Sashe 7
Uwani Yar Kashin Gwuiwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baki sake Dada take kallonsa, ta rafka salati haɗe da faɗin, "Maza kwashe mini lalatattun kayan nan kafin ranka ya ɓaci. Ni Kulu uban me zan saka a ciki? An ya Isuhu shaɗanu ba su dafa maka kai a cikin bacci ba?" Uwani da ke uwar ɗaki ta sunne kai ƙasa tana dariya.
"Haba Dada da farar safiya ki cika wa mutane kunne da ihu." Jafar ya faɗa yana sako kansa cikin ɗakin. Uwani da ke ɓoye a ɗaki ta yi ƙasa da murya ta ce, "Kai ma naka ihun yana tafe."
"Ba dole ka ji ihuna ba Jafaru yanzu kamar ni tsofai-tsofai." Sai kuka ya ci ƙarfin Dada sai da ta share hawaye sannan ta watsa wa Jafar rigunan a fuska ta ci gaba.
"Wai Isuhu ya rasa me zai kawo mini sai baraziya wai na saka. Yanzu saboda Allah Jafaru ko uwarka Saratu me za ta yi da baraziyya ballantana kuma ni?" Tun Dada ba ta gama magana ba Jafar ya watsar da rigunan sakamakon wani tsami da bashi-bashi da ya ji ya doko hancinsa.
"Haba Dada me kike yi haka ne?" Jafar ya faɗa a ƙazance.
Kafin Dada ta yi magana mai sunan Malam ya sake tsanyarewa da kuka, Lami ta dubi Jafar ta miƙa masa shi. Kamar Jafar zai yi magana sai kuma ya basar ya miƙa hannu ya karɓe shi, yana bin su da kallon mamaki.
"Don Allah Jafaru ka taimaki yaron nan ka ba shi mama ya sha ko ya yi shiru." Lami ta faÉ—a a É—an kunyace. Jafar ya kalli Lami cikin sauri ya ce.
"Wane Jafarun?" Jafar ya tambaya a hargitse.
"Kai mana Jafaru, don Allah ka yi ka ba shi kada ya shiɗe don tun ɗazu yake kuka." Baba Isuhu ya furta. Ran Jafar ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, ya haɗe fuska ya dubi baba Isuhu.
"Baba wannan wacce irin magana ce babu tsari, yanzu idan na faɗa maka magana a ce na yi rashin kunya. Idan har ni zan iya shayar da shi me ya hana kai ba ka shayar da shi ba?" Dada ta saki baki da hanci tana kallon baba Isuhu a tsorace, don ita a yanzu ya fara ba ta tsoro shi da Lami. A hankali ya ajiye mai sunan malam a gefe sannan ya miƙe, yana shirin tafiya Lami ta ce.
"Isuhu sai fa mun danne shi..."
Tun Lami ba ta ƙarasa magana ba baba Isuhu ya sa ƙafa ya shatalo ƙafar Jafar sai ga Jafar a ƙasa. Dada na ganin haka ta fara tafiya da rarrafe don ta tabbata yau su Isuhu babu lafiya, shi ya sa ta nemi guduwa kafin ita ma su dawo kanta su danne ta su saka mata rigar mama.
Jafar ya yi mamakin yadda ya gagara ƙwace kansa a hannun baba Isuhu, don haka jin baba Isuhu ya fara ɗaga masa riga sama ya fara kiciniyar kare kansa, garin yunƙurin danne rigarsa sai ga Jafar yana sakin tusa. Uwani kuwa me za ta yi ba dariya ba har hawaye saboda mugunta.
Ganin haka ba zai kai Jafar ba ya sa ya fara ihu.
"Wayyo Dada ki kawo mini ɗauki. Wayyo Allah! Mutanen gidan nan ku kawo min ɗauki su Lami za su haike mini." Uwani na daga ɗaki ban da dariya babu abin da take sheƙawa, saboda tsabar dariya har kwanciya ta yi ƙasa.
Suna cikin haka sai jin muryar Goggo Sala suka yi a bakin ƙofa ta fara lashe baki tana faɗin, "Allah na gode maka da har yanzu lokaci bai ƙure mini ba." A zabure baba Isuhu ya ɗaga Jafar, take jikinsa ya fara karkarwa ta fara tunkaro shi yana ja da baya.
"Wayyo Allah Dada ki zo Goggo Sala za ta sa a cinye ni." A madadin Jafar ya gudu tun da ya samu ya tsira sai ya bi baba Isuhu da kallo, saboda ba ƙaramin mamaki ya ba shi ba. Dada da ke cikin ɗaki ta kai wa Uwani duka tana ce wa.
"Dariyar me kike yi Uwani mu da ya kamata mu fara yunƙurin ƙwatar kanmu." Kafin Uwani ta yi magana suka ji baba Isuhu ya zuba ihu. "Wayyo ta shanye mini ƙafafu, Jafaru, Dada ku zo ku kawo mini ɗauki." Goggo Sala ba ta bi ta kan baba Isuhu ba ta shatalo ƙafafuwansa za ta sunkuta shi a baya sai ga baba Mustafa da baba Idris sun shigo.
"Subhanallahi kai Isuhu lafiya kuwa?" Suka ƙarasa maganar suna ƙarasawa wurin Goggo Sala, baba Isuhu da yake ya gama tsorata sai ji suka yi sharaf ya faɗo jikinsu da alama ya suma. Suka kama shi suka kwantar a ƙasa sai kawai Goggo Sala ta fashe da kuka.
"Yanzu shi kenan rayuwata ta zo ƙarshe."
Da mamaki suke bin ta da kallo, Baba Mustafa ya dubi Jafar da ya yi laƙwas a gefe ya ce.
"Kai Jafar wane sakarci ne haka ake yi kai kuma kana zaune?" Jafar ya sauke ajiyar zuciya ya ce. "Baba ni ma ta kaina nake da tuni sun haike mini, dube ni wai fa ni zan shayar da mai sunan Malam."
"Gara da Allah Ya kawo ku Idirisa, wallahi Isuhu shi da matarsa sun haukace. Ashe ba su kaɗai ba har da Salamatu ita ma, an ya ba gamo suka yi a cikin gidan ba. Ban da haka wai ni Isuhu zai kawowa rigar mama ya ce na saka, sannan su dubi garjejen ƙato kamar Jafaru su ce ya shayar da me sunan malam." Baba Mustafa ya yi farat ya ce.
"Shi Jafarun ne zai shayar da jariri?"
Dada ta wara hannuwa ta furta.
"Ta ya ni ji dai Muɗɗafa, ka ga dai a kan idona aka haifi Jafaru. Kai ƙarshe ma dai ni na yi jinyar shayin da aka yi masa ballantana na ce ko Jafaru ya koma mata-maza, Jafaru ko ka sauya daga baya zuwa mata-maza ne ban sani ba."
A ƙufule Jafar ya ce, "Wallahi Dada kar ki ƙara ce mini mata-maza."
Kukan da mai sunan malam yake tsanyarawa ne ya sa baba Idris ya yi wa Lami magana, sai da ta share ƙwallar idonta ta ce.
"An ce daga jiya kada na ƙara shayar da shi." A daidai lokacin baba Isuhu ya farfaɗo sakamakon ruwan da aka yayyafa masa.
"Waye ya hana ki shayar da shi?" Shiru gabaɗaya suka yi, baba Isuhu ya dubi Lami ita kuma ta kalli Goggo Sala sai kawai suka fashe da kuka lokaci ɗaya. Shiru ɗakin ya yi kowa yana bin su da kallon mamaki, ban da Uwani da ke sakin murmushi a fakaice. Sai da suka yi me isar su sannan aka samu da ƙyar Goggo Sala ta ce.
"Ni kam na san wannan jawabin da zan yi ƙila shi ne na ƙarshe a rayuwata don na san kashe ni za su yi." Baba Isuhu ya yi tsammanin bayanin 'yan ƙungiyar asirin da take ciki za ta faɗa, don haka ya zuba mata ido sai ya ji ta ce.
"Dama dai uwar garke ba..."
Kamar haÉ—in ba ki Lami da Isuhu suka ta fi da gudu suka toshe mata baki, da mamaki mutanen É—akin suka bi su da kallo.
"Ƙarya take yi makira haɗa ni da 'yan uwana za ta yi." Baba Isuhu ya faɗa yana haki kamar wanda ya ci gasar tseren gudu.
"Ba ma son shashancin banza da wofi Isuhu, sakar mata baki kada ranka ya yi mummunan ɓaci." Baba Mustafa ya faɗa a fusace. Babu yadda suka iya haka suka koma suka zauna jiki a sanyaye, baba Isuhu ya sunkuyar da kai ƙasa gabansa na faɗuwa. Goggo sala ta fara wassafo jawabi tiryen-tiryen tana hawaye. Tana gama jawabi gabaɗaya ɗakin suka ɗauki salati.
"Kaico rayuwa ni Kulu me na haɗa da sata da Isuhu zai janyo mini mugun hali cikin zuri'ata." Dada ta furta tana zubar da ƙwallah. Malam na Madina da ke gefe ya ce. "An ya Isuhu yanzu rayuwar da ka ɗauko mana kenan? Wallahi ka yi gaggawar yin istigifari kuma ka nemi masu kaya ka mayar musu da abin su. Idan ba haka ba muna cikin Firdausi kana Hawiya, atoh faɗar Allah ce ba ya yafe haƙƙin wani a kan wani." Shiru ɗakin ya yi kunyar duniya ta mamaye baba Isuhu shi da su Lami. Baba Idiris da baba Mustafa suka rufe shi da faɗa sosai, don haka ya nuna nadamarsa a fili. Sannan baba Mustafa ya juyo wurin Dada.
"Dada ki gafarce ni a game da abin da zan faɗa amma tun farko ke ce kika ɓata Isuhu, saboda Isuhu yana ɗan autanki kika ɗauki son duniya kika ɗora masa. Hatta makaranta da Baba Sa'idu ya saka shi daina zuwa ya yi kuma kika goya masa baya, duk cikinmu shi kaɗai ne bai samu karatun arabi da boko mai zurfi ba. Ga shi nan sana'o'in ma wacce ce ba a nuna masa ba amma kullin a tsalle-tsalle yake ba shi da aiki sai kame-kame, tun wuri ka yi wa kanka faɗa domin kullin girma kake ƙara yi." Dada ta sharce ƙwallar da ke fuskarta ta ce.
"Yanzu dama MuÉ—É—afa ka na da tarin nasihohin nan tutuni ba ka yi mini ba? Ni dai wannan maganar a rufe ta a nan kada Sa'idu ya ji don wallahi sai ya kusa cinye ni É—anya."
GabaÉ—aya suka amsa mata.
"Dama wannan abin kunyar ai ba za mu bari ya fita ba Dada, yanzu dai a tambayi Uwani tun da haƙƙinta ne ta yafe masa?"
Uwani da ke gefe ta saki murmushin ƙeta ta yi saurin cewa, "Ni dai Baba na riga da na yafe musu baba Isuhu ai tamkar mahaifina na ɗauke shi." Da sauri Jafar ya dube ta don haka kawai ya ji bai yarda da kalaman Uwani ba.
"Allah Ya yi miki albarka Uwani, dama ɗa ba sai wanda ka haifa ba kaico rayuwa Allah Ya gafarta wa Yaya Umaru." Baba Isuhu ya faɗa yana sharce ƙwallah.
Uwani ta saki murmushin ƙeta a ranta ta ce, "Za ka ga ɗa ba sai ka haifa ba." Baba Idris ya yi musu nasiha sannan ya ce shi da kansa a ranar zai kira su Aramma na gangare su yi saukar Alƙur'ani a gidan gabaɗaya.
"Haba Dada da farar safiya ki cika wa mutane kunne da ihu." Jafar ya faɗa yana sako kansa cikin ɗakin. Uwani da ke ɓoye a ɗaki ta yi ƙasa da murya ta ce, "Kai ma naka ihun yana tafe."
"Ba dole ka ji ihuna ba Jafaru yanzu kamar ni tsofai-tsofai." Sai kuka ya ci ƙarfin Dada sai da ta share hawaye sannan ta watsa wa Jafar rigunan a fuska ta ci gaba.
"Wai Isuhu ya rasa me zai kawo mini sai baraziya wai na saka. Yanzu saboda Allah Jafaru ko uwarka Saratu me za ta yi da baraziyya ballantana kuma ni?" Tun Dada ba ta gama magana ba Jafar ya watsar da rigunan sakamakon wani tsami da bashi-bashi da ya ji ya doko hancinsa.
"Haba Dada me kike yi haka ne?" Jafar ya faɗa a ƙazance.
Kafin Dada ta yi magana mai sunan Malam ya sake tsanyarewa da kuka, Lami ta dubi Jafar ta miƙa masa shi. Kamar Jafar zai yi magana sai kuma ya basar ya miƙa hannu ya karɓe shi, yana bin su da kallon mamaki.
"Don Allah Jafaru ka taimaki yaron nan ka ba shi mama ya sha ko ya yi shiru." Lami ta faÉ—a a É—an kunyace. Jafar ya kalli Lami cikin sauri ya ce.
"Wane Jafarun?" Jafar ya tambaya a hargitse.
"Kai mana Jafaru, don Allah ka yi ka ba shi kada ya shiɗe don tun ɗazu yake kuka." Baba Isuhu ya furta. Ran Jafar ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, ya haɗe fuska ya dubi baba Isuhu.
"Baba wannan wacce irin magana ce babu tsari, yanzu idan na faɗa maka magana a ce na yi rashin kunya. Idan har ni zan iya shayar da shi me ya hana kai ba ka shayar da shi ba?" Dada ta saki baki da hanci tana kallon baba Isuhu a tsorace, don ita a yanzu ya fara ba ta tsoro shi da Lami. A hankali ya ajiye mai sunan malam a gefe sannan ya miƙe, yana shirin tafiya Lami ta ce.
"Isuhu sai fa mun danne shi..."
Tun Lami ba ta ƙarasa magana ba baba Isuhu ya sa ƙafa ya shatalo ƙafar Jafar sai ga Jafar a ƙasa. Dada na ganin haka ta fara tafiya da rarrafe don ta tabbata yau su Isuhu babu lafiya, shi ya sa ta nemi guduwa kafin ita ma su dawo kanta su danne ta su saka mata rigar mama.
Jafar ya yi mamakin yadda ya gagara ƙwace kansa a hannun baba Isuhu, don haka jin baba Isuhu ya fara ɗaga masa riga sama ya fara kiciniyar kare kansa, garin yunƙurin danne rigarsa sai ga Jafar yana sakin tusa. Uwani kuwa me za ta yi ba dariya ba har hawaye saboda mugunta.
Ganin haka ba zai kai Jafar ba ya sa ya fara ihu.
"Wayyo Dada ki kawo mini ɗauki. Wayyo Allah! Mutanen gidan nan ku kawo min ɗauki su Lami za su haike mini." Uwani na daga ɗaki ban da dariya babu abin da take sheƙawa, saboda tsabar dariya har kwanciya ta yi ƙasa.
Suna cikin haka sai jin muryar Goggo Sala suka yi a bakin ƙofa ta fara lashe baki tana faɗin, "Allah na gode maka da har yanzu lokaci bai ƙure mini ba." A zabure baba Isuhu ya ɗaga Jafar, take jikinsa ya fara karkarwa ta fara tunkaro shi yana ja da baya.
"Wayyo Allah Dada ki zo Goggo Sala za ta sa a cinye ni." A madadin Jafar ya gudu tun da ya samu ya tsira sai ya bi baba Isuhu da kallo, saboda ba ƙaramin mamaki ya ba shi ba. Dada da ke cikin ɗaki ta kai wa Uwani duka tana ce wa.
"Dariyar me kike yi Uwani mu da ya kamata mu fara yunƙurin ƙwatar kanmu." Kafin Uwani ta yi magana suka ji baba Isuhu ya zuba ihu. "Wayyo ta shanye mini ƙafafu, Jafaru, Dada ku zo ku kawo mini ɗauki." Goggo Sala ba ta bi ta kan baba Isuhu ba ta shatalo ƙafafuwansa za ta sunkuta shi a baya sai ga baba Mustafa da baba Idris sun shigo.
"Subhanallahi kai Isuhu lafiya kuwa?" Suka ƙarasa maganar suna ƙarasawa wurin Goggo Sala, baba Isuhu da yake ya gama tsorata sai ji suka yi sharaf ya faɗo jikinsu da alama ya suma. Suka kama shi suka kwantar a ƙasa sai kawai Goggo Sala ta fashe da kuka.
"Yanzu shi kenan rayuwata ta zo ƙarshe."
Da mamaki suke bin ta da kallo, Baba Mustafa ya dubi Jafar da ya yi laƙwas a gefe ya ce.
"Kai Jafar wane sakarci ne haka ake yi kai kuma kana zaune?" Jafar ya sauke ajiyar zuciya ya ce. "Baba ni ma ta kaina nake da tuni sun haike mini, dube ni wai fa ni zan shayar da mai sunan Malam."
"Gara da Allah Ya kawo ku Idirisa, wallahi Isuhu shi da matarsa sun haukace. Ashe ba su kaɗai ba har da Salamatu ita ma, an ya ba gamo suka yi a cikin gidan ba. Ban da haka wai ni Isuhu zai kawowa rigar mama ya ce na saka, sannan su dubi garjejen ƙato kamar Jafaru su ce ya shayar da me sunan malam." Baba Mustafa ya yi farat ya ce.
"Shi Jafarun ne zai shayar da jariri?"
Dada ta wara hannuwa ta furta.
"Ta ya ni ji dai Muɗɗafa, ka ga dai a kan idona aka haifi Jafaru. Kai ƙarshe ma dai ni na yi jinyar shayin da aka yi masa ballantana na ce ko Jafaru ya koma mata-maza, Jafaru ko ka sauya daga baya zuwa mata-maza ne ban sani ba."
A ƙufule Jafar ya ce, "Wallahi Dada kar ki ƙara ce mini mata-maza."
Kukan da mai sunan malam yake tsanyarawa ne ya sa baba Idris ya yi wa Lami magana, sai da ta share ƙwallar idonta ta ce.
"An ce daga jiya kada na ƙara shayar da shi." A daidai lokacin baba Isuhu ya farfaɗo sakamakon ruwan da aka yayyafa masa.
"Waye ya hana ki shayar da shi?" Shiru gabaɗaya suka yi, baba Isuhu ya dubi Lami ita kuma ta kalli Goggo Sala sai kawai suka fashe da kuka lokaci ɗaya. Shiru ɗakin ya yi kowa yana bin su da kallon mamaki, ban da Uwani da ke sakin murmushi a fakaice. Sai da suka yi me isar su sannan aka samu da ƙyar Goggo Sala ta ce.
"Ni kam na san wannan jawabin da zan yi ƙila shi ne na ƙarshe a rayuwata don na san kashe ni za su yi." Baba Isuhu ya yi tsammanin bayanin 'yan ƙungiyar asirin da take ciki za ta faɗa, don haka ya zuba mata ido sai ya ji ta ce.
"Dama dai uwar garke ba..."
Kamar haÉ—in ba ki Lami da Isuhu suka ta fi da gudu suka toshe mata baki, da mamaki mutanen É—akin suka bi su da kallo.
"Ƙarya take yi makira haɗa ni da 'yan uwana za ta yi." Baba Isuhu ya faɗa yana haki kamar wanda ya ci gasar tseren gudu.
"Ba ma son shashancin banza da wofi Isuhu, sakar mata baki kada ranka ya yi mummunan ɓaci." Baba Mustafa ya faɗa a fusace. Babu yadda suka iya haka suka koma suka zauna jiki a sanyaye, baba Isuhu ya sunkuyar da kai ƙasa gabansa na faɗuwa. Goggo sala ta fara wassafo jawabi tiryen-tiryen tana hawaye. Tana gama jawabi gabaɗaya ɗakin suka ɗauki salati.
"Kaico rayuwa ni Kulu me na haɗa da sata da Isuhu zai janyo mini mugun hali cikin zuri'ata." Dada ta furta tana zubar da ƙwallah. Malam na Madina da ke gefe ya ce. "An ya Isuhu yanzu rayuwar da ka ɗauko mana kenan? Wallahi ka yi gaggawar yin istigifari kuma ka nemi masu kaya ka mayar musu da abin su. Idan ba haka ba muna cikin Firdausi kana Hawiya, atoh faɗar Allah ce ba ya yafe haƙƙin wani a kan wani." Shiru ɗakin ya yi kunyar duniya ta mamaye baba Isuhu shi da su Lami. Baba Idiris da baba Mustafa suka rufe shi da faɗa sosai, don haka ya nuna nadamarsa a fili. Sannan baba Mustafa ya juyo wurin Dada.
"Dada ki gafarce ni a game da abin da zan faɗa amma tun farko ke ce kika ɓata Isuhu, saboda Isuhu yana ɗan autanki kika ɗauki son duniya kika ɗora masa. Hatta makaranta da Baba Sa'idu ya saka shi daina zuwa ya yi kuma kika goya masa baya, duk cikinmu shi kaɗai ne bai samu karatun arabi da boko mai zurfi ba. Ga shi nan sana'o'in ma wacce ce ba a nuna masa ba amma kullin a tsalle-tsalle yake ba shi da aiki sai kame-kame, tun wuri ka yi wa kanka faɗa domin kullin girma kake ƙara yi." Dada ta sharce ƙwallar da ke fuskarta ta ce.
"Yanzu dama MuÉ—É—afa ka na da tarin nasihohin nan tutuni ba ka yi mini ba? Ni dai wannan maganar a rufe ta a nan kada Sa'idu ya ji don wallahi sai ya kusa cinye ni É—anya."
GabaÉ—aya suka amsa mata.
"Dama wannan abin kunyar ai ba za mu bari ya fita ba Dada, yanzu dai a tambayi Uwani tun da haƙƙinta ne ta yafe masa?"
Uwani da ke gefe ta saki murmushin ƙeta ta yi saurin cewa, "Ni dai Baba na riga da na yafe musu baba Isuhu ai tamkar mahaifina na ɗauke shi." Da sauri Jafar ya dube ta don haka kawai ya ji bai yarda da kalaman Uwani ba.
"Allah Ya yi miki albarka Uwani, dama ɗa ba sai wanda ka haifa ba kaico rayuwa Allah Ya gafarta wa Yaya Umaru." Baba Isuhu ya faɗa yana sharce ƙwallah.
Uwani ta saki murmushin ƙeta a ranta ta ce, "Za ka ga ɗa ba sai ka haifa ba." Baba Idris ya yi musu nasiha sannan ya ce shi da kansa a ranar zai kira su Aramma na gangare su yi saukar Alƙur'ani a gidan gabaɗaya.