Sashe 62
Yarena Addinina Part Complete Hausa Novel · about 7 min read
Suhaif ya dauki katin ya bude amma tsabar rudewa, da daman kawai ba karantawa yake yi ba, bai san upside-down ya juya katin ba sai da Huzaifa ya kula ya karba ya gyara masa gami da cewa "Malam Suhaif yaya dai ciwon kanne yake damun ka, ka juya katin Upside-down kana karantawa? Suhaif yayi ajiyar zuciya har guda uku a jere ya kirkiro wani bushasshen murmushi ya ce "Kamar ka sani kaina ne yake ciwo. Najib wanda ya kurawa Suhaif ido yana masa nuni akan ya daure ya sake daurewa ya cije kada a gane shi.
Suhaif bai san Najib ya fadawa Iman halin da yake ciki ba, don baisan ta sani ba, haka su duka basu san Huzaifa yaji ba. Sai kowa yake dannewa yana nunawa babu komai a ransa. Kallo daya Suhaif ya yiwa katin yaga an rubuta Huzaifa Ahamed Jalingo weeds Fatima Lamin Jalingo sai yaga ganinsa ya raunana ya koma hatsa-hatsa tamkar yanar ido ce ta tsuro a idonsa yanzu-yanzu. Sai yayi sauri ya mikawa Iman kati ya ce "Ke amarya baki karanta ba. Iman ta karbi katin ta kasa budewa sai ta ajiye kan tebur ta rufe fuska. Huzaifa ya dubeta ya ce "Waike har yanzu kunyar fulanin ce bata sake ki ba? Kunsan da fa ana fara zancen auran take tashi tabar wajen. Wai nan dagewa tayi ta zauna a wajen da ake rabon katin bikinta. Najib da Suhaif suka yi dariya.
Ina tunanin sai jibine zan ci gaba idan Allah Ya kaimu
Reedwan Suraj Isma'il
>>>>>>>>>>>>>>> YARENA ADDININA
___CIGABAN LABARI
Huzaifa yayi gyaran murya ya ce "To Alhamdulillahi! Mun gode Allah, mun gode muku akan matukar kokarin da kuka yi wajen dawainiya da ni da bataliyata, ga Uwa Uba wahalar da zan baku ta gayyatarku da nayi zuwa wajen daurin aurenmu tun daga Abuja har Jalingo Allah Ya saka da alherinSa. Najib ya yi sauri ya katse shi ya ce "Haba mai gida meye abun wannan doguwar godiya? Mu da ku ai mun kulla zumunci har abada kuma duk kasar da kuke zamu kai muku ziyara balle daga nan zuwa Jalingo ai babu nisa. Suhaif ya yi gyaran murya ya ce "Iman *yar gidanmu ce, kanwarmu ce, tamkar jinin jikina take. Idan a bangon duniya za'ayi daurin aurenta zamu je. Kai kuma mai gidanta kun zama daya, mun zama daya da ku. Huzaifa yayi murmushi ya ce "To mun gode mun ji dadi muma zamu rike ku kamar yadda ku ka dauke mu *yan Uwa, jinin jikinku kuma dan Allah ku cika alkawari, kamar yadda ku kayi alkawari, nasan zaku cika alkawari ku zo daurin auren nan kada a samu matsala wani daga cikin ku yaki zuwa. Najib ya ce "Haba Huzaifa ai mu da Iyayenmu mata da maza da kannan mu duk zamu zo insha Allah. Huzaifa ya ce "Lallai kuwa zan zamo mai farin ciki. Yanzu zamu kama hanya zuwa Jalingo ina ga zai fi kyau mu tafi Yola ta jirgi. Nan ma zamu raba kati, sai mu wuce Jalingo. Iman ta ce "Ba da Bilkisu zamu tafi ba, ko ita ba yau ba? Huzaifa ya ce "Duk zancen nan da muke baki gane ba? Nafisa ta tafi Lagos tun karfe bakwai na zafe zata sayo ankon da za suyi kuma zata karbo dinkunanki, dukka lefen naki can takai a dinka miki. Tace sai wajen jibi zata je Jalingo shine ta bawa direbanta katinan daurin auren ya kawo min, ta bani lambarsa nayi masa kwatance, yanzu muka hadu a bakin titi ya bani, ta ce ko zamu fara rabawa kafin ta zo. Iman ta ce "Ai da ban gane ba, na dauka tana gidanta zan zamu je sai mu dunguma mu tafi. Huzaifa ya ce "Na rasa yadda zamuyi wannan tafiyar ina so in tsaya a Kano akwai abokaina da *yan Uwana da nake so in gayyata. Najib ya yi caraf ya ce "Muma Kanon zamu tafi dan *yan gida ba su san mun dawo jiya ba. Me zai hana mu dunguma a mota muje Kanon kayi rabon katinan, Iman ma ga kawayenta su Naja'at ta gayyacesu da bakinta. Ku kwana gobe da sassafe in saku a jirgin Yola ku isa Yola da wuri kuyi rabon a nutse sannan ku wuce Jalingo. Tun da yau bikin saura kwana shida babu lokacin da zaka je Yola ka dawo Kano kuma. Huzaifa ya ce "Gaskiya ne. Ya dubi Iman ya ce "Haka yayi miki? Ta gyada kai ta ce "Haka yayi Hamma Huzaifa. Suhaif dai yana zaune yana kallonsu tamkar ya rusa ihu dan tashin hankali. Ya rasa haushin wanda yake ji. Haushin Iman yake ji? Ko na Huzaifa? Ko kuwa haushin kansa da kansa yake ji oho?
Haka kuwa aka yi, mota daya direba da Huzaifa a gaba Iman da Zainab matarsa a baya. Daya motar direba da Najib a gaba, Suhaif da yaran Huzaifa a baya. Suka dunguma suka kama hanyar Kano. Tafiya suke a titi, tamkar a jirgin sama suke saboda dadin motar. Kujeru lausasa hade da sanyin A.C da kamshin turaren dake manne a kowacce kusurwar cikin motocin.
Huzaifa ya juyo ya dubi Iman cikin harshen fulatanci yace mata "Fatima bani labari, wanne labari Hamma Huzaifa? Labarin da kika taba bani can kwanaki na abubuwan da suka faru da rayuwarki bayan tafiyata. Kin fada min inda kika zami jariri da yadda ki kayi da jaririn. Kin tsaya a inda kikabi matar nan Masallacin B.U.K baki karasamin ba. Iman ta ce "Duk tsawon lokacin nan baka tambayeni ba sai yau? Huzaifa ya ce "Ai kin san komai kamawa yake yi, kinga yanzu da kin karasa mun labarin da nasan su Suhaif kafin ki gabatar mun dasu kamar yadda suka sanni kafi ki musu bayanina. Iman tayi murmushi ta ce "Haka ne amma kasan ban cika son yin hira da kai ba a gaban matarka ko? Babu dadi za taga kamar cin fuska ne kasan mata da kishi. Huzaifa ya ce "Ke kike ganin haka laifine ita tasan zan aureki yanzu haka ma katunan daurin auren duka suna wajenta saita hana mu hira? Bani labari bata jin fulatanci shima direba baya jin fulatanci.
Iman bata yiwa Huzaifa musu, duk abunda Huzaifa zaisata komai wahala zata yi masa balle labari ai ba zai zama matsala ba. Ta gyara zama ta fara rangadowa Huzaifa labarin duk abunda ya faru. Musamman da taga barci ya kwashe matarsa sai ta saki jiki tana ta zuba. Ta bashi labarin zamanta a gidan larabawa wato Mummy Naila, bata boye masa ba duk yadda suka yi da Matsafan akan Abdul-Malik dalilin da yasa ta bar Kano kenan ta nufi Doko garin su Suhaif. Tana hawaye tana fada masa halinda ta tsinci kanta da irin halaccin da Suhaif yayi mata. Amma har yanzu Huzaifa bai ji kalmar da yake son ji ba daga bakin Iman, bata kira kalmar so ba tsakaninta da Suhaif. Sai take kiran Suhaif da Yayanta.
Huzaifa ya tausayawa Iman matuka, kuma ya jinjinawa Suhaif da irin taimakon da yayi mata. Haka suka dinga hira har suka shiga Kano. Motar su Suhaif na gaban ta su Iman dan haka su suke bi a baya. Basu tsaya a ko ina ba sai a Hadeja Road unguwar Iyayen Najib. Suka shiga gidan suka iske Mama da Baba suna nan. Sai Baba ya dubi Suhaif da Najib ya ce "Wai yaran nan kun zama *yan Saudia ne, na ganku da larabawan mata har da *ya*yansu? Suka yi dariya dukkansu. Suhaif ya ce "Kwarai kuwa Baba muma mun zama *yan kasar Makka tunda gamu da *yan kasar mun taho muku dasu. Najib ya ce Baba wannan itace Iman *yar Jalingon nan da ta zauna a Doko. Sai Suhaif ya yi sauri ya ce "Ga kuma mijinta gobe zasu wuce Jalingo bikinsu. Kallo daya zaka yiwa Baba da Mama kasan sun shiga damuwa sabida tausayin Suhaif. Idan kasan Suhaif kasan shi da kaunar Iman. Huzaifa ya zaro kati ya mikawa Baba ya ce "Baba ya amsa da insha-Allah. Akayi-akayi a kawo musu abinci Najib ya ce a gidansa zasu ci abinci ya yiwa Naja'at waya ta hada musu abinci kala-kala.
Suhaif bai san Najib ya fadawa Iman halin da yake ciki ba, don baisan ta sani ba, haka su duka basu san Huzaifa yaji ba. Sai kowa yake dannewa yana nunawa babu komai a ransa. Kallo daya Suhaif ya yiwa katin yaga an rubuta Huzaifa Ahamed Jalingo weeds Fatima Lamin Jalingo sai yaga ganinsa ya raunana ya koma hatsa-hatsa tamkar yanar ido ce ta tsuro a idonsa yanzu-yanzu. Sai yayi sauri ya mikawa Iman kati ya ce "Ke amarya baki karanta ba. Iman ta karbi katin ta kasa budewa sai ta ajiye kan tebur ta rufe fuska. Huzaifa ya dubeta ya ce "Waike har yanzu kunyar fulanin ce bata sake ki ba? Kunsan da fa ana fara zancen auran take tashi tabar wajen. Wai nan dagewa tayi ta zauna a wajen da ake rabon katin bikinta. Najib da Suhaif suka yi dariya.
Ina tunanin sai jibine zan ci gaba idan Allah Ya kaimu
Reedwan Suraj Isma'il
>>>>>>>>>>>>>>> YARENA ADDININA
___CIGABAN LABARI
Huzaifa yayi gyaran murya ya ce "To Alhamdulillahi! Mun gode Allah, mun gode muku akan matukar kokarin da kuka yi wajen dawainiya da ni da bataliyata, ga Uwa Uba wahalar da zan baku ta gayyatarku da nayi zuwa wajen daurin aurenmu tun daga Abuja har Jalingo Allah Ya saka da alherinSa. Najib ya yi sauri ya katse shi ya ce "Haba mai gida meye abun wannan doguwar godiya? Mu da ku ai mun kulla zumunci har abada kuma duk kasar da kuke zamu kai muku ziyara balle daga nan zuwa Jalingo ai babu nisa. Suhaif ya yi gyaran murya ya ce "Iman *yar gidanmu ce, kanwarmu ce, tamkar jinin jikina take. Idan a bangon duniya za'ayi daurin aurenta zamu je. Kai kuma mai gidanta kun zama daya, mun zama daya da ku. Huzaifa yayi murmushi ya ce "To mun gode mun ji dadi muma zamu rike ku kamar yadda ku ka dauke mu *yan Uwa, jinin jikinku kuma dan Allah ku cika alkawari, kamar yadda ku kayi alkawari, nasan zaku cika alkawari ku zo daurin auren nan kada a samu matsala wani daga cikin ku yaki zuwa. Najib ya ce "Haba Huzaifa ai mu da Iyayenmu mata da maza da kannan mu duk zamu zo insha Allah. Huzaifa ya ce "Lallai kuwa zan zamo mai farin ciki. Yanzu zamu kama hanya zuwa Jalingo ina ga zai fi kyau mu tafi Yola ta jirgi. Nan ma zamu raba kati, sai mu wuce Jalingo. Iman ta ce "Ba da Bilkisu zamu tafi ba, ko ita ba yau ba? Huzaifa ya ce "Duk zancen nan da muke baki gane ba? Nafisa ta tafi Lagos tun karfe bakwai na zafe zata sayo ankon da za suyi kuma zata karbo dinkunanki, dukka lefen naki can takai a dinka miki. Tace sai wajen jibi zata je Jalingo shine ta bawa direbanta katinan daurin auren ya kawo min, ta bani lambarsa nayi masa kwatance, yanzu muka hadu a bakin titi ya bani, ta ce ko zamu fara rabawa kafin ta zo. Iman ta ce "Ai da ban gane ba, na dauka tana gidanta zan zamu je sai mu dunguma mu tafi. Huzaifa ya ce "Na rasa yadda zamuyi wannan tafiyar ina so in tsaya a Kano akwai abokaina da *yan Uwana da nake so in gayyata. Najib ya yi caraf ya ce "Muma Kanon zamu tafi dan *yan gida ba su san mun dawo jiya ba. Me zai hana mu dunguma a mota muje Kanon kayi rabon katinan, Iman ma ga kawayenta su Naja'at ta gayyacesu da bakinta. Ku kwana gobe da sassafe in saku a jirgin Yola ku isa Yola da wuri kuyi rabon a nutse sannan ku wuce Jalingo. Tun da yau bikin saura kwana shida babu lokacin da zaka je Yola ka dawo Kano kuma. Huzaifa ya ce "Gaskiya ne. Ya dubi Iman ya ce "Haka yayi miki? Ta gyada kai ta ce "Haka yayi Hamma Huzaifa. Suhaif dai yana zaune yana kallonsu tamkar ya rusa ihu dan tashin hankali. Ya rasa haushin wanda yake ji. Haushin Iman yake ji? Ko na Huzaifa? Ko kuwa haushin kansa da kansa yake ji oho?
Haka kuwa aka yi, mota daya direba da Huzaifa a gaba Iman da Zainab matarsa a baya. Daya motar direba da Najib a gaba, Suhaif da yaran Huzaifa a baya. Suka dunguma suka kama hanyar Kano. Tafiya suke a titi, tamkar a jirgin sama suke saboda dadin motar. Kujeru lausasa hade da sanyin A.C da kamshin turaren dake manne a kowacce kusurwar cikin motocin.
Huzaifa ya juyo ya dubi Iman cikin harshen fulatanci yace mata "Fatima bani labari, wanne labari Hamma Huzaifa? Labarin da kika taba bani can kwanaki na abubuwan da suka faru da rayuwarki bayan tafiyata. Kin fada min inda kika zami jariri da yadda ki kayi da jaririn. Kin tsaya a inda kikabi matar nan Masallacin B.U.K baki karasamin ba. Iman ta ce "Duk tsawon lokacin nan baka tambayeni ba sai yau? Huzaifa ya ce "Ai kin san komai kamawa yake yi, kinga yanzu da kin karasa mun labarin da nasan su Suhaif kafin ki gabatar mun dasu kamar yadda suka sanni kafi ki musu bayanina. Iman tayi murmushi ta ce "Haka ne amma kasan ban cika son yin hira da kai ba a gaban matarka ko? Babu dadi za taga kamar cin fuska ne kasan mata da kishi. Huzaifa ya ce "Ke kike ganin haka laifine ita tasan zan aureki yanzu haka ma katunan daurin auren duka suna wajenta saita hana mu hira? Bani labari bata jin fulatanci shima direba baya jin fulatanci.
Iman bata yiwa Huzaifa musu, duk abunda Huzaifa zaisata komai wahala zata yi masa balle labari ai ba zai zama matsala ba. Ta gyara zama ta fara rangadowa Huzaifa labarin duk abunda ya faru. Musamman da taga barci ya kwashe matarsa sai ta saki jiki tana ta zuba. Ta bashi labarin zamanta a gidan larabawa wato Mummy Naila, bata boye masa ba duk yadda suka yi da Matsafan akan Abdul-Malik dalilin da yasa ta bar Kano kenan ta nufi Doko garin su Suhaif. Tana hawaye tana fada masa halinda ta tsinci kanta da irin halaccin da Suhaif yayi mata. Amma har yanzu Huzaifa bai ji kalmar da yake son ji ba daga bakin Iman, bata kira kalmar so ba tsakaninta da Suhaif. Sai take kiran Suhaif da Yayanta.
Huzaifa ya tausayawa Iman matuka, kuma ya jinjinawa Suhaif da irin taimakon da yayi mata. Haka suka dinga hira har suka shiga Kano. Motar su Suhaif na gaban ta su Iman dan haka su suke bi a baya. Basu tsaya a ko ina ba sai a Hadeja Road unguwar Iyayen Najib. Suka shiga gidan suka iske Mama da Baba suna nan. Sai Baba ya dubi Suhaif da Najib ya ce "Wai yaran nan kun zama *yan Saudia ne, na ganku da larabawan mata har da *ya*yansu? Suka yi dariya dukkansu. Suhaif ya ce "Kwarai kuwa Baba muma mun zama *yan kasar Makka tunda gamu da *yan kasar mun taho muku dasu. Najib ya ce Baba wannan itace Iman *yar Jalingon nan da ta zauna a Doko. Sai Suhaif ya yi sauri ya ce "Ga kuma mijinta gobe zasu wuce Jalingo bikinsu. Kallo daya zaka yiwa Baba da Mama kasan sun shiga damuwa sabida tausayin Suhaif. Idan kasan Suhaif kasan shi da kaunar Iman. Huzaifa ya zaro kati ya mikawa Baba ya ce "Baba ya amsa da insha-Allah. Akayi-akayi a kawo musu abinci Najib ya ce a gidansa zasu ci abinci ya yiwa Naja'at waya ta hada musu abinci kala-kala.