Sashe 57
Yarena Addinina Part Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kwanci tashi shekarar auren su Najib uku. Su Naja'at har sun gama bautar kasa. Zubaida ta haifi *yan biyu mace da namiji aka saka musu suna Hauwa da Adam. Amma Naja'at da Najib Allah bai basu haihuwa ba, suna neman haihuwa ido rufe.
Suhaif da Najib suka je Umara a watan Maulud. Ba su cika zama a katafaren Hotel din da suka sauka ba, koda yaushe suna Harami. Babu abin da suke sai ibada, babbar matsalar Najib shine Allah Ya basu haihuwa shi da matarsa Naja'at, sai kuma Allah Yasa a kara masa girma a wajen aiki. Suhaif kuwa bayan ya nemawa kansa da Iyayensa gafara, sai addu'ar Allah Ya hada shi da Iman kuma ya aureta. Domin ya kasa aure har yanzu bayan duk abokansa da kannansa sun yi aure sun hayayyafa. Dawafi suke tayi, Suhaif ya daga hannu yana addu'a fadi yake "Allah Ka jeho min Iman ina zuwa Nigeria, Allah Ka sa in auri Iman. Allah Kai ka halicceni ka halicci Iman Allah Kasa Iman ce matata. Allah Kai ka hadani da Iman Ka rabamu Allah Ka sake hada mu alfarmar Annabinka Muhammad (S.A.W). Najib dake kusa dashi ya karasa salatin. Suhaif ya juya ya kalli Najib ya ce "Daman kana jin abunda nake cewa? Najib ya ce "Wanda yake nesa da kai ma zai ji balle ni da nake kusa dakai, ai a fili kake fada baro-baro. Ina jinka wannan shine zagayenmu na shidda amma abu daya kake roko Iman! Iman!! Iman!!! Kawai kake ambato. Ba gara ka dinga sirkawa da idan ba ita ba wata da ta fita. Wani tsoho Bahaushe a bayansu ya ce "Ai ina bayanku duk zagayen nan da kuke yi Iman kawai kake kira. Wasu mata larabawa guda biyu a gabansu kawaye ko kuma ya da kanwa suma tare suke zagayen sai suka waiwayo suna kallon Suhaif kamar sun san su ko kuma suna jin abunda suke cewa. Duk da dai bakaken kayane a jikin matan tun daga sama har kasa babu abinda zaka gani sai farin tafin hannunsu. Sun rufe fuskarsu da nikaf. Hawaye ya kwararo daga idanuwan Suhaif ganin ya fara zautuwa har ya zama abin kallo saboda ambaton Iman. Son ta ya zame masa tamkar numfashinsa, yadda dole zaiyi numfashi haka dole Iman tana ransa.
Da suka kewayo na bakwai kenan, sai suka yi kokarin fitowa daga wajen dawafin zuwa bayan mukami Ibrahim dan suyi sallar Nafila raka'a biyu wacce ake yi idan an gama dawafi. Tare suka fito da Bahaushe tsohon nan na bayansu da matan larabawan nan guda biyu na gabansu suma sun yi zagaye bakwai. Suka yi nafila a waje daya. Dai-dai lokacin aka kira sallar magruba. Suka jira aka yi sallar Isha'ai. Suhaif yana addu'a, sai Najib ya ce da Suhaif "Muna jinka fa har yanzu. A zuciyarsa yake addu'a amma baya sanin sanda addu'ar take fitowa, Iman dai yake kira. Tsohon nan ya ce da Suhaif "Yaro wacece Iman? Najib ya ce "Wacce yake so ya aura amma bai san inda take ba, kuma ya kasa daina sonta. Tsohon ya ce "Allah Sarki sannu yaro, Allah mai amsa addu'a ne zai bayyana maka ita kaji ko Insha Allah. Suhaif ya kasa magana amma a zuciyarsa yace amin.
Daya daga cikin larabawan nan biyu ta matso tayi musu sallama, su duka ukun suka amsa. Tayi magana da larabci, su duka ukun basu gane abunda take cewa ba. Sai suka ji tayi Hausa ta ce "Allah mai karbar addu'a ya hadaka da Iman. Sai suka zazzare idanu suna kallon-kallo, su kalli junansu su kalleta babu wanda ya iya bata amsa ko kuma ya tambayeta me take nufi. Babban abun mamaki Balarabiyar Saudia da ta iya Hausa radau. Bayan wannan ma ya akayi tasan sunan Suhaif. Tasa hannayenta farare tas ta bude nikafin dake fuskarta sai ga fuskar Iman. Iman ce Allah ya hada Suhaif da ita inda bai taba tsammani ba. Su duka ukun suka hada baki suka ce "ALLAHU AKBAR!
Kafin Suhaif ya ce komai sai da ya tashi yayi sallar nafila raka a biyu ya idar sannan ya ce "Iman! Iman!! Kece? Ta yi dariya nan tata mai kayatar da mai kallonta. Ta ce "Yaya Suhaif ni ce. Cike da fargaba yana in-ina ya tambayeta ya ce "Iman kin yi aure? Kafin ta bashi amsa na kusa dashi zai iya jiyo bugun zuciyarsa saboda fargabar irin amsa da zata bashi, ba Suhaif kadai ba har da Najib da tsohon nan zuciyarsu bugawa take uku-uku Allah ya sa amsar ita ce bata yi aure ba. Iman tayi murmushi gami da rufe ido don kunya, can ta dago taga sun zubo mata ido suna jiran abunda zai fito daga bakinta. Ta ce "Banyi aure ba, Najib kai fa kayi aure? Najib ya ce "Eh nayi aure amma Suhaif baiyi ba, su duka suka yi dariya. Najib ya ce "Ai nasan Suhaif kike so ki tambaya ko yayi aure ko baiyi ba, to baiyi ba. Shi kuwa gogan sai murmushi yake kawai dadi zai kashe shi. Najib ya zunguri Suhaif ya ce "Ta shi ka sake yin nafila raka'a biyu bata da aure. Suhaif ya tashi ya tayar da ikama, ita kuma Iman sai dariya take yi musu kawai.
Kamar yadda su Najib suka saba idan suka idar da sallar Isha'i sai su koma Hotel su ci abinci, su yi wanka, sannan su kwanta ba tare da sunyi shafa'i da wutiri ba. Su tashi karfe biyun dare su dawo masallaci suyi ta nafifili har sai kusan asubah sai suyi shafa'i da wutiri, suyi sallar asubah tare da Liman. Bayan an idar sai suyi ta dawafi har gari ya waye. Sannan su koma gida suci abincin safe sai su sake kwanciya suyi barci har sai da azahar suke tashi suyi wanka suci abinci sannan su koma Harami ayi sallar azahar dasu.
Suhaif, Najib, Baba tsoho, Iman da kawarta suka fito daga Masallaci zuwa bakin titi. Iman ta ce "Ya kamata mu je ku ga gidan da nake zaune, Najib ya ce "Tare da *yan garinku ki ka zo? Iman ta ce "A'a ni ai yanzu shekara ta hudu kenan a kasar nan ina karatu a jami'ar koyar da ilimin addini. Na kammala karatun waccan watan muka gama, akwai gidan da nake zama, anan kurkusa babu nisa, mu je ku ga gidan. Suhaif yayi sauri ya amsa mata da "To muje.
Baba tsoho ya mikawa Suhaif da Najib hannu suka gaisa ya ce "To na barku lafiya zan tafi masaukina naga hanyar ba daya ba ce. Suhaif yasa hannu a aljihu ya dauko Riyad da yawa ya bawa tsohon. Mamakin kudin nan mai yawa ya rufe tsoho sai godiya da addu'a yake yiwa Suhaif Allah Yasa Iman rabonsa ce. Suhaif yaji dadin adu'ar baba tsoho. Ya sake ciko hannu da Riyad ya sake bawa tsoho. Tsoho ya sake rike baki yana mamaki. Suhaif ya dauko katin da yake dauke da adreshinsa da nambar waya ya bawa tsohon ya ce idan sun koma Nigeria ya nemeshi zai yi masa alheri. Najib cewa yake "Ai kai dan tsoho Allah Ya hadaka da arzikinka tunda Allah Yasa a gabanka Suhaif yaga Iman. Iman da kawarta suna gefe sai murmushi Iman take kawai.
Suna tafiya a hanya Najib yake cewa "Af ban tambayi sunan kawar taki ba ko gaisawa ba muyi ba. Iman ta ce "Sunanta Zainab ai bata jin Hausa kuma bata jin turanci Balarabiyar baharain ce. Da kyar Iman ta yarda suka jera da su Suhaif saboda girmamawa sai take tsayawa a bayansu. Saida Suhaif ya roketa sannan ta yarda suka jera. Farin ciki ya hana Suhaif magana sosai, Najib da Iman ne suke hira. Idan za'a auna yawan farin cikin Suhaif da Iman ban san na wanda zai rinjayi na wani ba.
Yo aini bakin ciki ne ya rufe ni, na san ba na da wani abin katabus da na shiga takara, tunda har yanzu Hamma Huzaifa ya na sonta,,,, uhmmm wayyoni Masoyiyata!!!
Reedwan Suraj Isma'il
:::::::::::::::::::::::::::::: YARENA ADDININA
___CIGABAN LABARI
Suhaif da Najib suka je Umara a watan Maulud. Ba su cika zama a katafaren Hotel din da suka sauka ba, koda yaushe suna Harami. Babu abin da suke sai ibada, babbar matsalar Najib shine Allah Ya basu haihuwa shi da matarsa Naja'at, sai kuma Allah Yasa a kara masa girma a wajen aiki. Suhaif kuwa bayan ya nemawa kansa da Iyayensa gafara, sai addu'ar Allah Ya hada shi da Iman kuma ya aureta. Domin ya kasa aure har yanzu bayan duk abokansa da kannansa sun yi aure sun hayayyafa. Dawafi suke tayi, Suhaif ya daga hannu yana addu'a fadi yake "Allah Ka jeho min Iman ina zuwa Nigeria, Allah Ka sa in auri Iman. Allah Kai ka halicceni ka halicci Iman Allah Kasa Iman ce matata. Allah Kai ka hadani da Iman Ka rabamu Allah Ka sake hada mu alfarmar Annabinka Muhammad (S.A.W). Najib dake kusa dashi ya karasa salatin. Suhaif ya juya ya kalli Najib ya ce "Daman kana jin abunda nake cewa? Najib ya ce "Wanda yake nesa da kai ma zai ji balle ni da nake kusa dakai, ai a fili kake fada baro-baro. Ina jinka wannan shine zagayenmu na shidda amma abu daya kake roko Iman! Iman!! Iman!!! Kawai kake ambato. Ba gara ka dinga sirkawa da idan ba ita ba wata da ta fita. Wani tsoho Bahaushe a bayansu ya ce "Ai ina bayanku duk zagayen nan da kuke yi Iman kawai kake kira. Wasu mata larabawa guda biyu a gabansu kawaye ko kuma ya da kanwa suma tare suke zagayen sai suka waiwayo suna kallon Suhaif kamar sun san su ko kuma suna jin abunda suke cewa. Duk da dai bakaken kayane a jikin matan tun daga sama har kasa babu abinda zaka gani sai farin tafin hannunsu. Sun rufe fuskarsu da nikaf. Hawaye ya kwararo daga idanuwan Suhaif ganin ya fara zautuwa har ya zama abin kallo saboda ambaton Iman. Son ta ya zame masa tamkar numfashinsa, yadda dole zaiyi numfashi haka dole Iman tana ransa.
Da suka kewayo na bakwai kenan, sai suka yi kokarin fitowa daga wajen dawafin zuwa bayan mukami Ibrahim dan suyi sallar Nafila raka'a biyu wacce ake yi idan an gama dawafi. Tare suka fito da Bahaushe tsohon nan na bayansu da matan larabawan nan guda biyu na gabansu suma sun yi zagaye bakwai. Suka yi nafila a waje daya. Dai-dai lokacin aka kira sallar magruba. Suka jira aka yi sallar Isha'ai. Suhaif yana addu'a, sai Najib ya ce da Suhaif "Muna jinka fa har yanzu. A zuciyarsa yake addu'a amma baya sanin sanda addu'ar take fitowa, Iman dai yake kira. Tsohon nan ya ce da Suhaif "Yaro wacece Iman? Najib ya ce "Wacce yake so ya aura amma bai san inda take ba, kuma ya kasa daina sonta. Tsohon ya ce "Allah Sarki sannu yaro, Allah mai amsa addu'a ne zai bayyana maka ita kaji ko Insha Allah. Suhaif ya kasa magana amma a zuciyarsa yace amin.
Daya daga cikin larabawan nan biyu ta matso tayi musu sallama, su duka ukun suka amsa. Tayi magana da larabci, su duka ukun basu gane abunda take cewa ba. Sai suka ji tayi Hausa ta ce "Allah mai karbar addu'a ya hadaka da Iman. Sai suka zazzare idanu suna kallon-kallo, su kalli junansu su kalleta babu wanda ya iya bata amsa ko kuma ya tambayeta me take nufi. Babban abun mamaki Balarabiyar Saudia da ta iya Hausa radau. Bayan wannan ma ya akayi tasan sunan Suhaif. Tasa hannayenta farare tas ta bude nikafin dake fuskarta sai ga fuskar Iman. Iman ce Allah ya hada Suhaif da ita inda bai taba tsammani ba. Su duka ukun suka hada baki suka ce "ALLAHU AKBAR!
Kafin Suhaif ya ce komai sai da ya tashi yayi sallar nafila raka a biyu ya idar sannan ya ce "Iman! Iman!! Kece? Ta yi dariya nan tata mai kayatar da mai kallonta. Ta ce "Yaya Suhaif ni ce. Cike da fargaba yana in-ina ya tambayeta ya ce "Iman kin yi aure? Kafin ta bashi amsa na kusa dashi zai iya jiyo bugun zuciyarsa saboda fargabar irin amsa da zata bashi, ba Suhaif kadai ba har da Najib da tsohon nan zuciyarsu bugawa take uku-uku Allah ya sa amsar ita ce bata yi aure ba. Iman tayi murmushi gami da rufe ido don kunya, can ta dago taga sun zubo mata ido suna jiran abunda zai fito daga bakinta. Ta ce "Banyi aure ba, Najib kai fa kayi aure? Najib ya ce "Eh nayi aure amma Suhaif baiyi ba, su duka suka yi dariya. Najib ya ce "Ai nasan Suhaif kike so ki tambaya ko yayi aure ko baiyi ba, to baiyi ba. Shi kuwa gogan sai murmushi yake kawai dadi zai kashe shi. Najib ya zunguri Suhaif ya ce "Ta shi ka sake yin nafila raka'a biyu bata da aure. Suhaif ya tashi ya tayar da ikama, ita kuma Iman sai dariya take yi musu kawai.
Kamar yadda su Najib suka saba idan suka idar da sallar Isha'i sai su koma Hotel su ci abinci, su yi wanka, sannan su kwanta ba tare da sunyi shafa'i da wutiri ba. Su tashi karfe biyun dare su dawo masallaci suyi ta nafifili har sai kusan asubah sai suyi shafa'i da wutiri, suyi sallar asubah tare da Liman. Bayan an idar sai suyi ta dawafi har gari ya waye. Sannan su koma gida suci abincin safe sai su sake kwanciya suyi barci har sai da azahar suke tashi suyi wanka suci abinci sannan su koma Harami ayi sallar azahar dasu.
Suhaif, Najib, Baba tsoho, Iman da kawarta suka fito daga Masallaci zuwa bakin titi. Iman ta ce "Ya kamata mu je ku ga gidan da nake zaune, Najib ya ce "Tare da *yan garinku ki ka zo? Iman ta ce "A'a ni ai yanzu shekara ta hudu kenan a kasar nan ina karatu a jami'ar koyar da ilimin addini. Na kammala karatun waccan watan muka gama, akwai gidan da nake zama, anan kurkusa babu nisa, mu je ku ga gidan. Suhaif yayi sauri ya amsa mata da "To muje.
Baba tsoho ya mikawa Suhaif da Najib hannu suka gaisa ya ce "To na barku lafiya zan tafi masaukina naga hanyar ba daya ba ce. Suhaif yasa hannu a aljihu ya dauko Riyad da yawa ya bawa tsohon. Mamakin kudin nan mai yawa ya rufe tsoho sai godiya da addu'a yake yiwa Suhaif Allah Yasa Iman rabonsa ce. Suhaif yaji dadin adu'ar baba tsoho. Ya sake ciko hannu da Riyad ya sake bawa tsoho. Tsoho ya sake rike baki yana mamaki. Suhaif ya dauko katin da yake dauke da adreshinsa da nambar waya ya bawa tsohon ya ce idan sun koma Nigeria ya nemeshi zai yi masa alheri. Najib cewa yake "Ai kai dan tsoho Allah Ya hadaka da arzikinka tunda Allah Yasa a gabanka Suhaif yaga Iman. Iman da kawarta suna gefe sai murmushi Iman take kawai.
Suna tafiya a hanya Najib yake cewa "Af ban tambayi sunan kawar taki ba ko gaisawa ba muyi ba. Iman ta ce "Sunanta Zainab ai bata jin Hausa kuma bata jin turanci Balarabiyar baharain ce. Da kyar Iman ta yarda suka jera da su Suhaif saboda girmamawa sai take tsayawa a bayansu. Saida Suhaif ya roketa sannan ta yarda suka jera. Farin ciki ya hana Suhaif magana sosai, Najib da Iman ne suke hira. Idan za'a auna yawan farin cikin Suhaif da Iman ban san na wanda zai rinjayi na wani ba.
Yo aini bakin ciki ne ya rufe ni, na san ba na da wani abin katabus da na shiga takara, tunda har yanzu Hamma Huzaifa ya na sonta,,,, uhmmm wayyoni Masoyiyata!!!
Reedwan Suraj Isma'il
:::::::::::::::::::::::::::::: YARENA ADDININA
___CIGABAN LABARI