Sashe 23
Uwani Yar Kashin Gwuiwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Eh ɗakina nake nema?" Kallon tsaf ya yi mata, nan take ya lura da Uwani farin shigar zuwa hotel ce. Ba ta yi aune ba ta ji ya janyo hannunta ciki ya datse ƙofar, ya fara shafa gemu ya ce. "Ranki shi daɗe ni fa dama tun ɗazu nake ɗago miki hannu ba ki fahimta ba ne." Uwani ta fisge hannunta da sauri ta ce.
"Malam ni ba 'yar iska ba ce ka buɗe mini ƙofa." Alhajin mai tumbin kuɗi ya ajiye towel ɗin a gefen gado, ya sake tunkarar Uwani ya furta. "Yarinya kada ki cuci kanki, yayyafin kuɗi zan yi miki ko awa guda ba za ki yi ba za ki kama gabanki." Ya ƙarasa maganar yana sake riƙo hannun Uwani.
Uwani ta fisge tana ja da baya, Alhaji mai tunbin kuɗi ya lashe baki yana faɗin. "Ni fa tun da na yi arba da ke yawuna ya tsinke, dama tunanina ɗaya na san yadda za a yi na yi arba da ke." Alhaji tumbin kuɗi na rufe baki Uwani ta sunkuyar da kai ƙasa tana ɗagowa sai ji ya yi ta fara ɓaɓɓaka dariya. Juya idanunta ta yi ta fara wani ƙobare hannuwa cikin wata irin murya ta fara magana.
"A yau za ka mutu tun da har ka taɓo mana goɗiya 'yar sarkin mayun aljanu." Uwani ta fara tunkarar Alhaji tumbin kuɗi tana wani murɗe kai gefe. A can gefen gado ta hango belt ɗinsa sai ta buga wani uban tsalle ta suri belt ɗin, daidai wurin ƙarfen ta shammaci Alhaji ta zuba masa a baya. A zabure Alhaji ya ƙandare yana faɗin. "Wash! Bayana."
Uwani ta dafa hannuwanta biyu a saman kanta, tana motsi da bakinta. Ganin haka ya sa Alhaji ya saki baki yana kallonta a tsorace.
"Uwar ƙwaƙwido ki ɗauke gashin kaina a yanzu, saboda mummunan hukunci za mu zartar a yanzu. Ki mayar mini da kaina babu gashi irin na wannan tsinannan da yake gabana." Uwani na gama faɗin haka ta fisge hular kanta, nan take Alhaji tumbin kuɗi ya zaro ido cikin tashin hankali ganin kan Uwani babu gashi. Uwani ta fara wani gurnani tana tunkararsa, ganin haka ya sa Alhaji ya taƙarƙare ya zuba uban ihu yana faɗin.
"Wayyo Allah maman Garzali ki taimaka mini za a hallaka ni."
Uwani ta maƙe wuya tana zaro harshe ta ce. "Za mu kwashe wannan tumbin naka mu zuba maka duwatsu a ciki, domin kana cin amanar Maman Garzali matarka. Zan kuma fafe ƙoƙon ƙeyarka na dura maka ruwan tekun maliya a ciki." Da sauri Alhaji tumbin kuɗi ya dafe ƙeyarsa ya zuba a guje, hawaye haɗe da majina suka wanke masa fuska.
"Matso ka hau saman silin ko ka hau kan fanka, idan ba haka ba zan sa a yi sama da kai ko a nutse ƙarƙashin ƙasa da kai." Jiki na karkarwa Alhaji ya hau saman gado ya fara tsalle zai hau saman silin, idan ya yi tsalle ɗaya sai ka ji ɗass! Uwani ta zuba masa duka da belt. A galabaice ya dubi Uwani ya ce, "Don Allah ku yi mini rai wallahi a yanzu jinina zai iya hawa, ko nawa kuke so zan ba ku amma ku ƙyale ni." Uwani ta yi wani farrr da idanu, sannan ta ce. "Mu ba matsiyata ba ne, ba ma buƙatar kuɗinka Dama mu yawo muke Otel-otel muna hukunta masu hali irin naku masu lalata 'ya'yan mutane."
"Wallahi har abada na daina ba zan sake ba don Allah ku yi mini rai."
Uwani ta wurƙila ƙafa tana kanne ido ɗaya ta ce, "Za mu ƙyale ka amma da sharaɗin sai ka cinye sabulun wankan da ke banɗakinka, ko kuma mu farke cikinka mu tura maka 'ya'yan aljanu bakwai..." Tun Uwani ba ta gama magana ba Alhaji ya faɗa banɗaki da gudu ya ɗauko ragowar sabulun wankansa ya tura baki, yana ci yana kuka haka ya cinye sabulun bakinsa sai kumfa yake.
Uwani ta suri hularta a fakaici ta riƙe sannan ta sake ɓaɓɓaka wata irin dariya ta ce. "A zo a buɗewa Goɗiyar mayun aljanu ƙofa." Ba musu Alhaji tumbin kuɗi ya buɗe mata ƙofar, jikinsa banda karkarwa da gumi babu abin da yake yi.
Sai da Uwani ta fita ta sauke ajiyar zuciya don ita kanta ilahirin jikinta karkarwa yake, duk abin da take yi ƙarfin hali ne don ta lura da ta nuna masa tsoronta a fili ba abin da zai hana bai ci galaba a kanta ba.
Daga É—aki mai kallon na Alhaji tumbin kuÉ—i ta ji wani mutum yana yi mata É—an kira, a shekaru shi ma bai fi sa'an Alhajin ba. Yi ta yi kamar ba ta gan shi ba gabanta sai faÉ—uwa yake. Ta bayanta ta ji ya fara biyo ta yana faÉ—in.
"Haba 'yan mata kada ki yi wasa da damarki, abin da abokina ya ba ki ni zan ninka miki shi." A tunanin mutumin tun da ya ga Uwani ta fito daga ɗakin abokinsa ita ma 'yar hannu ce. Ganin haka ya sa Uwani ta fara sauri mutumin na biye da ita har dai ta ga da gaske yake ta saka gudu, tana yunƙurin shan kwana sai ta ji ta yi karo mutum. Cikin tashin hankali ta furta.
"Don Allah ku taimaka mini wallahi É—an iska ne ya biyo ni." Mutumin da kawo kansa kenan ya furta.
"Haba 'yan mata ni fa ko awa guda ba za ki yi mini ba, don Allah ki bari..." Maganarsa ta maƙale sakamakon arba da ya yi da Uwani riƙe da Jafar.
"Kai yaro wannan fa ba kalar yara ba ce. Don 'yan shiloli kamar su sun wuce ajinku." Cikin ɓacin rai Jafar ya furta.
"Amma dai Allah wadaran hali irin na lalatattun tsofaffi kamar ku."
Jin muryar Jafar ya sa Uwani ta ɗago da sauri don ko kaɗan ba ta taɓa tsammanin shi ba ne, suna haɗa ido ta riƙe shi ƙam jikinta na rawa cikin kuka ta furta. "Ya Jafar." Sai kawai kuka ya sake cin ƙarfinta.
Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki turo ta Acc Aisha Adam 3090957579 First bank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624
Free pages É—inmu ya kusa Æ™arewaðŸ«
#Ummou Aslam Bint Adam🌚
*UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA*
©AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye.
SHAFI NA SHA UKU
Jin yadda jikin Uwani yake karkarwa ya sa Jafar ya kwantar da ita a jikinsa ya sa hannu ya fara bubbuga bayanta, nan take idanunsa suka yi jawur saboda ɓacin rai. Ya dubi mutumin murya a dashe ya furta.
"Ka san wa ka taɓa kuwa? Ka san wanne irin kuskure kake yunƙurin aikatawa. Wallahi sai na nuna maka bakin rijiya ba wurin wasan makaho ba ne." Jafar ya ƙarasa maganar yana yunƙurin cire Uwani daga jikinsa, cikin kuka Uwani ta furta. "Tsoro nake ji Ya Jafar don Allah kada ka sake tafiya."
Ajiyar zuciya Jafar ya sauke ya riƙe hannunta suka fara tafiya rai a ɓace, ganin haka ya sa Alhajin ya zuba a guje ya faɗa ɗakinsa ya datse ƙofa. Ɗakinsu suka wuce sai da Jafar ya sa key ya buɗe suka shiga, ya kai ta kan kujera ya zaunar da ita sannan ya ce. "Ki jira ji yanzu zan dawo." Fuska da hawaye Uwani ta furta.
"Ya Jafar kada ka tafi ya shigo mini."
Sunkuyawa ya yi daidai fuskarta ya É—an hura mata iska ya furta.
"Ba abin da zai faru da ke yanzu zan dawo kin ji." A hankali Uwani ta gyaÉ—a masa kai sannan ya fice.
Ɗakin Alhajin ya koma ya yi bugun duniya ya ƙi buɗewa, shi kuwa Alhaji tumbin kuɗi jin ana buga ƙofar ɗakin abokinsa da ƙarfi, ya sa ya ƙara wa tashi ƙofar key sannan ya wuce banɗaki a guje jiki na rawa ya ɓuya.
Ganin ba shi da niyyar buɗewa ya sa Jafar ya zaro waya ya danna lambar DPO ɗin unguwar Zoo road, da yake abokinsa ne. Nan take ya sanar da shi abin da ya faru tsakanin Uwani da Alhajin. Sannan Jafar ya sauka ƙasa ya sanar da ma'aikatan reception abin da yake faruwa da kuma ɗakin da Alhajin yake ciki. Wata mata da ke gefe nan take ta furta.
"Kai malam Allah Ya yi maka albarka. Wallahi ni ma jiya da dare na ɗan fita unguwa na dawo haka wani ya dinga mini ɗan kira, da na shiga ɗaki har buga mini ƙofa ya yi ƙila ma shi ne." Jafar ya furzar da iska mai zafi ya ce. "Daga yau ai ba zai ƙara ba."
"A toh ai wasu mutanen gani suke idan suka ga mutum ya kama hotel kowa ma É—an iska ne, Allah Ya kyauta."
Ba a ɗauki lokaci ba sai ga motar 'yan sanda ta ƙaraso, lokacin da suka je bakin ƙofar Alhaji sai da ƙyar ya buɗe musu ƙofa. Har ƙasa ya tsugunna yana ba wa Jafar haƙuri amma fir ya ƙi sauraronsa, yaran D.P.O bayan sun saka masa ankwa Jafar ya ce su wuce da shi zai zo daga baya.
A wurin da ya bar Uwani a nan ya koma ya same ta, fuskarta ta kumbura saboda kuka. Tana ganinsa ta yi zumbur! Ta miƙe tsaye. Bai kula ta ba ya koma can gefen gado ya zauna ya dafe kansa, wani irin ɗaci yake ji a maƙoshinsa ya ɗago murya can ƙasa ya ce.
"Ya aka yi mutumin nan ya biyo ki ke da na bar ki a É—aki?" Zuciyar Uwani É—aya ta fara masa jawabi.
"Ni fa kasan ƙafata ba ta saba zaman wuri ɗaya ba, gajiya na yi da zama shi ne na fita can ƙasa na sha iska. Da na dawo sai na rasa ɗakin nan, bisa tsautsayi na faɗa ɗakin wani ɗan iska..." Uwani ta kwashe komai ta gaya masa amma ba ta gaya masa irin azabar da ta yi wa Alhaji tumbin kuɗi ba, ta dai ce masa Allah ne ya ƙwato ta bayan ta fito wannan Alhajin ya biyo ta.
"Malam ni ba 'yar iska ba ce ka buɗe mini ƙofa." Alhajin mai tumbin kuɗi ya ajiye towel ɗin a gefen gado, ya sake tunkarar Uwani ya furta. "Yarinya kada ki cuci kanki, yayyafin kuɗi zan yi miki ko awa guda ba za ki yi ba za ki kama gabanki." Ya ƙarasa maganar yana sake riƙo hannun Uwani.
Uwani ta fisge tana ja da baya, Alhaji mai tunbin kuɗi ya lashe baki yana faɗin. "Ni fa tun da na yi arba da ke yawuna ya tsinke, dama tunanina ɗaya na san yadda za a yi na yi arba da ke." Alhaji tumbin kuɗi na rufe baki Uwani ta sunkuyar da kai ƙasa tana ɗagowa sai ji ya yi ta fara ɓaɓɓaka dariya. Juya idanunta ta yi ta fara wani ƙobare hannuwa cikin wata irin murya ta fara magana.
"A yau za ka mutu tun da har ka taɓo mana goɗiya 'yar sarkin mayun aljanu." Uwani ta fara tunkarar Alhaji tumbin kuɗi tana wani murɗe kai gefe. A can gefen gado ta hango belt ɗinsa sai ta buga wani uban tsalle ta suri belt ɗin, daidai wurin ƙarfen ta shammaci Alhaji ta zuba masa a baya. A zabure Alhaji ya ƙandare yana faɗin. "Wash! Bayana."
Uwani ta dafa hannuwanta biyu a saman kanta, tana motsi da bakinta. Ganin haka ya sa Alhaji ya saki baki yana kallonta a tsorace.
"Uwar ƙwaƙwido ki ɗauke gashin kaina a yanzu, saboda mummunan hukunci za mu zartar a yanzu. Ki mayar mini da kaina babu gashi irin na wannan tsinannan da yake gabana." Uwani na gama faɗin haka ta fisge hular kanta, nan take Alhaji tumbin kuɗi ya zaro ido cikin tashin hankali ganin kan Uwani babu gashi. Uwani ta fara wani gurnani tana tunkararsa, ganin haka ya sa Alhaji ya taƙarƙare ya zuba uban ihu yana faɗin.
"Wayyo Allah maman Garzali ki taimaka mini za a hallaka ni."
Uwani ta maƙe wuya tana zaro harshe ta ce. "Za mu kwashe wannan tumbin naka mu zuba maka duwatsu a ciki, domin kana cin amanar Maman Garzali matarka. Zan kuma fafe ƙoƙon ƙeyarka na dura maka ruwan tekun maliya a ciki." Da sauri Alhaji tumbin kuɗi ya dafe ƙeyarsa ya zuba a guje, hawaye haɗe da majina suka wanke masa fuska.
"Matso ka hau saman silin ko ka hau kan fanka, idan ba haka ba zan sa a yi sama da kai ko a nutse ƙarƙashin ƙasa da kai." Jiki na karkarwa Alhaji ya hau saman gado ya fara tsalle zai hau saman silin, idan ya yi tsalle ɗaya sai ka ji ɗass! Uwani ta zuba masa duka da belt. A galabaice ya dubi Uwani ya ce, "Don Allah ku yi mini rai wallahi a yanzu jinina zai iya hawa, ko nawa kuke so zan ba ku amma ku ƙyale ni." Uwani ta yi wani farrr da idanu, sannan ta ce. "Mu ba matsiyata ba ne, ba ma buƙatar kuɗinka Dama mu yawo muke Otel-otel muna hukunta masu hali irin naku masu lalata 'ya'yan mutane."
"Wallahi har abada na daina ba zan sake ba don Allah ku yi mini rai."
Uwani ta wurƙila ƙafa tana kanne ido ɗaya ta ce, "Za mu ƙyale ka amma da sharaɗin sai ka cinye sabulun wankan da ke banɗakinka, ko kuma mu farke cikinka mu tura maka 'ya'yan aljanu bakwai..." Tun Uwani ba ta gama magana ba Alhaji ya faɗa banɗaki da gudu ya ɗauko ragowar sabulun wankansa ya tura baki, yana ci yana kuka haka ya cinye sabulun bakinsa sai kumfa yake.
Uwani ta suri hularta a fakaici ta riƙe sannan ta sake ɓaɓɓaka wata irin dariya ta ce. "A zo a buɗewa Goɗiyar mayun aljanu ƙofa." Ba musu Alhaji tumbin kuɗi ya buɗe mata ƙofar, jikinsa banda karkarwa da gumi babu abin da yake yi.
Sai da Uwani ta fita ta sauke ajiyar zuciya don ita kanta ilahirin jikinta karkarwa yake, duk abin da take yi ƙarfin hali ne don ta lura da ta nuna masa tsoronta a fili ba abin da zai hana bai ci galaba a kanta ba.
Daga É—aki mai kallon na Alhaji tumbin kuÉ—i ta ji wani mutum yana yi mata É—an kira, a shekaru shi ma bai fi sa'an Alhajin ba. Yi ta yi kamar ba ta gan shi ba gabanta sai faÉ—uwa yake. Ta bayanta ta ji ya fara biyo ta yana faÉ—in.
"Haba 'yan mata kada ki yi wasa da damarki, abin da abokina ya ba ki ni zan ninka miki shi." A tunanin mutumin tun da ya ga Uwani ta fito daga ɗakin abokinsa ita ma 'yar hannu ce. Ganin haka ya sa Uwani ta fara sauri mutumin na biye da ita har dai ta ga da gaske yake ta saka gudu, tana yunƙurin shan kwana sai ta ji ta yi karo mutum. Cikin tashin hankali ta furta.
"Don Allah ku taimaka mini wallahi É—an iska ne ya biyo ni." Mutumin da kawo kansa kenan ya furta.
"Haba 'yan mata ni fa ko awa guda ba za ki yi mini ba, don Allah ki bari..." Maganarsa ta maƙale sakamakon arba da ya yi da Uwani riƙe da Jafar.
"Kai yaro wannan fa ba kalar yara ba ce. Don 'yan shiloli kamar su sun wuce ajinku." Cikin ɓacin rai Jafar ya furta.
"Amma dai Allah wadaran hali irin na lalatattun tsofaffi kamar ku."
Jin muryar Jafar ya sa Uwani ta ɗago da sauri don ko kaɗan ba ta taɓa tsammanin shi ba ne, suna haɗa ido ta riƙe shi ƙam jikinta na rawa cikin kuka ta furta. "Ya Jafar." Sai kawai kuka ya sake cin ƙarfinta.
Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki turo ta Acc Aisha Adam 3090957579 First bank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624
Free pages É—inmu ya kusa Æ™arewaðŸ«
#Ummou Aslam Bint Adam🌚
*UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA*
©AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye.
SHAFI NA SHA UKU
Jin yadda jikin Uwani yake karkarwa ya sa Jafar ya kwantar da ita a jikinsa ya sa hannu ya fara bubbuga bayanta, nan take idanunsa suka yi jawur saboda ɓacin rai. Ya dubi mutumin murya a dashe ya furta.
"Ka san wa ka taɓa kuwa? Ka san wanne irin kuskure kake yunƙurin aikatawa. Wallahi sai na nuna maka bakin rijiya ba wurin wasan makaho ba ne." Jafar ya ƙarasa maganar yana yunƙurin cire Uwani daga jikinsa, cikin kuka Uwani ta furta. "Tsoro nake ji Ya Jafar don Allah kada ka sake tafiya."
Ajiyar zuciya Jafar ya sauke ya riƙe hannunta suka fara tafiya rai a ɓace, ganin haka ya sa Alhajin ya zuba a guje ya faɗa ɗakinsa ya datse ƙofa. Ɗakinsu suka wuce sai da Jafar ya sa key ya buɗe suka shiga, ya kai ta kan kujera ya zaunar da ita sannan ya ce. "Ki jira ji yanzu zan dawo." Fuska da hawaye Uwani ta furta.
"Ya Jafar kada ka tafi ya shigo mini."
Sunkuyawa ya yi daidai fuskarta ya É—an hura mata iska ya furta.
"Ba abin da zai faru da ke yanzu zan dawo kin ji." A hankali Uwani ta gyaÉ—a masa kai sannan ya fice.
Ɗakin Alhajin ya koma ya yi bugun duniya ya ƙi buɗewa, shi kuwa Alhaji tumbin kuɗi jin ana buga ƙofar ɗakin abokinsa da ƙarfi, ya sa ya ƙara wa tashi ƙofar key sannan ya wuce banɗaki a guje jiki na rawa ya ɓuya.
Ganin ba shi da niyyar buɗewa ya sa Jafar ya zaro waya ya danna lambar DPO ɗin unguwar Zoo road, da yake abokinsa ne. Nan take ya sanar da shi abin da ya faru tsakanin Uwani da Alhajin. Sannan Jafar ya sauka ƙasa ya sanar da ma'aikatan reception abin da yake faruwa da kuma ɗakin da Alhajin yake ciki. Wata mata da ke gefe nan take ta furta.
"Kai malam Allah Ya yi maka albarka. Wallahi ni ma jiya da dare na ɗan fita unguwa na dawo haka wani ya dinga mini ɗan kira, da na shiga ɗaki har buga mini ƙofa ya yi ƙila ma shi ne." Jafar ya furzar da iska mai zafi ya ce. "Daga yau ai ba zai ƙara ba."
"A toh ai wasu mutanen gani suke idan suka ga mutum ya kama hotel kowa ma É—an iska ne, Allah Ya kyauta."
Ba a ɗauki lokaci ba sai ga motar 'yan sanda ta ƙaraso, lokacin da suka je bakin ƙofar Alhaji sai da ƙyar ya buɗe musu ƙofa. Har ƙasa ya tsugunna yana ba wa Jafar haƙuri amma fir ya ƙi sauraronsa, yaran D.P.O bayan sun saka masa ankwa Jafar ya ce su wuce da shi zai zo daga baya.
A wurin da ya bar Uwani a nan ya koma ya same ta, fuskarta ta kumbura saboda kuka. Tana ganinsa ta yi zumbur! Ta miƙe tsaye. Bai kula ta ba ya koma can gefen gado ya zauna ya dafe kansa, wani irin ɗaci yake ji a maƙoshinsa ya ɗago murya can ƙasa ya ce.
"Ya aka yi mutumin nan ya biyo ki ke da na bar ki a É—aki?" Zuciyar Uwani É—aya ta fara masa jawabi.
"Ni fa kasan ƙafata ba ta saba zaman wuri ɗaya ba, gajiya na yi da zama shi ne na fita can ƙasa na sha iska. Da na dawo sai na rasa ɗakin nan, bisa tsautsayi na faɗa ɗakin wani ɗan iska..." Uwani ta kwashe komai ta gaya masa amma ba ta gaya masa irin azabar da ta yi wa Alhaji tumbin kuɗi ba, ta dai ce masa Allah ne ya ƙwato ta bayan ta fito wannan Alhajin ya biyo ta.