Sashe 59
Yarena Addinina Part Complete Hausa Novel · about 4 min read
Suhaif da dan Uwansa Najib basu fasa nafilfili ba da dawafi suna addu'ar Allah Ya zaba abunda yafi alheri tsakanin Suhaif da Iman. Har ranar da su Huzaifa suka zo suka dauke su zuwa filin jirgi. Tun bayan da Suhaif ya gaishe da Huzaifa da El-Sadik, Iman ma da matar Huzaifa suka gaishe shi, Suhaif bai sake cewa komai ba har suka shiga jirgi. Ya tafi can nesa ya samu kusa da wani ya zauna. Najib da Huzaifa ne suka zauna kujera daya, Iman da matar Huzaifa a bayansu sai Fatima da Huzaifa *ya*yan Huzaifa suma an balla musu belt din kujeru suna zaune a bayan kujerun su Iman. Har zuka iso Abuja Suhaif bai ce uffan ba haka ko kallon abincin da ake rabawa a jirgi baiyi ba. Zuciyarsa ta nausa ta tafi uwa duniya tana tunanin Iman. Haka Iman ta kasance bata magana sosai saboda damuwar da ta shiga ganin yadda taga Suhaif yana damuwa, ta rasa abun da yake damunsa ga Najib ya ce ba damuwar rashin aurenta ba ya shiga. Tasan Suhaif, tasan halinsa ba haka yake ba ada.
Najib da Huzaifa kuwa hira ce ta rincabe a tsakaninsu suna yi suna kyalkyala dariya suna tafawa kamar da can sun san juna. Har mutanen jirgin duk suka yi shiru sai su kadai suke magana. Ko gyangyadi basu yi ba suna labari har aka iso Abuja. Bayan doguwar mota ta debe su daga bakin jirgi zuwa arrival. Huzaifa yana kokarin saka layinsa na Nigeria ya kira kanwarsa Bilkisu zata aiko da direba ya zo ya daukesu. Sai Najib ya hana shi ya ce ya bari sunyi waya tun kafin su taso, za'a zo da motoci a daukesu tun da tsakar dare ne sai su kwana a gidansu washe gari sai a kaisu inda zasu je. Huzaifa yaje ya sanarwa Iman abunda Najib ya ce, tayi murmushi ta ce ba komai su je su kwana gobe sai su je gidan Bilkisu kanwarsa din.
Motoci guda hudu na alfarma ne suka biyo layi suka zo taryar uban gidansu Suhaif. Tun daga nan Iman da Huzaifa suka fara mamaki kafin suga gidan da za'a kaisu. Sun sha matukar mamaki a lokacin da suka gansu a cikin katafaren gidan Suhaif wanda kirarsa da zubinsa irin na turawane tamkar a America. Amma ba su tantance gidan na Suhaif ne ko na Najib ne. Najib ya kai Huzaifa wani bangare a gidan masaukinsa, ya dawo ya kai Iman da matar Huzaifa da yaran bangaransu. A cikin gidan suke su duka amma wani ba zai ga wani ba saboda girman gidan. Kowanne bangaren yana dauke da tafka-tafkan falo mai dauke da maka-makan bandakuna na alfarma. Lallai gidan Suhaif gida ne kayataccen gaske, ko daga wacce kasa kake sai ka dubeshi ka sake duba, kuma da wuya idan baka ga abunda baka taba gani ba. Iman ta kwana tana tunani ko wannan gidan waye a cikinsu amma bashi ya fi damunta ba irin halin damuwa da Suhaif yake ciki har yaki ya kulata balle ya dubi inda take har yayi mata magana.
Washegari da safe Najib yaje bangaren Huzaifa ya kwankwasa kofa, bayan ya bude sai ya shiga suka gaisa ya ce idan ya kintsa ya fito babban falo zasu karya kumallo. Najib ya fito ya nufi bangaren su Iman, nan ma Iman ce ta leko bayan sun gaisa ya ce suna jiransu a babban falo idan sun kintsa su zo suci abinci, ta amsa da "To gamu nan zuwa. Najib ya wuce bangaren maigida Suhaif dan shima a bangare daban ya kwana. Najib ya shiga ya iske shi a zaune a falo yana kallo da alama ya dade da tashi daga bacci. Bayan Najib yayi masa sallama, Suhaif ya amsa. Ya mika masa hannu suka gaisa sai ya sanar da shi ya fito falo za'a hadu a ci abinci. Suhaif ya dan yatsine fuska ya ce "Bana jin zan iya cin komai yau. Najib ya zauna a kan kujerar dake fuskantar Suhaif ya ce "Gaskiya Suhaif bai dace irin wannan basarwar da shariya da kake yiwa wadannan bayin Allah ba, idan kayi musu haka a Makka amma nan gidanka suka zo. Ba su san maye a ranka ba, basu yi maka laifi ba, to meyasa ba zaka daure zuciyarka ba don karsu dauki wani abu a ransu. Ko baka ci dole ka zauna ayi wasa da dariya, kuma lallai-lallai dole muje Jalingo bikinsu, ka dauki kaddara matar mutum kabarinsa. Hakika abun da Najib ya fada gaskiya ne amma fa bugun da zuciyata take yi, tsananin bakin cikin daya addabeni ba zai bari in zauna a tsakiyar Huzaifa da Iman ina kallonsu ba. Suhaif yake tunani a zuciyarsa. Najib ya katse shi ya ci gaba da cewa "Zancen wasa ya wuce ina gaya maka gaskiya da gaskiya nasan yadda kake ji, duk wani masoyinka zai jiye maka, amma ikon Allah Ya wuce haka, duk yadda Allah Ya so haka ya keyi da bayinsa, ka zubawa Sarautar Allah ido kaga irin matar da zai sauya maka a madadin Iman. Suhaif ya yi ajiyar zuciya ya mike tsaye ya dafa kafadar Najib ya ce "Na ji abun da ka fada, mu je falon ba komai.
Cab! Allah Ya kiyaye,,,, gaskiya soyayya wata wahala ce babba, hmm *
Reedwan Suraj Isma'il
::::::::::::::::::::::::::::: YARENA ADDININA
___CIGABAN LABARI
Najib da Huzaifa kuwa hira ce ta rincabe a tsakaninsu suna yi suna kyalkyala dariya suna tafawa kamar da can sun san juna. Har mutanen jirgin duk suka yi shiru sai su kadai suke magana. Ko gyangyadi basu yi ba suna labari har aka iso Abuja. Bayan doguwar mota ta debe su daga bakin jirgi zuwa arrival. Huzaifa yana kokarin saka layinsa na Nigeria ya kira kanwarsa Bilkisu zata aiko da direba ya zo ya daukesu. Sai Najib ya hana shi ya ce ya bari sunyi waya tun kafin su taso, za'a zo da motoci a daukesu tun da tsakar dare ne sai su kwana a gidansu washe gari sai a kaisu inda zasu je. Huzaifa yaje ya sanarwa Iman abunda Najib ya ce, tayi murmushi ta ce ba komai su je su kwana gobe sai su je gidan Bilkisu kanwarsa din.
Motoci guda hudu na alfarma ne suka biyo layi suka zo taryar uban gidansu Suhaif. Tun daga nan Iman da Huzaifa suka fara mamaki kafin suga gidan da za'a kaisu. Sun sha matukar mamaki a lokacin da suka gansu a cikin katafaren gidan Suhaif wanda kirarsa da zubinsa irin na turawane tamkar a America. Amma ba su tantance gidan na Suhaif ne ko na Najib ne. Najib ya kai Huzaifa wani bangare a gidan masaukinsa, ya dawo ya kai Iman da matar Huzaifa da yaran bangaransu. A cikin gidan suke su duka amma wani ba zai ga wani ba saboda girman gidan. Kowanne bangaren yana dauke da tafka-tafkan falo mai dauke da maka-makan bandakuna na alfarma. Lallai gidan Suhaif gida ne kayataccen gaske, ko daga wacce kasa kake sai ka dubeshi ka sake duba, kuma da wuya idan baka ga abunda baka taba gani ba. Iman ta kwana tana tunani ko wannan gidan waye a cikinsu amma bashi ya fi damunta ba irin halin damuwa da Suhaif yake ciki har yaki ya kulata balle ya dubi inda take har yayi mata magana.
Washegari da safe Najib yaje bangaren Huzaifa ya kwankwasa kofa, bayan ya bude sai ya shiga suka gaisa ya ce idan ya kintsa ya fito babban falo zasu karya kumallo. Najib ya fito ya nufi bangaren su Iman, nan ma Iman ce ta leko bayan sun gaisa ya ce suna jiransu a babban falo idan sun kintsa su zo suci abinci, ta amsa da "To gamu nan zuwa. Najib ya wuce bangaren maigida Suhaif dan shima a bangare daban ya kwana. Najib ya shiga ya iske shi a zaune a falo yana kallo da alama ya dade da tashi daga bacci. Bayan Najib yayi masa sallama, Suhaif ya amsa. Ya mika masa hannu suka gaisa sai ya sanar da shi ya fito falo za'a hadu a ci abinci. Suhaif ya dan yatsine fuska ya ce "Bana jin zan iya cin komai yau. Najib ya zauna a kan kujerar dake fuskantar Suhaif ya ce "Gaskiya Suhaif bai dace irin wannan basarwar da shariya da kake yiwa wadannan bayin Allah ba, idan kayi musu haka a Makka amma nan gidanka suka zo. Ba su san maye a ranka ba, basu yi maka laifi ba, to meyasa ba zaka daure zuciyarka ba don karsu dauki wani abu a ransu. Ko baka ci dole ka zauna ayi wasa da dariya, kuma lallai-lallai dole muje Jalingo bikinsu, ka dauki kaddara matar mutum kabarinsa. Hakika abun da Najib ya fada gaskiya ne amma fa bugun da zuciyata take yi, tsananin bakin cikin daya addabeni ba zai bari in zauna a tsakiyar Huzaifa da Iman ina kallonsu ba. Suhaif yake tunani a zuciyarsa. Najib ya katse shi ya ci gaba da cewa "Zancen wasa ya wuce ina gaya maka gaskiya da gaskiya nasan yadda kake ji, duk wani masoyinka zai jiye maka, amma ikon Allah Ya wuce haka, duk yadda Allah Ya so haka ya keyi da bayinsa, ka zubawa Sarautar Allah ido kaga irin matar da zai sauya maka a madadin Iman. Suhaif ya yi ajiyar zuciya ya mike tsaye ya dafa kafadar Najib ya ce "Na ji abun da ka fada, mu je falon ba komai.
Cab! Allah Ya kiyaye,,,, gaskiya soyayya wata wahala ce babba, hmm *
Reedwan Suraj Isma'il
::::::::::::::::::::::::::::: YARENA ADDININA
___CIGABAN LABARI