Sashe 70
Yar Dangi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A babban masallacin santan brllow dake anguwar sarki. bayan an kammala sallar jumma'arh aka daura auren AB'ILAL da hilwah a kan sadaki nera dubu dari uku. 1m alhaji babba yaso bayarwa a matsayin sadakin auren, abokinsa yace masa ai ba sadaki me yawa ba, albarkar auren ake nema. Zucial fal farin cikin da alhaji babba besan dalilinsa ba ya dawo gidan, yasa zee ta kirawo masa hajiya maryam, taje ta sameta ta idar da sallar azahar kenan tana lazimi a side din hajiya babba ta sanar da ita saqon Alhaji dmn kmr tana jira, a tare suka shigo side din ita da zee, direct zee ta nufa bedroom din Alhaji babbah tin kafin a kara korinta. hajiya Maryam ta karasa ta zauna kujerar data tashi dazu. Alhaji se jifanta yakeyi da murmushi ya zaro kudade daga aljihunsa 300k yan dubu dubu ya mikawa hajiya maryam ta amsa tana Murmushi yace "ga sadakin nan an daura..."seda amihh ta daga hannayenta duka biyu sama tama ALLAH godiya kana ta amshi kudin daga hannun alhaji babbah zucia fal farin ciki se ynzu ne takejin natsuwa na ratsa ta. "Alhmdllh an daura Aure kmr yadda kk bukata ALLAH yasa alheri..." Cewar alhaji babbah. hajiya maryam ta amsa da Ameen,yayinda bakinta ke kmr gonar audiga, washe haqora takeyi. "Na gode Alhaji ALLAH ya kara girma..." Hajiya maryam tayi mgnr cikin annashuwa dajin dadih. Alhaji babba ya amsa da "Ameen...ynzu yaushe za a kawo mna Amaryar?'' Hajiya maryamn tayi yar dariya tace "insha ALLAH alhaji za a kawota tazo ta gadaiku..." Alhaji babba yace "to madallah...wlhy hajiya kar kiso ki tona zuciarta, nayi farin ciki da nga wannan rnr da hannu na daurawa yaronnan aure Alhmdllh..." Hajiya maryam ta jinjina kai hadi da cewa "Allah shine abin godia Alhaji...Alhamdulillahi!" Ta karashe mgnr da hamdalah. Dukkaninsu farin ciki ya rufesu, alhaji se kiran waya yakeyi yna sanar da abokanayensa wadanda basu samu halartar daurin aurenba, cewa dansa yayi aure yau, wadanda sukayi sallah a masallaci daya kam duk sun samu halartar Auren....zucia fal jin ddh Hajiya maryam tama alhaji sallahma ta bar Falon ko sallahma bata tsaya yima sauran matan gidanba, taja motarta tabar gidan, a hanya ta tsaya ga almajirai seda tayi sadakar naira dubu dari biyar da hamsin din dake bag dinta duka, ta dawo gida da 300k din sadakin hilwah. Packing tayi a packing space ta fito zucia fal farin ciki se murmushi takeyi ita kadai bata taba tsintar knta a farin ciki makamancin wannan da take ciki ba, kai kace bushara aka mata da aljannarh. Falon ta shigo bakinta dauke da sallahma, hilwah da amal na zaune a falon suna kallon TV tinda suka tashi basu ganta ba salwah tasha ko taje asibiti ne, hilwah se aikin tambayarta takeyi ina Amihh nan ta sanar da ita taje asibiti, se Allah Allah kawai hilwah keyi Amihh ta dawo, yayinda tinda ta tashi a baccin zuciarta da kirjinta keta dum dum dum din da batasan dalilinsana."sannu da zuwa Amihh.." Cewar salwah ta taso ta amshi bag din dake hannunta. Hilwah ta zubo mata ido. Ta karasa kan kujerar da hilwah din ke zaune ta zauna gefenta, hilwah tayi kasa da kanta. "Sannu da zuwa Amihh.." Amsawa Amihh tayi cikin tsananin jin ddh hadi da farin ciki, ta shiga kare mata kallo sanye take da doguwar riga mara nauyi wadda ta amshi kirar jikinta, ita knta Amihh tana yabawa da yanayin halittar jikin hilwah, sbda Akwai komi da komi yaji. Salwah ta nufa hanyar bedroom din Amihh domin ta ajiye mata bag dinta a can, Amihh tace ta kawo mata nan, ba bata lokaci salwah ta juyo ta bawa Amihh bag din, ta zauna kan kujerar 2ct wadda ke facing Dinsu, ta zubawa Amihh ido se barin murmushi takeyi kmr gonar audiga tin shigowarta falon salwah ta kula da hakan. Zuge bag dinta tayi ta ciro wadannan kudin 300k ta mikawa hilwah wadda kanta ke kasa ganin kudin da Amihh ke mika mata yasata dago kwayar idonta ta zubawa Amihh tana me neman karin bayani a kan kudin. "Amsa mana.." Cewar Amihh. Ba musu hilwah ta kawo hannu biyu ta amshi kudin cikin ladabi, still kwayar idonta na kn Amihh tana me neman karin bayani a kan kudin. Amihh ta gyara zamanta kana ta fara mgna cikin muryarta me cike da zallar farin ciki "Wadannan kudin da kika riqe a hannunki sadakin ki ne..." Ba hilwah ba hatta da salwah seda sukaji saukar mgnr kmr saukar aradu, nan da nan xuciar hilwah ta hau luguden tashin hnkli. Salwah kam tini ta zaro idanuwa waje, tana me adduarh ALLAH yasa bada AB'ILAL aka daura aurenba. "Sadaki?'' Hilwah Ta maimaita cikin kid'imewa ita sam mafa bata fahimci me Amihh take shirin fada mata ba. Daga mata kai Amihh tayi alamar tabbatarwa kana ta ci gaba da mgna "eh sasakin ki na aure keda d'ana na cikina..." A wannan karon Salwah tafi hilwah shiga tsananin damuwa hadi da tashin hnkali a zahirin gaskia bataso aka ce hilwah ta Auri AB'ILAL ba sbda mugun halinsa ita kuma hilwah bata da mugun hali, ga sanyin rai, ta yaya zata iya zama da AB'ILAL? Salwah ta tambayi kanta, hadi da rafka uban tagumi ta zubowa hajiyar ido, ita bata taba ganin inda akayi haka ba, kawai ka daurawa mutum aure ba tare da abincewarsa ba... A bad'ini salwah tana wa AB'ILAL sha'awar auren hilwah amma bata fatan hkn sbda wuyar kansa, kuma tasan Allah kadai yasan irin izayar daze ta ma hilwah Din in aka barsu a gida daya, AB'ILAL babu sauki a lamarinsa, dan uwanta ne ta sanshi kar!. "Why Amihh?'' Salwah ta fadi kasa kasa ta yadda amihh baza ta iya jiyowa ba, ji takeyi kmr ta fashe da kuka, da ace mafarki takeyi da in ta tashi bazata koma baccin ba wlhy. A bangaren Hilwah kam sbda tsabar firgici da tsantsar tashin hnkli suka ziyarceta, bata san sadda kudin dake hannunta ba suka zube kasa, gani takeyi kmr a mafarki take ba gaskia bane . Hajiya maryam ta zubawa kudaden da suka zube kasa ido, tana kokarin sunkuyawa ta dauki kudin hilwah ta rigata yin saurin sunkuyawa ta dauki kudin zucia fal tashin hnkali, hadi da tsantsar firgici. Amsar kudin hajiya maryam tayi daga hannun hilwah din, ta dawo da kudaden jikinta, hilwah tayi kasa da knta. "Ba ki son jinina ne ko hilwah? A zahirin gaskia ban miki adalci ba sbda ban tambayeki ko kinada wanda kikeso ba na yanke danyen hukunci amma ina me neman afuwarki tinda baki son jinina zan raba Auren kinji karki damu...nasha ko na isa dake ne shiyasa. ..." Tana gama fadar hkn ta mike ta bar falon da kudaden a hannunta ta nufa bedroom dinta zucia bb ddh, a yanayin reaction din hilwah tasan babu farin ciki dukda dmn batayi tsammanin ganin farin cikin ba a kn fuskarta. Hilwah ta gaza bude baki tayi mgna dukda kuwa tanason yin mgnr jikinta yy sanyi zuciarta tayi weak gabobin jikinta suka zama kmr ba nata ba, jinta takeyi tmkr ba ita ba, tabbas a duniarnan bata tunanin da abinda amihh zata nema a gareta da bazata iya mata shi ba, tamkar uwarda ta haifeta take jinta a rnta. "Zaki iya bijircewa uwarda ta haifeki?'' Zuciarta ta jefo mata wannan tambayar, shiru tayi kawai zuciata bb ddh, tabbas komi amihh zata mata zata amsheshi hannu biyu biyu koda kuwa bata son abun. "Ya rabbih!'' Ta fadi a bayyabe, zucia babu dadih, sam bata shiryawa wannan kaddarar tataba... Salwah ta taso ta dawo kan kujerar da hilwah take zaune ta jawota jikinta zucia fal tausanta, a ranta batasan meyasa amihh zata yanke wannan d'any'en hukun ba ba tare da amincewar mutum biyu ba, harga ALLAH salwah bataji dadin wannan hadin ba, sam be mata ba, AB'ILAL nada mugun hali na karshe be dauki mace a bakin komi ba, kada yaje yayi ta dukan hilwah, sune tunani tunanin daketa yawo a zuciar salwah. Jawo hilwah jikinta tayi ta rungumeta sosai ga jikinta hilwah tayi shiru tana nazarin rayuwarta tin daga fari har zuwa ynzu, ita de tanada kaddarori dayawa. "Kiyi hkri plx da hukuncin da Amihh ta yanke, in baki sonshi ki ce baki sonshi ma kawai plx, karma ki ce kina snshi tinda ma baki snshi ba...nasan in kkce baki so Amihh zata raba Auren, dan Allah kice mata baki sonshi ma kawai plx!" Cewar salwah hilwah tayi shiru ta lumshe idanuwanta tana me nazarin kalaman salwah. "Meyasa zaki ce in ce bana sonshi?'' Hilwah ta tambayi salwah da sanyin muryarta wadda ta koma kmr ta marasa lafia. Salwah ta sauke ajiyar zucia kana tace "bkm, but plx karki yadda knji dan ALLAH..." Ta karashe mgnr kmr a firgice. Hilwah tayi shiru na wasu yan dakiku, nan ta shiga girgiza ma salwah kai ta ce "Bazan iya ba har abadan..." Tayi mgnr hadi da mikewa tsaye, tana girgiza kai, nan take taji jiri na neman dibarta daba dan tabada dakiya ba dase ta fadi kasa, karasawa tayi ta jingina da bangon falon, Salwah ta zubo mata ido, nan take ta hango tsantsar damuwa a kan fuskar hilwah din. Murya a sanyaye hilwah ta fara mgna "Bazan iya bijirewa Amihh ba wlhy sis..." Salwah ta bita da ido ita knta tana tsananin cikin dmwa Ita abun uku hudu ya taru ya hadar mata, harga Allah batason wannan hadin AB'ILAL da hilwah sun dace a sura amma basu dace ba a hali. Ta bude baki da niyar zatayi mgna hilwah ta fara takawa a hnkli ta nufa hnyar bedroom din Amihh . salwah ta bita da ido harta shige dakin, ta tashi ta bita cikin sauri.... Zaune take a gefen bed dinta ta rafka uban tagumi nan da nan taji guiwarta tayi sanyi, sbda batason abinda zata takurawa hilwah, dade ace AB'ILAL ne tasan dolensa ma ya amince ko bayaso. Hilwah ce ta shigo dakin dagowa tayi ta zuba mata ido, Salwah ta shigo bayanta. Dai-dai kasan kafafuwanta hilwah ta zube taba fadin ''na Amince amihh... bazan iya bijirewa umarninki ba, har abadan..." Tana gama fadar hkn ta fashe da kuka, salwah dake tsaye itama idanuwanta suka cicciko da kwallar tausan Hilwah, ita fa batason hadinnan harga ALLAH. Amihh ta zuba mata ido kukan nata yana taba mata