Sashe 3
Yarena Addinina Part Complete Hausa Novel · about 6 min read
Mahaifin Suhaif Alh. Hayat dan garin Doko ne haka ma Mahaifiyarsa Raliya. Raliya ita ce matar Alh. Hayat ta farko kuma tun daga kanta bai sake aure ba. Hayatu yana son Raliya sosai don sunyi soyayya mai wahala dakyar iyayensu suka yarda suka daura musu aure, kasancewar Raliya kyakkyawa ce duk garin babu mai kyanta a waccan zamanin, samari da dattijan garin masu kudi da masu sarauta sun fito neman aurenta. Ita kuwa ta ji bata son kowa sai saurayinta Hayatu shi kuma a lokacin maraya ne ba uwa ba uba sai kakansa ne yake rike dashi amma yana da sana'ar yi, da gonar gadonsa makekiya yana nomawa kuma yana da tumakan da yake kiwatawa. Yana da ilimin boko daidai Junior secondry school ya kuma sauke kur'ani yafi a kirga. Ba karamar gwagwarmaya aka sha ba wajen neman auren nan. Kakar Suhaif Hajja ita ta haifi Raliya Mahaifiyarsa. Ta kekashe idanuwanta ta ce ita fa *yar ta ba zata auri dan yaku bayi ba sai mai kudi. Mahaifin Raliya lokacin bai rasu ba shine ya takura Hajja ya canja mata wannan tsattsuaran ra'ayi nata ya ce dole a aurawa Raliya saurayin da take so tunda bai sabawa shari'a ba. Shi musulmi ne kuma yana da sana'ar yi. Dole bada son ran mahaifiyar Raliya ba aka daura musu aure da Hayatu.
Allah Ya albarkace su da *ya*ya mata har uku sai dai kash, da sun fara dan wayo sai su rasu, daga baya ne suka haifi Suhaif. Raliya tayi ta addu'a tayi kuka, tayi fargaba akan tana tsoron ko shima Suhaif mutuwa zaiyi kafin ya girma amma Allah mai komai mai kowa sai Ya raya musu shi har sai da ya shekara shida, sannan akayi masa kanwa mai suna Nadiya ana yaye Nadiya itama ta rasu. Bayan nan ta kara haifar *yan biyu suna rarrafe suka rasu. Hakika wannan rasuwar yara guda shida ba karamin tayar da hankalin Raliya da Hayatu yayi ba suka dukufa da yin addu'a suka rungumi dansu kwaya daya Suhaif, tamkar su hadiyeshi don kauna.
Alh. Hayatu su uku ne a wajen iyayensu akwai Furera itace Babba tana Garki tana aure. Sai Alh. Hayatu sannan kaninsa Usman. Allah ya yiwa Usman arziki don haka yana da katafaren gida a Kano a Unguwar *Yankaba da matarsa Usaina ana kiranta Usai ita *yar Gumel ce suna da *ya*ya uku. Babban dansu sunansa Najib, sai na biyun Sagir sai *yar autarsu Zubaida. Don haka Alh. Hayatu yayi shawarar gara ya dauki dansa kwaya daya jal ya kaishi Kano wajen kaninsa Usman ya hadasu da Najib dansa a saka si a makarantar boko me kyau yadda zaiyi ilimi sosai. Haka kuwa akayi tun daga Nursiry har suka shiga primary tare ajinsu daya Suhaif da Najib kuma daman kamarsu daya tunda iyayensu kamarsu daya kamar an tsaga kara suma kuma kowa da mahaifinsa yayi kama sai dai Suhayf ya dauko farar fatar Mahaifiyarsa da gwarzagwarzan idanuwanta. Suhaif yana firamare aka yi masa kanwa Naja'atu Raliya bata ma dora rai akan Naja'atu ba don taji a jikinta ba rayuwa zata yi ba ita ma. Amma babu wanda yasan gaibu sai Allah Ya raya Naja'atu har ta girma.
Naja'atu Hayatu da Zubaida Usman suma sa'anni ne duk da Naja'atu a garin su Doko tayi karatun firamare sai daga baya ta koma Kano aka hadata da Zubaida a makarantar Sakandire daya wato F.G.C Kano nan suka gama shima Suhaif da Najib F.G.C Azare suka gama suna fita daga sakandire suka wuce Bayero University Kano inda Suhaif ya karanci Enginearing, Najib kuma ya karanci Physic. Sun gama cikin wannan shekarar sakamakonsu ya fito, bautar kasa zasu wuce.
Raliya kuwa su biyu mahaifinsu suka haifa ita da kaninta Nasiru shima ya haifi *ya*yansa da yawa duk suna mutuwa sai Rabi ce kawai tayi saura wato *yar Hajja tana karama mahaifinta ya rasu Hajja ta dauketa shine yanzu take rike da ita.
Naja'at Hayat da Zubaida Usman sun shaku bayan *yan uwantaka ta jini ga kawance, don ko a makaranta ba sa rabuwa har *yan biyu ake kiransu daman kuma kamarsu daya suma sai dai Zubaida ita kuma ta danfi Naja'atu haske. Yanzu ma haka basu fi watanni biyu da kammala karatun sakandiren su ba shine kuma suka dungumo Doko suka zauna har suka shiga makarantar Islamiyya. Kullum da safe daga karfe tara zuwa sha biyun rana, ranar alhamis da juma'a ne kawai basa zuwa makaranta. Sai su zauna a gida suyi ta hira da mahaifiyarsu Raliya wacce suke kira da Goggo tamkar wasu kawayenta. Suyi labari suyi dariya su tafa haka suhaif ma yake zama da mahaifiyarsa yayi ta hira, wasa da dariya, sai dai son girmansa yayi yawa bai cika zama da kannensa Naja'at da Zubaida yayi hira dasu ba. Wani lokaci idan *yan fara'ar basa kusa ko kallansu yayi sai su hau makyarkyata suyi wuf su shige daki. Amma wasu lokutan yakan yi hira dasu, amma yana taka musu birki idan yaji hirar tasu ta fara shiga raini. Yafi yin wasa da *yar Hajja saboda dariya take bashi, bayan kauyancin daya addabi halinta gata rikon Kaka ce, saboda haka tabargazarta tayi yawa.
Fargabar Suhaif da Mahaifansa daya, ita ce a zaman Iman da su Naja'at sun san dole sai Iman ta fuskanci wariyar launin fata don sai sun hade mata kai su biyu sun wareta duk da sa'anni ne su duka ukun. Ba sau daya ba, ba biyu ba Naja'at da Zubaida sun sha yiwa kawayensu halin ko in kula baku damemu ba, kanmu kawai muka sani, bamu san ku ba. Duk kawar data rabesu sukan shareta har ta gaji ta kama gabanta kansu a hade yake su biyu basa son su sami ta uku. Haka kuwa aka yi suka ware Iman suna wani kaf-kaf da junansu ita kuma tana binsu, idan suna hirarsu tazo ta zauna ta tsoma musu baki. Idan aiki suke yi tazo ta sa hannu suyi tare. Suhaif yasa ido sosai yana kula da yanayin zamansu, ya gane abinda ke faruwa. Bai wata-wata ba ya kira Naja'atu da Zubaida dakinsa ya ja musu kunne sosai yayi musu fada, yaci layar muddin basu canja halinsu ba, sunja Iman jikinsu tamkar *yar uwarsu, kawarsu to lallai su guji hukuncin da zai yanke a kansu. Ko tantama basu yi a zuciyarsu ba sunsan zai aikata abunda yace zaiyi musu in har suka kuskure gargadinsa. Suna daurewa suna jan Iman a jikinsu badan sun saba da ita ba, sai don dolen da Yaya Suhaif yayi musu. Ko da suka fara zama da Iman sai suka ji sun fara sonta har cikin zuciyarsu, saboda Iman mutum ce mai tsananin dadin zama. Mai hakuri, mai fara'a tasan me take fada, mai son aiki ga tsananin ladabi da biyayya bayan tsantsar ibada ta rike addininta.
Gason Reedwan da ta ke .....lolx =))
*yaudara* ni na ma mance ko wacece Matawata,,,, na daina sonta ga daidai dani Iman...............reed1
Ehem to gwauraye a huta anan sai kuma gobe da yardar Allah.
Reedwan Suraj Isma'il
INA KWANAN KU?
_____________________ YARENA ADDININA
CI GABAN LABARIN
Allah Ya albarkace su da *ya*ya mata har uku sai dai kash, da sun fara dan wayo sai su rasu, daga baya ne suka haifi Suhaif. Raliya tayi ta addu'a tayi kuka, tayi fargaba akan tana tsoron ko shima Suhaif mutuwa zaiyi kafin ya girma amma Allah mai komai mai kowa sai Ya raya musu shi har sai da ya shekara shida, sannan akayi masa kanwa mai suna Nadiya ana yaye Nadiya itama ta rasu. Bayan nan ta kara haifar *yan biyu suna rarrafe suka rasu. Hakika wannan rasuwar yara guda shida ba karamin tayar da hankalin Raliya da Hayatu yayi ba suka dukufa da yin addu'a suka rungumi dansu kwaya daya Suhaif, tamkar su hadiyeshi don kauna.
Alh. Hayatu su uku ne a wajen iyayensu akwai Furera itace Babba tana Garki tana aure. Sai Alh. Hayatu sannan kaninsa Usman. Allah ya yiwa Usman arziki don haka yana da katafaren gida a Kano a Unguwar *Yankaba da matarsa Usaina ana kiranta Usai ita *yar Gumel ce suna da *ya*ya uku. Babban dansu sunansa Najib, sai na biyun Sagir sai *yar autarsu Zubaida. Don haka Alh. Hayatu yayi shawarar gara ya dauki dansa kwaya daya jal ya kaishi Kano wajen kaninsa Usman ya hadasu da Najib dansa a saka si a makarantar boko me kyau yadda zaiyi ilimi sosai. Haka kuwa akayi tun daga Nursiry har suka shiga primary tare ajinsu daya Suhaif da Najib kuma daman kamarsu daya tunda iyayensu kamarsu daya kamar an tsaga kara suma kuma kowa da mahaifinsa yayi kama sai dai Suhayf ya dauko farar fatar Mahaifiyarsa da gwarzagwarzan idanuwanta. Suhaif yana firamare aka yi masa kanwa Naja'atu Raliya bata ma dora rai akan Naja'atu ba don taji a jikinta ba rayuwa zata yi ba ita ma. Amma babu wanda yasan gaibu sai Allah Ya raya Naja'atu har ta girma.
Naja'atu Hayatu da Zubaida Usman suma sa'anni ne duk da Naja'atu a garin su Doko tayi karatun firamare sai daga baya ta koma Kano aka hadata da Zubaida a makarantar Sakandire daya wato F.G.C Kano nan suka gama shima Suhaif da Najib F.G.C Azare suka gama suna fita daga sakandire suka wuce Bayero University Kano inda Suhaif ya karanci Enginearing, Najib kuma ya karanci Physic. Sun gama cikin wannan shekarar sakamakonsu ya fito, bautar kasa zasu wuce.
Raliya kuwa su biyu mahaifinsu suka haifa ita da kaninta Nasiru shima ya haifi *ya*yansa da yawa duk suna mutuwa sai Rabi ce kawai tayi saura wato *yar Hajja tana karama mahaifinta ya rasu Hajja ta dauketa shine yanzu take rike da ita.
Naja'at Hayat da Zubaida Usman sun shaku bayan *yan uwantaka ta jini ga kawance, don ko a makaranta ba sa rabuwa har *yan biyu ake kiransu daman kuma kamarsu daya suma sai dai Zubaida ita kuma ta danfi Naja'atu haske. Yanzu ma haka basu fi watanni biyu da kammala karatun sakandiren su ba shine kuma suka dungumo Doko suka zauna har suka shiga makarantar Islamiyya. Kullum da safe daga karfe tara zuwa sha biyun rana, ranar alhamis da juma'a ne kawai basa zuwa makaranta. Sai su zauna a gida suyi ta hira da mahaifiyarsu Raliya wacce suke kira da Goggo tamkar wasu kawayenta. Suyi labari suyi dariya su tafa haka suhaif ma yake zama da mahaifiyarsa yayi ta hira, wasa da dariya, sai dai son girmansa yayi yawa bai cika zama da kannensa Naja'at da Zubaida yayi hira dasu ba. Wani lokaci idan *yan fara'ar basa kusa ko kallansu yayi sai su hau makyarkyata suyi wuf su shige daki. Amma wasu lokutan yakan yi hira dasu, amma yana taka musu birki idan yaji hirar tasu ta fara shiga raini. Yafi yin wasa da *yar Hajja saboda dariya take bashi, bayan kauyancin daya addabi halinta gata rikon Kaka ce, saboda haka tabargazarta tayi yawa.
Fargabar Suhaif da Mahaifansa daya, ita ce a zaman Iman da su Naja'at sun san dole sai Iman ta fuskanci wariyar launin fata don sai sun hade mata kai su biyu sun wareta duk da sa'anni ne su duka ukun. Ba sau daya ba, ba biyu ba Naja'at da Zubaida sun sha yiwa kawayensu halin ko in kula baku damemu ba, kanmu kawai muka sani, bamu san ku ba. Duk kawar data rabesu sukan shareta har ta gaji ta kama gabanta kansu a hade yake su biyu basa son su sami ta uku. Haka kuwa aka yi suka ware Iman suna wani kaf-kaf da junansu ita kuma tana binsu, idan suna hirarsu tazo ta zauna ta tsoma musu baki. Idan aiki suke yi tazo ta sa hannu suyi tare. Suhaif yasa ido sosai yana kula da yanayin zamansu, ya gane abinda ke faruwa. Bai wata-wata ba ya kira Naja'atu da Zubaida dakinsa ya ja musu kunne sosai yayi musu fada, yaci layar muddin basu canja halinsu ba, sunja Iman jikinsu tamkar *yar uwarsu, kawarsu to lallai su guji hukuncin da zai yanke a kansu. Ko tantama basu yi a zuciyarsu ba sunsan zai aikata abunda yace zaiyi musu in har suka kuskure gargadinsa. Suna daurewa suna jan Iman a jikinsu badan sun saba da ita ba, sai don dolen da Yaya Suhaif yayi musu. Ko da suka fara zama da Iman sai suka ji sun fara sonta har cikin zuciyarsu, saboda Iman mutum ce mai tsananin dadin zama. Mai hakuri, mai fara'a tasan me take fada, mai son aiki ga tsananin ladabi da biyayya bayan tsantsar ibada ta rike addininta.
Gason Reedwan da ta ke .....lolx =))
*yaudara* ni na ma mance ko wacece Matawata,,,, na daina sonta ga daidai dani Iman...............reed1
Ehem to gwauraye a huta anan sai kuma gobe da yardar Allah.
Reedwan Suraj Isma'il
INA KWANAN KU?
_____________________ YARENA ADDININA
CI GABAN LABARIN