauko kudi mai yawa na bashi, ya sani, nima nasan yafi kudin aikin da yayi mun. Yana ta godiya muka yi sallama na nufi wajan motoci shi kuma ya buga babur dinsa yana mai matukar farin ciki shikam ranar kamar danshi na sayar da gwal dinnan, saboda kudin da ya samu.
Nayi tambaya ina zanje in hau motar Kano? Aka nuna mun, kwarai kuwa gaskiya ne, Kano garine na Musulmai da Musulunci. Domin matan dana iske a layin yankar tikitin shiga mota sun burgeni gaba dayansu sanye suke da hijabai har kasa wasu harda abun lullube fuska wato (nikaf) nabi layi nima a bayansu. Kamar yadda naga suna yi duk wacce ta mika kudinta aka yankar mata tikiti sai ta dauki jakar kayanta ta shiga cikin zungureriyar mota. Layi yazo kaina na tambayeshi nawa ne? Ya fada mun na zaro kudin na bashi ya bani tikiti saina dauki jakata na shiga mota. Na shiga cikin mota ina ta baza ido ina neman wajan da zan zauna, kasancewar motar tana da kujerun zaman mutane bibbiyu ne a layi-layi. Kowanne layi ya cika da mutane. Hankalina ya tashi ganin zan rasa wajen zama kuma kowa abokin tafiyarsa yake tanadarwa kusa dashi, ni kuwa ni kadaice bansan kowa ba. Amma zuciyata tayi sanyi hankalina ya kwanta ganin kowacce na hada ido da ita sai tayi mun murmushi tace mun "Salamu alaikim. Na wuce can karshen motar saina iske wata mata ita kadai, koda taga na tunkaro wajenta nan da nan ta dauke jakarta ta nuna mun kusa da ita ta ce in zo in zauna. Ina zama a kusa da ita saita mikomun hannu gami da cemun "Salamu alaikim". Muka gaisa. Nayi ajiyar zuciya na ce a zuciyata "Addinin Musulunci kenan, Musulmi suna son *yan uwansu Musulmai.
Mota ta cika aka rufe kofar mota, direba ya shiga ya kunna mota ya ja muka fara tafiya, yayin da hawaye ya kece mun. Matar da ta ke kusa dani ta lura da kuka nake sai ta shiga yimun tambayoyi meya sameni nake kuka? Duk ta damu ta rikice tana tambayata. Na rasa amsar da zan bata na goge hawayena na hau murmushin dole. Ta fara mun nasiha tana jawomin aya tana bani musalai da rayuwar da sahabbai suka yi, daman duniya kurkukun mumini ce sai lahira zaiji dadi dan haka duk yawancin masu holewa a duniya su sha giya, suyi zina, suyi sata, su suke jin dadin duniya lahirarsu kuwa tamkar kurkukunsu ne. Nan ma naji na karu da abunda ta fadamun na rike a zuciyata. Sai na fara tambayarta ita *yar Kano ce ko *yar Jalingo ce? Ko da yake naji ta iya Hausa sosai daga dukkan alamu *yar Kano ce. Sai ta ce mun ita *yar Kano ce aure ya kawota Jalingo, amma duk shekara tana zuwa Kano. Na sake tambayarta ganin gida take zuwa. Sai ta ce "Bama ganin gida kawai ba, kinsan wannan watan Azumi ne duk gomar karshe muna shiga Ittikafi a Masallaci har sai ranar sallah muke fitowa muna Masallaci muna ibada. Nayi shiru na kasa magana tunda bansan har an fara azumi ba an yi kusan ashirin. Sai dai duk sanda na shiga gidansu Huzaifa sai suce min suna azumi, bansan Ramadan bane koma na sani ai ba damar inyi a gidanmu. Ina mata tambayoyi tana amsamin duk yadda suke yi. Ta nuna min sauran tawagar tafiyarta ta ce haka suke yi duk shekara a Masallacin BUK old site suke zama har kwana goma suna sallah cikin dare suna addu'o'i. Nan danan na ce mata nima zan bita inje mu kwana goma. Ta dube ni cike da mamaki sai ta tambayeni "Kin fadawa iyayenki sun yadda? Na Marairaice na fara hawaye na ce "Ai ni marainiya ce, aikin wanke-wanke da shara nake a Jalingo suka koreni, shine zan taho Kano ko zan samu wani aikin. Sai naga ta kuramin ido tana min kallon kurilla daga ni har kayan jikina. Da alama taga babu wahala a tare dani, sai ta shiga wani tunani mai zurfi. Dana ga haka dan karta gane ni sai na hau tsarata yadda zata yadda da ni na ce "Sun rike ni amana a gidan aikin tamkar *yar gida tun ina karama, sun saka ni a makaranta, to tun lokacin da mai gidan ya ce yana sona matar gidan ta tsaneni ta kore ni. Nan da nan matar ta gaskata abunda nake fada mata ta ce "Eh kwarai dole ta kore ki karki aure mata miji, to Allah Ya kyauta. Ta yi shiru bata sake cewa komai ba muka ci gaba da tafiya, Jalingo da Kano akwai nisa. Duk inda muka tsaya salla sai matar ta siya mana abubuwan ciye-ciye kona roketa ta bari in siya da kudina sai ta ki. Ganin duk suna azumi nima sai in ajiye in ki ci ina jiran sai an sha ruwa. Amma ta lura bana azumi sai ta ce min "Zan iya ajiye azumin saboda ni matafiya ce bayan sallah sai na rama azumin. Na ce "A'a azumi nake nima. Sai daf da zamu shiga Kano aka kira sallar Magaruba, dukkan mu muka yi buda baki da abubuwan da muka siya. Mun isa Masallacin BUK ana kiran sallar isha'i.
Mun iske mata da yawa masu zaman Ittifaki, haka wasu da yawa sun zo bayanmu. Na sha mamaki dana ga wasu harda kayan abincinsu danye da rusho din dahuwa kamar a gida. Sunan matar da muke tare da ita Maman Aisha. Tana da kirki sosai kamar yadda ya kamata, tana kaunata tamkar jininta, naji dadin zama da ita kamar yadda taji dadin zama dani. Ta bani hijab dogo har kasa haka duk wasu ayyuka da suka taso da rawar jiki zan tashi inyi bana barinta ta wanke ko cokali. Muna zaman lafiya da kowa, *yan uwa Musulmi masu neman ladan ciyarwa a cikin wannan watan mai girma na azumi suna ta tururuwar kawo abinci sadaka cikin Masallaci, don haka akwai wadatar abinci kuma idan wasu daga cikinmu suka dafa suna kiran kowa da kowa a taru aci saboda Allah.
Muna yini ibada, mu kwana ibada, bayan sallolin farilla da muke bin jam'i, daga karfe sha biyun dare mata suke tururuwa su taru a Masallacinmu ana cika taf har wasu a waje saboda cika. Maza kuma a bangaransu babu mai ganin wani idan aka fara salla har asuba. Allahu Akbar! Lallai Musulmi su suke ibada tukuru da jikinsu kuma duk mulkinka da kudinka. Na sha wuya kafin in saba dare da rana sallah, ga yunwar azumi amma zuciyata a dake take na sawa raina son Musulunci, kafin kwana gomar nan harna saba na daina gajiya. Ba shakka wannan shine mafarkin da nayi, sahun sallah sahu-sahu sannan ayi karatun kur'ani. Ina nacewa Maman Amina tana biyamin karatun kur'ani na kuwa fara koya yadda ya kamata.
RANAR SALLAH. !!!
ALLAH YA KARA DAUKAKA MUSULUNCI DA MUSULMAI AMEEN
Reedwan Suraj Isma'il
*************** YAREANA ADDININA
___CIGABAN LABARI